Duk da dimbin arzikin man fetur, sannan da yawan al’umma da kuma harkokin kasuwancin da ke samar wa gwamnati kudaden shiga na ribar fetur da haraji, har yau kasar ba ta fita daga cikin jerin matalautan kasashen da yunwa, fatara da talauci su ka yi kaka-gida a gidajen sama da mutum milyan 100 a kasar ba.
Wasu kididdigar da cibiyoyi da kungiyoyi na Turai da na cikin gida su ka yi, sun nuna cewa akwai tsakanin mutum milyan 45 zuwa milyan 70, wadanda ba su da cin yau ko na gobe, har tilas a kullum sai sun fita sun nema.
Allah kadai ya san yawan mutanen da ba su iya samun kwatankwacin dalar Amurka 1 tal a rana, a Najeriya.
NAJERIYA: Yadda Kashe-kashen Kabilanci Da Na Addini, Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Su Ka Bindige Zaman Lafiya
Yayin da shekaru barkatai ana fama da kashe-kashen kabilanci da rikice-rikicen addini, bullowar Boko Haram ya maida sauran kashe-kashen kamar wasan kwaikwayo.
Cikin shekaru 10 Allah kadai ya sa yawan dubban mutanen da yakin Boko Haram ya ci rayukan su. An kashe sojoji masu tarin yawa. An fasa garuruwa, an tarwatsa kauyuka. Sama da mutum milyan daya sun fada zaman gudun hijira. Sannan dubban kananan yara sun zama marayu.
Rikice-rikicen ‘yan bindiga, mahara da masu gsrkuwa da mutane sun kara dagula al’amurra. Matsalolin sun yi dagulewar da su na neman su fi karfin gwamnati.
Tunanin cewa Gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari za ta magance matsalolin da ta yi alkawari, an koma ana ganin cewa abin ya zama mafarki ko ma tatsuniya. Domin lamura sai kara rincabewa su ke yi.
Da yawa na ganin cewa jam’iyyar APC ta yaudari al’ummar Najeriya a zaben 2015, lokacin da ta buga tambarin kawo canji. Mafi yawa sun gaskata ta. Bayan an zabi jam’iyyar ta kafa gwamnati, ana ganin wadda aka rika yaba wa sallah, sai ta shi ta shiga limanci ashe ko alwala ba ta iya ba.
Yayin da Najeriya ta cika shekaru 60 da samun ‘yanci, hankulan jama’a sun fi damuwa ne wajen neman mafitar masifu, bala’o’i, matsaloli da dimbin kalubalen da su ka dabaibaye kasar.
Ko za a iya warware su nan kusa, ko kuma sai nan da wasu shekaru 60, wannan kuma shi ne abin da kowa ke kwana ya na tashi da shi a zukata.
Discussion about this post