• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Majalisa ta nemi a dakatar da Shirin Daukar 774, 000

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
July 2, 2020
in Labarai
0
Ahmed Lawan Senate President

Ahmed Lawan Senate President

Majalisar Dattawa da ta Tarayya, sun nemi a dakatar da Shirin Gwamnatin Tarayya na daukar kananan ma’aikata 774, 000, har sai an yi mata bayani gamsasshe dangane da yadda ake bi ana daukar ma’aikatan.

Hakan ya biyo bayan tankiyar da ta faru ce tsakanin Karamin Ministan Kwadago, Fesrus Keyamo da kuma Kwamitin Lura da Ayyuka da Ma’aikata na Majalisar Dattawa a ranar Talata.

Cikin wata sanarwar hadin-kai da Majalisar Dattawa da ta Tarayya suka fitar a ranar Laraba, sun amince cewa a tsaida shirin, jar sai Babban Ministan Kwadago, Chris Ngige da dukkan masu ruwa da tsaki a batun shirin daukar leburorin sun bayyana a gaban kwamiti sun yi gamsasshen bayanin matakan da suke bi wajen daukar ma’aikatan.

Daukar ma’aikatan ta zo da rikici, saboda an raba wa manyan kasar nan adadin da kowane bangare zai kawo sunayen su.

Yayin da Majalisar Dattawa ke zargin Keyamo da cuwa-cuwar sunaye, shi kuma ya yi musu bambami ne saboda ya yi zargin cewa su na neman kwace shirin daga hannun su, duk kuwa da cewa an ba su guraben kawo sunayen leburori har kashi 10% na adadin da za a dauka aikin.

PREMIUM TIMES ta buga labarin bobbotan da Karamin Minista Keyamo ya yi a gaban Kwamitin Majalisa, wanda sanadiyyar hakan har Sanata Ifeanyi Uba ya maida masa raddin cewa Minista Keyamo dan jagaliya ne, shi ya sa ya yi bambami a Majalisa -Sanata Ubah

Sanata Ifeanyi Ubah daga Jihar Anambra, ya bayyana bobbotan da Karamin Ministan Kwadago, Festus Keyamo ya yi a Majalisar Dattawa da cewa dabi’a ce ta dan jagaliya da ‘yan tasha.

Ya ce ya na mamakin yadda Keyamo ya rika hauragiyar tunanin cewa Sanatoci na kokarin kwace daukar leburorin aiki daga hannun sa.

Ya yi wannan raddi ne a wata tattaunawa da manema labarai a Abuja, ranar Laraba, inda ya yi matashiya cewa aikin Sanatoci shi ne sa-ido kan ayyukan da Ministoci ke yi, kuma shi Keyamo din ya san haka.

PREMIUM TIMES ta buga lanarin yadda Keyamo ya rika hayagaga da bambami a zaman sa Kwamitin Ayyuka na Majalisar Dattawa a ranar Talata.

An shirya taron ne domin su san inda aka kwana game da batun daukar ma’aikatan leburodi 774,000 da gwamnatin tarayya ta ce za ta dauka aiki.

A cikin Kasafin 2020, Majalisar Dattawa ta amince da kashe naira bilyan 52 wajen biyan wadannan leburori da kuma ayyukan da za su rika yi a fadin kasar nan.

Za a dauki lebura 1,000 a kowace Karamar Hukuma a fadin kasar nan cikin Kananan Hukumomi 774.

Keyamo ya zargi Sanatoci da kokarin yin banakeren kwace yawan leburorin da za a dauka, duk kuwa da cewa an ba su alfarmar kawo leburori a dauka aikin har adadin kashi 15% daga cikin 774, 000 da za a dauka aikin.

Sanata Ubah ya ce Sanatoci ba su yi laifi ba don sun tambayi yadda aka raba daukar ma’aikatan.

A matsayi na na sanatan da ke wakiltar jama’a, hakki na ne na binciki yadda ya ke tafiyar da tsarin daukar leburin a kasar nan. Saboda abin ya shafi wadanda na ke wakilta. Sannan kuma wanda aka damka wa aikin daukar leburorin na cikakken Minista ba ne, na je-ka-na-yi-ka ne.

“Ni ban san abin da Minista ke nufi ba, da ya yi kane-kane wajen daukar leburorin da za a rika biya ladar naira 20,000 ko 30,000 a wata ba. In banda dan tasha da dan jagaliya, ya daga mun yi maka tambaya za ka kama cika ka na batsewa, ka na ihu da kwaratsatsa?

“Mu ne ya kamata a bai wa damar dauka ko kawo sunayen wadanda za a dauka.

