Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa ya gana da sufeto Janar din Najeriya a fadar gwamnati a yau juma’a kuma ya umarce shi da ya gaggauta magance korafin da ‘yan Najeriya ke yi da kira da a rushe rundunar tsaro na SARS.
” Na sake ganawa da Sufeto Adamu cikin daren nan, kuma na umarce shi ya gaggauta duba matsalolin da ake kuka akai da yadda jami’an SARS din ke gudanar ayyukan su. Ina sane da irin sauye sauyen da ake yi a rundunar Yansanda, amma bai dace ace kuma maimakon agyara sai arika kukan batawa ake yi ba.
” Na umarce shi da kakkausar murya cewa lallai ya bi diddigin korafe-korafen da ‘yan Najeriyua keyi akan ayyukan SARS din domin magance su sannan wadanda suka aikata ba daidai ba ya tabbata an hukunta su cikin gaggawa.
” Ina rokon ‘Yan Najeriya su cigaba da hakuri su duk da ko suna da daman nuna rashin amincewarsu ga yadda jami’an ke muzguna wa mutane, cewa lallai za a gyara.
An kafa SARS domin dakile manya ko muggan laifuka da su ka hada da fashi da makami da garkuwa da mutane da sauran mugayen mutanen da ke hana al’umma zaman lafiya.
Sannu a hankali sai wasun su aka rika amfani da su wajen gallazawa, azabtarwa ko kuma ‘koya wa wani ko wasu hankali’ ta hanyar da shari’ar tsarin dokar kasa bai tanadar ba.
Maimakon al’ummar da ake so a kare lafiya, rayuka da dukiyoyin su su rika murnar kafa SARS, sai yawancin mutane su ka koma yin da-na-sanin kafa SARS.
Jami’an SARS da dama su na kallon kan su tamkar sun fi dokar ita kan ta kan ta karfi. Duk wani korafi, kuka, karajin da ake yi na a rushe rundunar SARS, ba abin mamaki ba ne, domin yawancin masu arba da su, da wuya su wanye lafiya.
SARS ba su jin ko dar-dar wajen darzaza harbi dararam, ko da kuwa a kan harkar tankiya, gardama ko sabani ne.
A kullum a jaridu a na samun rahotannin wadanda SARS su ka kashe, ko su ka jikkata, ko su ka lahanta.
Cikin watan Satumba ‘yan Najeriya sun sake kokartawa wajen tashi haikan su na kiraye-kirayen a rushe SARS. Abin ya yi karfi har ta kai cikin Oktoba din nan an ta zanga-zanga a jihohi daban-daban na kasar nan
Ba a bar manya wajen korafi da irin abin da su ke kira “ta’asar da SARS ke yi” ba. Ranar Laraba tsohon Mataimakin Shugaban Kasa ya yi Allah wadai da yadda wasu jami’an tsaro na SARS ke gallaza wa talakawa da ma masu karfin baki daya.
SARS, rundunar da aka kafa don dakile fashi da makami da manyan laifuka, sun koma hatta matasa maza masu yin askin ‘yarbatsula’, wanda ake barin gashi a cukuikuye ko kitso, kamawa su ke yi.
Haka nan SARS kan damke matashin da su ka gani da rankwaleliyar waya. Kafin ta tabbatar masu cewa ba ta sata ba ce, tuni jikin ka ya yi tsami, ya kumbura, ka koma ta neman ran ka.
Azabtarwar da su ke wa jama’a ta kara harzuka ‘yan Najeriya har aka shiga zanga-zangar neman a ruguje rundunar.
Hatta ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje, sun shiga sahun masu neman a rushe SARS.
Ya rage ga a duba a ga shin amfannin su ko rashin amfanin su, wane ya fi rinjaye? Amma dai aikace-aikacen SARS abin dubawa ne. Saboda ko makaho ya yi arba da su, zai iya ce maka harkar ta su akwai aika-aika.
Wanda ya shiga hannun SARS da ganganci ko da tsautsayi ko azal, shi ne zai tabbatar da cewa kirarin da ake wa dan sanda wai abokin kowa, to tatsuniya ke kawai!