Gwamnatin Tarayya ba za ta zuba ido masu tayar da tarzoma su hargitsa Najeriya, ta hanyar daukar doka a hannun su ba.
Wannan kalami ya fito ne daga bakin Ministan Yada Labarai Lai Mohammed, lokacin da aka yi wata doguwar tattaunawa da shi, ranar Asabar da dare, a Gidan Talbijin na NTA.
Ya yi kakkausan gargadin, ganin yadda zanga-zangar lumanar da ake yi domin rashin amincewa da Jami’an SARS, ta barke zuwa fito-na-firo da arangama a wasu wurare.
Furucin Lai ya zo ne kwana biyu bayan da Rundunar Sojojin Najeriya ta sanar cewa ba za ta zuba ido wasu tsiraru su dauki doka a hannun su ba.
Sojojin Najeriya sun ce ba za su bari wasu su gurgunta dimokradiyyar kasar nan ba. Kuma sun kara jaddada goyon bayan su da biyayya ga Shugaba Buhari.
Ya ce harin da aka kai wa Gwamna Oyetola na Osun ya nuna cewa ‘yan-ta-more sun kwace ragamar jagorancin zanga-zangar lumanar da ke gunada sama da mako daya.
Ya ce zai iya yiwuwa wadanda su ka tsara zanga-zangar nan da kyakkyawar manufa su ka shirya ta. “Amma dai tabbas abubuwan da ke faruwa sun nuna cewa lallai marasa kishi da ‘yan daba sun kwace ragamar zanga-zangar.
“Yanzu fa ba masu zanga-zangar #EndSARS gwamnati ke fuskanta ba. Kawai wasu dandazon ‘yan a-fasa kowa ya rasa sun karbe ragamar zanga-zangar.
“Don haka tilas gwamnati ta tashi tsaye domin kada abin ya kai ga jefa kasar nan cikin mummunan hargitsi.
“Wajibin Gwamnatin Tarayya ne ta tashi tsaye domin ta kare rayuka, dukiyoyi da lafiyar ‘yan Najeriya.
Ya yi nuni da yadda aka fara samun rahotanni da su ka tabbatar da asarar rayuka a wurin zanga-zanga. Sai tare hanyoyi da ake yi masu tafiya wuraren aiki ba su samun damar zuwa aiki.
Har ila yau, Minista Lai ya ce gwamnati na ganin zanga-zangar wata kullalliya da manufa ce boyayya ta neman dagula gwamnatin Buhari da kuma dagula Najeriya baki daya.
Ya ce tunda gwamnatin Buhari ta amince ta biya dukkan bukatun masu zanga-zangar, bai ga dalilin ci gaba da zanga-zangar ba.
Lai ya roki ‘yan Najeriya su kalli zanga-zangar da idon basira, za su game da akwai wata boyayyar manufar dagula wannan gwamnati da Najeriya baki daya.
Discussion about this post