• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

BINCIKEN MUSAMMAN: Yadda PREMIUM TIMES ta karade Kudancin Kaduna, ta gano kashe-kashen ramuwar-gayya ke hana yankin zaman lafiya

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
September 24, 2020
in Babban Labari, Rahotanni
0
BINCIKEN MUSAMMAN: Yadda PREMIUM TIMES ta karade Kudancin Kaduna, ta gano kashe-kashen ramuwar-gayya ke hana yankin zaman lafiya

‘Katilan-makatulan’: Ranar 18 Ga Agusta,2020, a kauyen Unguwan Garkon, mahara sun ritsa Hanatu Kefas da ‘yar ta mai shekara uku. Aka ce ta balle ganin goyo ta ajiye yarinyar a gefe. A tunanin ta fyade za a yi mata. Amma sai maharan wadanda aka hakkake Fulani ne, su ka rufe ta cikin garken aladu, aka yi ta yi tsirara ta rika birgima cikin dagwalon kazantar dagwallatsin kazantar kashin adalun nan.

Hanatu Kefas ta shaida wa PREMIUM TIMES cewa haka ta rika birgima ta na damalmala wa jikin ta kashin alade. Ta na cikin haka ta rika jin ana dankara wa mijin ta harbi da bindiga.

“Ina ji ina ganin sa ya na kakarin mutuwa, amma ba ni da ikon matsawa kusa da shi.”

Kisan da aka yi wa mijin ta Maliki Kefas, ya gigita ta, har sai da aka kwantar da ita asibitin Zonkwa, cikin Karamar Hukumar Zangon Kataf a Jihar Kaduna.

“Ramuwar Gayya Fulani Su Ka Yi A Kauyen Mu” – Hanatu Kefas

Bayan kisan da aka yi wa mijin Hanatu, an kashe wasu mutane uku. Maharan, wadanda Fulani ne, “sun zo ramuwar gayya ne a Unguwan Garkon, saboda a baya an kashe wani dan uwan su Bafulatani. Amma dai ni ban san wadanda su ka yi kisan ba. Saboda na je Kaduna, na dawo na taras an yi kisan.” Inji Hanatu, a hirar da PREMIUM TIMES.

A wannan harin ramuwar-gayya da Fulani su ka kai, ba su taba mata ba. Maza kadai su ka rika farauta, kuma sun kashe mutum biyu bayan mijin Hanatu.

Wannan hari alama ta irin salo da musabbabi da kuma dalilan da ke sa kashe-kashen zubar da jinainai a Kudancin Kaduna ya ki ci, ya ki cinyewa.

“Tasirin Kabilanci Da Asalanci A Kashe-kashen Kudancin Kaduna”:

Kudancin Kaduna mai ƙabilu daban-daban wadanda mafi yawan su Kiristoci ne, akwai kabilu irin su Kataf, Kaje, Adara, Takad, Fantswam, Ikulu, Chawai, Ham, wadanda su ne mafi yawan al’ummar yankin.

Sannan kuma akwai Hausawa da Fulani waɗanda su kuma Musulmi ne, amma su sauran ƙabilun yankin ba su yarda cewa Hausawa da Filani ‘yan asalin yankin ba ne.

Akwai tsirarun ƙabilu a yankin waɗanda ba Hausawa ba ne, ba kuma Fulani ba ne, amma kuma Musulmai ne. Su ne irin su tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Usman Mu’azu, musulmi ne dan kabilar Ham. Sai kuma irin su Mataimakiyar Gwamna Nasir El-Rufai, Hadiza Balarabe, ƴar ƙabilar Numana ce, kuma Musulma.

Su dai Hausawan yankin sun yi ikirarin cewa tun wajen shekarar 1650 su ke a yankin, su ne ma su ka kafa garin Zangon Kataf a shekarar.

Akwai Fulanin da ke shiga yankin su na kiwon shanu da damina, saboda yalwar ciyawa da yankin ke da shi. Amma dai sauran haifaffin Kudancin Kaduna wadanda Hausawa da Fulani ne, sun ki amincewa a ce musu su ba ‘yan asalin yankin ba ne.

Wani Kiriasta kuma shugaban yankin sa mai suna Gambo Waziri, cewa ya yi, “duk rigimar nan ta su wa ne ne ‘yan asali su wa ke bare ce. Mu ne ‘yan asali. Saboda ko da shekara 300 na yi a Enugu, ba za a kira ni dan asalin yankin kabilar Enugu ba.”

Kashe-kashen Kudancin Kaduna: Rikicin Gonaki, Addinanci, Kabilanci

“Kasar mu, ko kuma na ce maka gonakin mu daga kakannin- kakannin mu duk mu kagaje su.” Inji Saidu Umaru, wani dan kabilar Fantswam kuma jagora, Dagacin Zikfak ta Masarautar Kafanchan, cikin Karamar Hukumar Jema’a.

Wannan ra’ayi na sa ya yi daidai da ra’ayin duk wani kabila kirista dan yankin Kudancin Kaduna, ko ma a wace Karamar Hukuma ya ke a yankin.

Katutun Kiyayya, Gaba, Rashin Amintar Juna:

Wakilin mu ya fahimci a bangarorin biyu akwai tsananin gaba, kiyayya da rashin amintaka a duk inda ya shiga, tsawon kwanaki da ya shafe ya na karakaina a kananan hukumomin jihar.

