Hukumar Bunkasa Harkokin Noma ta Amurka, ta ce a cikin 2019 Najeriya ta shigo da masara daga waje, adadin da rabon da ta shigo da shi tun cikin 2009.
USDA ta ce Najeriya ta shigo da tan na masara har 400,000 a cikin 2019, daidai abin da ta shigo da shi a baya cikin shekarar 2009.
Rahoton ya ce tan 400,000 din su ne na biyu a yawan masarar da Najeriya ta shigo da ita, tun shekarar 2016 da ta shigo da tan 650,000 na masara.
Masara ta zama daya daga cikin manyan kayan abinci a Afrika, tun bayan shigo a ita a nahiyar a cikin shekarun 1500s.
Najeriya ce kasar da ta fi kowace kasa noman masara a Afrika. Daga ita sai Tanzania, kamar yadda Cibiyar Binciken Noma a Afrika ta tabbatar.
Sai dai kuma abin mamaki, duk da haka Najeriya kuma it’s ce ta fi kowace kasa a Afrika shigo da masara a fadin Afrika.
Hakan ya na faruwa ne saboda yadda bukatar abincin dabbobi ke karuwa a Najeriya.
A duk shekara na bukatar metrik tan milyan 15 na masara. Amma kuma ta na noma metrik tan milyan 10.5 kadai.
Shekaru da dama manoman masara a Najeriya na korafin cewa za su iya wadatar da kasar nan masarar da ake ci da kuma wadda ake ciyar da dabbobi baki daya.
Dalili kenan manoman masara ke korafin cewa Najeriya ta ki hana shigo da masara kamar yadda ta haramta shigo da shinkafa.
Edwin Uche, Shugaban Kungiyar Manoma da Machasa Shinkafa na Kasa, MAGPAN, ya shaida wa PREMIUM TIMES cewa “idan gwamnati ta tallafa mana ta ba mu goyon baya, za mu iya noma masarar da za a ci a kasar nan, har wadda za a yi amincin dabbobi da ita.”
Najeriya ce ta uku a jerin kasashen da suka sayo masara daga waje. Zimbabwe ce ta farko, wadda ta sayo tan milyan 1, sai Kenya ta 2 da ta sayo tan 900,000.
A nan Najeriya, Babban Bankin Najeriya, CBN ya bayyana cewa ya shirya tsaf domin tallafa wa manoman masara 200,000 a fadin kasar nan.
A cikin watan Yuni CBN ya bayyana haka, lokacin da aka kaddamar da shirin noman masara na daminar bana a Jihar Delta.