Hukumar NCDC ta sanar da karin mutum 151 da suka kamu da cutar Korona a Najeriya ranar Juma’a.
Alkaluman da hukumar NCDC ta fitar ranar Juma’a sun nuna cewa jihar Legas ta samu karin mutum -71, Ogun-26, Kaduna-17, Osun-10, Oyo-8, FCT-6, Rivers-6, Plateau-5, Akwa Ibom-1, da Ekiti-1
Yanzu mutum 59,992 suka kamu da cutar a Najeriya, mutum 51,614 sun warke, 1,113 sun rasu. Sannan kuma zuwa yanzu mutum 7,265 ke dauke da cutar a Najeriya.
Har yanzu dai jihar Legas ne ke da mafi yawan wadanda suka kamu da mutum 19,886, FCT –5,790, Oyo – 3,293, Edo –2,635, Delta –1,803, Rivers 2,659, Kano –1,740, Ogun – 1,927, Kaduna –2,484, Katsina -894, Ondo –1,638, Borno –745, Gombe – 883, Bauchi – 707, Ebonyi –1,042, Filato -3,504, Enugu – 1,289, Abia – 898, Imo – 579 , Jigawa – 325, Kwara – 1,050, Bayelsa – 401, Nasarawa – 469, Osun –874, Sokoto – 162, Niger – 261, Akwa Ibom – 295, Benue – 482, Adamawa – 248, Anambra – 250, Kebbi – 93, Zamfara – 79, Yobe – 76, Ekiti – 323, Taraba- 106, Kogi – 5, da Cross Rivers – 87.