Duk bangarorin da akan kai wa hari, akan lalata musu abin da suka fi takama da shi na dukiya, baya ga kisan rayuka. Duk bangaren da aka kai wa hari, sai sun rama komai daren dadewa.

Amma wakilin mu ya lura a yankin akwai hare-hare da ba su da alaka da rikice-rikicen ƙabilanci, wato irin na masu garkuwa da mutane da ke ritsawa da mai tsautsayi.

Manyan Kiristoci da wakilin mu ya yi hira da su, su na ganin kamar wasu tsare-tsaren da Gwamnatin Kaduna ta fito da su, duk na kokarin danne yankin ne. Amma akwai masu ganin cewa akwai bukatar a yi zaman kaunar juna tsakanin bangarorin biyu a yankin.

Shi ma babban Limamin Babban Masallacin Kafanchan, Muhammad Kassim, cewa ya yi sai bangarorin Kiristoci da Musulmi sun fahimci juna sun zauna lafiya sannan yankin zai samu kwanciyar hankali.

Duk Maganar Ɗaya Dai Ce

Ko a Iburu ko a Kajuru, ko a Kasuwan Magani ko a Kafanchan ko a Zangon Kataf ko ma ina a yankin Kudancin Kaduna har ka haɗa da kashe-kashen yankin ƙabilar Adara, duk dai magana ce ta rashin hakuri da juna, gaba, kiyayya, ƙabilanci, addinanci da kuma ramuwar-gayya.

Haka abjn ya ke a kashe-kashen da aka yi a Gidan Dutse, Kujeni da Bakira, duk na ramuwar-gayya ce.

PREMIUM TIMES ta gano wasu munanan hare-hare da aka har 11 a Gonan Rogo, Makyali, Ungwan Rana, Idazu, Ungwan Araha, Ungwan Dantata, Agwala Dutse, Tudu Doka Avong da Unguwan Magayaki da aka kashe akalla mutum 70.

PREMIUM TIMES ta mallaki sunayen wadanda aka kashen da kuma munanan raunukan da aka ji musu kafin a kashe su.

Hare-haren na ramuwar gayya kowane bangare kan yi asarar rayuka da dukiyoyi har ma da kone gidaje ko rugage.

An ce akwai akalla masu gudun hijira Katafawa 3,455 a wata makarantar Cocin ECWA da ke Zonkwa, Karamar Hukumar Zangon Kataf. Amma dai wakilin mu ya ce ya samu masu gudun hijira ba su fi 100 ba.

Wani jami’i ya ce akwai sansanin gudun hijira na Fulani a Kamoru, karkashin Zangon Kataf, inda Fulanin da aka tarwatsa wa rugage a Lisudu da kauyen Boto su ke can zaune.

Sai dai PREMIUM TIMES ta gano a sansanin Kamoru, an tsugunar da Fulani ne kamar 200, kuma ba su wuce kwana uku a wurin ba.

Wannan kashe-kashen da a yanzu haka Gwamnatin Jihar Kaduna a karkashin Gwamna Nasir El-Rufai na so ya kawo karshen sa, ya zama tarihi. Sai dai kuma Musulman yankin na ganin duk wani abu da za a yi to dole sai an koma wa Rahoton Kwamitin Bincike na Rikicin 1992, wanda aka kashe dubban Musulmai. Su kuma masu magana da yawun jama’ar yankin na cewa bimbinin wancan rahoto na baya ba zai haifar da da mai ido ba. Domin su su na ganin hari ne aka nemi a shafe su a bayan kasa, amma kuma su ka nuna jarumta su ka kare kan su.

Da alama babu ranar kare wannan rikice-rikice, domin PREMIUM TIMES na da munanan hotunan barnar da aka yi wa Fulani cikin watan Yuni, ranar 11 da 12 Ga wata, inda aka banka wa gidaje 36 wuta a kauyukan Gidan Zaki, Zarkwai, Takamaimen, Kigudu, Makwakwu, Bakin Kogi, Shilliam, Gidan Gata, Gidan Avong da Gora.

Ko ya kokarin da Gwamna El-Rufai ke yi na wanzar da zaman lafiya a Kaduna zai karke? Ko za a bari ya yi karko kuwa? Bari mu sa-ido mu gani.

Tags: AbujaHausaKadunaKudanciLabaraiNesNewsPREMIUM TIMESTsaro
Previous Post

JIGAWA: Jami’an tsaro sun damke dan shekara 30 da ya yi wa ƴar shekara 5 fyade

Next Post

SABON SARKIN ZAZZAU: A daina yada jita-jita da labaran karya, masu zaben sarki na nan na aikin dake gaban su – Gwamnatin Kaduna

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
SABON SARKIN ZAZZAU: A daina yada jita-jita da labaran karya, masu zaben sarki na nan na aikin dake gaban su – Gwamnatin Kaduna

SABON SARKIN ZAZZAU: A daina yada jita-jita da labaran karya, masu zaben sarki na nan na aikin dake gaban su - Gwamnatin Kaduna

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • TATTALIN ARZIKI: Ɗanyen man Najeriya ya fara kwantai a duniya, bayan Chana, Turai da Indiya sun koma sayen na Rasha mai rahusa sosai
  • HAJJI 2023: Hukumar Alhazai ta gindiya sabbin sharuɗɗan adadin kwanakin ziyara Madina
  • HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125
  • KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu
  • DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.