Kotu a jihar Kano ta aika da wata mata mai Suna Saratu Ya’u asibitin mahaukata domin a tabbatar bata da tabuwar hankali.
Kotun na tuhumar Saratu dake zama a kauyen Sabon Birni karamar hukumar Gwarzo bisa laifin kisan kai.
Lauyan da ya shigar da karar Lamido Soron-Dinki ya ce Saratu ta aikata kisa kai ranar 12 ga Yunin 2018 a gidanta dake Sabon Birni, Gwarzo.
Sorondinki ya ce a wannan rana da misalin karfe 8:25 Saratu ta yi wa dan da ta haifa mai shekaru biyar yankan rago.
Ya yi kira ga kotun da ta yi amfani da dokar jihar na shekara ta 2019 domin a aika da Saratu a asibitin mahaukata domin tabbatar da lafiyar kwakwalwar ta.
Saratu ta amsa laifin da ta aikata.
Alkalin kotun ya yanke hukuncin a kai Saratu asibitin mahaukata domin a duba ta sannan za a ci gaba da shari’a ranar 8 ga watan Oktoba.
Idan ba a manta ba a cikin wannan mako ne rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama matar da ta daure dan kishiyarta a wani daki har na tsawon shekara 15.
Kakakin rundunar Abdullahi Haruna ya sanar da haka yana mai cewa matar da mijinta wato mahaifin yaron sun daure yaron a cikin gidan su dake kwatas din Sheka a karamar hukumar Kumbotoso a cikin wani gurbataccen daki babu ruwa babu abinci.
Ya ce jami’an tsaro sun ceto Ibrahim Lawan mai shekaru 40 daga cikin wannan mummunar hali ranar 16 ga watan Agusta.
Discussion about this post