Hukumar NCDC ta sanar da karin mutum 423 da suka kamu da cutar Korona a Najeriya ranar Talata.
Alkaluman da hukumar NCDC ta fitar ranar Talata sun nuna cewa Jihar Legas ta samu karin mutum – 117, FCT 40, Ondo 35, Rivers 28, Osun 24, Benue 21, Abia 19, Ogun 19, Ebonyi 18, Delta 17, Kwara 17, Kaduna 15, Anambra 14, Ekiti 11, Kano 9, Imo 6, Gombe 4, Oyo 3, Taraba 3, Bauchi 1, Edo 1 da Nasarawa 1.
Yanzu mutum 47290 suka kamu da cutar a Najeriya, mutum 33609 sun warke, 956 sun rasu. Sannan kuma zuwa yanzu mutum 12,725 ke dauke da cutar a Najeriya.
Har yanzu dai jihar Legas ne ke da mafi yawan wadanda suka kamu da mutum 16,074 FCT – 4,525, Oyo – 2,890, Edo – 2,399, Delta –1,613, Rivers 1,972, Kano –1,643, Ogun – 1,497, Kaduna – 1,628, Katsina –746, Ondo –1,324 , Borno –690, Gombe – 635, Bauchi – 578, Ebonyi – 888, Filato -1,584, Enugu – 914, Abia – 663, Imo – 485, Jigawa – 322, Kwara – 882, Bayelsa – 346, Nasarawa – 371, Osun – 652, Sokoto – 154, Niger – 226, Akwa Ibom – 235, Benue – 430, Adamawa – 185, Anambra – 156, Kebbi – 90, Zamfara – 77, Yobe – 67, Ekiti – 193, Taraba- 75, Kogi – 5, da Cross Rivers – 73.
Kasar Rasha hada da rigakafin Korona na farko a Duniya
A ranar Talata ne Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ya bayyana cewa masana magunguna a kasar sun kammala hada rigakafin Korona da kowa zai yi amfani da shi.
Masana kimiyar dake hukumar gudanar da bincike ‘Gamaleya Institute’ dake Moscow ne suka hada wannan magani na rigakafi bayan akalla watanni watanni biyu suka yi suna gwajin inganci da sahihancin sa.
Putin ya tabbatar da inganci da sahihancin maganin yana mai cewa daya daga cikin ‘ya’yansa da ta kamu da cutar ta samu lafiya bayan ta yi amfani da rigakafin.
Ya ce yana sa ran nan ba da dadewa ba za a fara sarrafa maganin da yawa domin mutanen kasar.
Yanzu kasar Rasha ita ce kasa ta farko da ta fara hada maganin rigakafin cutar Korona da hakan zai taimaka wajen rage yawan mace-macen da ake samu a kasar sanadiyyar wannan cuta.
Discussion about this post