Gwamnati jihar Kebbi ta bayyana cewa mutum 328 sun kamu da cutar amai da gudawa da ake kira ‘Gastroenteritis’ a jihar.
Hakan ya faru a dalilin ambaliyar ruwan saman da aka yi a jihar inda ambaliyar ruwan ya gurbata ruwan shan da mutanen ke amfani da shi a jihar.
Jami’in ma’aikatar kiwon lafiya ta jihar Muhammad-Abdullahi Bubuce ya Sanar da haka ranar Asabar yana mai cewa wannan cuta ta bullo a kanana hukumomin hudu a jihar.
Babuce ya ce tuni dai ma’aikatar ta dauki matakan dakile yaduwar cutar.
” Zuwa yanzu mutum 328 ne suka kamu da cutar sai dai kananan hukumomin Kalgo, Sakaba, Maiyama da Suru sun fi fama da barkewar cutar.
” Ma’aikatar lafiya ta jihar ta wadatar da isassun magungunar wannan cuta a asibitoci domin kula da wadanda suka kamu da ita.
Babuce ya yi kira ga mutanen da su tsaftace jiki da muhallinsu domin guje was kamuwa da cutar.
” Sannan a yi kokari a gina bandakuna a gidaje saboda yin bahaya a waje na daga cikin matsalolin dake sa a kamu da cutara.
Wata majiya ta bayyana cewa cutar ta yi ajalin wasu mutane a jihar sai dai Babuce bai tabbatar da adadin yawan mutanen da suka mutu ba.
Sannan wasu da suka warke sun kara kamuwa da cutar saboda rashin samun tsaftattacen ruwa.
Discussion about this post