Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bai wa Babban Bankin Najeriya (CBN) iznin kulle asusun ajiyar wasu jagororin zanga-zangar #EndSARS da ke bankuna daban-daban.
Babban Bankin Najeriya ne ya nemi Mai Shari’a Mohammed Ahmed ya ba shi iznin kulle asusun bankunan na su, tun a ranar 20 Ga Oktoba.
PREMIUM TIMES ta ga wasikar da kotu ta tura wa Access Bank, Fedility Bank, First Bank, Guaranty Trust Bank, UBA da kuma Zenith Bank, inda aka umarce su kada su sake su bar masu asusun ajiyar a bankunan na su har su 20 su taba ko sisi cikin kudaden ajiyar na su.
Umarnin ya nuna cewa gwamnati na so ta yi amfani da kudaden da ke cikin asusun su a matsayin shaida.
Dalili kenan aka ce kada a bari su 20 din su taba kudaden ajiyar ta su, har sai bayan kwanaki 180, yadda kafin lokacin an kammala duk wani binciken da ya kamata a yi a kan su.
Wasu ‘yan gaba-dai-gaba-dai din #EndSARS da abin ya shafa sun hada da Bolatito Racheal Oduala, Chima David Ibebunjoh, Mary Doose Kpengwa, Saadat Temitope Bibi, Bassey Obi, Nicholas Ikhalea Osazele, Ebere Idibie, Akintomide Lanre Yusuf, Uhio Ezenwanyi Promise da Mosopefoluws Odesepe.
Sauran sun hada da Adegoke Pamilerin Yusuf, Umoh Grace Ekanem, Babatunde Vicror Segun, Mulu Louis Teghenan, Mary Oshifonawora, Winifred Akpevweoghene Jacob, Victor Solomon, Idunu Williams da Gatefield Nigeria Limited.
Duk da gwamnati ta amince za ta cika dukkan sharuddan da masu zanga-zangar su ka nema, sai kuma ga shi yanzu ta koma kokarin bin wasu da su ka hada zanga-zangar da kokarin yi masu bi-ta-da-kulli.
A farkon makon nan ne aka hana wata lauya wadda ta na cikin #EndSARS fita Turai, kuma aka kwace fasfo din ta.
Discussion about this post