An yanke wa mutum Tara hukuncin kisa a jihar Kano bayan an kamsu da laifin aikata laifuka da ya kaiga hukuncin su kisa ne daga watan janairu zuwa Agustan 2020.
Kamar yadda BBC Hausa ta ruwaito bakwai daga cikin masu laifin an same su da laifin kisan kai, sai kuma mutum daya da laifin fyade sai kuma wanda aka yanke wa hukuncin yin kisa saboda yin kalaman batanci ga Manzon Allah SAW.
Ga jerin Sunayen su da laifukan da suka aikata
1 – Ali Abdullahi – Kotu ta yanke masa hukuncin Kisa bayan an kama shi da laifin aikata kisan kai ta hanyar rataya.
2 – Yakubu Dalha – Kotu ta yanke masa hukuncin Kisa bayan an kama shi da laifin aikata kisan kai ta hanyar rataya.
3 – Abdullahi Isyaku – Kotu ta yanke masa hukuncin Kisa bayan an kama shi da laifin aikata kisan kai ta hanyar rataya.
4 – Mujahid Sa’id – Kotu ta yanke masa hukuncin Kisa bayan an kama shi da laifin aikata kisan kai ta hanyar rataya.
5 – Naziru Ya’u – Kotu ta yanke masa hukuncin Kisa bayan an kama shi da laifin aikata kisan kai ta hanyar rataya.
6 – Shehu Ado Shehu – Kotu ta yanke masa hukuncin Kisa bayan an kama shi da laifin aikata kisan kai ta hanyar rataya.
7 – Isah Auta – Kotu ta yanke masa hukuncin Kisa bayan an kama shi da laifin aikata kisan kai ta hanyar rataya.
8 – Yahaya Aminu – Kotu ta yanke masa hukuncin Kisa bayan an kama shi da laifin yin kalaman batanci ga Manzo Muhammadu SAW.
9 – Mati Abdu – Kotu ta yanke masa hukuncin Kisa bayan ta hanyar jifa bayan an kama shi da laifin fyade.
Discussion about this post