“Amma damka aikin a hannun dan jagaliya da zai je ya yi harkallar raba guraben ayyukan, abu ne da ba za mu amince ba.”

Asalin Yadda Batun Daukar Leburori 774, 000 Ya Taso:

Matasa 774,000 da za a dauka aiki, za su yi kwalbati, shara da hanyoyin burji a biya su naira 20,000 a wata -Minista Keyamo

Karamin Ministan Kwadago Festus Keyamo, ya bayyana dalla-dallar irin ayyukan da matasa 774,000 da Shugaba Muhammadu Buhari ya sanar cewa tuni an fara shirin daukar su aiki a dukkan kananan hukumomin kasar nan.

Da ya ke ganawa da manema labarai kwanan baya, Keyamo cewa ya yi sai ranar 1 Ga Oktoba matasan za su fara aiki.

Sannan kuma ya ce a ranar, za a fara ne da gwaji a jihohi takwas tukunna.

Jihohin da Kiyamo ya ce za a fara aikin sun hada da Adamawa, Barno, Ekiti, Ebonyi, Edo, Jigawa, Kwara da kuma Katsina.

Minista Keyamo ya ce za a fara ne da matasa 40,000 a wadannan jihohi takwas, kafin daga nan kuma a ci gaba a sauran jihohin kasar nan.

Irin Ayyukan Da Za Su Rika Yi A Kan Naira 20,000 A Wata:

Keyamo ya ce ayyuakan na su akasari duk ci-da-karfin-ka ne da suka hada da:

1. Yin amfani da diga da cebur da minjagara su na ginin kwalbatoci, ginar ramu da kuma aikin fitikin sare ciyawar da ke gefen titi.

2. Sassabe, shara da kaftun hanyar ruwan da ke kwarara daga madatsar-ruwa zuwa cikin cikin gonakin noman rani.

3. Aikin ginin hanyoyin shararra da burji da gyaran hanyoyin.

4. Rainon sabbin shuke-shuken itatuwa da yi musu ban-ruwa a jihohin Jigawa, Barno da Katsina.

5. Kula da warware matsalar cinkoson ababen hawa a kan titina.

6. Shara da goge-goge a makarantu, asibitoci da wasu ofissoshin gwamnati.

Premium Times Hausa ta buga labarin albishir din da Buhari ya yi a Ranar Dimokradiyya cewa gwamnatin sa ta fara Shirin Samar Da Ayyukan Musamman ga
matasa 774,000, don yaye musu talaucin Coronavirus.

Shugaba Muhammadu Buhari ya ce Gwamnatin sa ta fara wani gagarimin shiri na gaggauwar daukar matasa 774,000 aiki na musamman, domin yaye musu kuncin rayuwar da jama’a suka shiga sanadiyyar barkewar cutar Coronavirus.

Da ya ke jawabi a ranar Juma’a yayin tunawa da Ranar Dimokradiyya, wadda ta koma 12 Ga Yuni, Buhari ya ce cutar Coronavirus ba karamar illa ta yi wa milyoyin jama’a ba.

“Da yawa sun rasa iyalai, ‘yan uwa da masoyan su. Wasu sun rasa aikin su baki daya. Milyoyi sun rasa dukiyoyin su. Tattalin arzikin wasu ya karye dalilin cutar Coronavirus.”

A kan haka ne Buhari ya ce gwannatin sa ta raba kayan tallafin rage radadin talauci da kuma raba bilyoyin kudade ga milyoyin marasa galihu a kasar nan.

Da ya juya a kan ayyukan musamman da ya ce gwamnatin sa za ta samar wa matasa kwanan nan, Buhari ya ce za a tsamo matasa 1,000 ne daga kowace karamar hukuma daga Kananan Hukumomi 774 da ake da su a fadin kasar nan.

Ya bada hakuri dangane da irin matsanancin halin kuncin da ‘yan Najeriya suka shiga, dalilin tsauraran matakan da gwamnatin tarayya ta dauka domin kokarin dakile cutar Coronavirus.

Ya ce cutar abin tsoro ce ganin yadda ta fara kamar da wasa a kasar China, amma ga shi cikin ‘yan watanni ta shafi mugum sama da milyan 7 a duniya a cikin kasashe 216.

Ya ce jo shakka babu Coronavirus babbar barazana ce ga rayuwar dan Adam gaba daya a duniya da kuma tattalin arzikin duniyar baki daya.

Idan ba a manta ba, Buhari ya rasa Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Abba Kyari sanadiyyar cutar Coronavirus da ya dauko a kasar Jamus.

Kyari dai an yi ittifakin cewa a gwamnatance, shi ne mutumin da ya fi kowa kusanci da Buhari, kafin Coronavirus ta yi sanadiyyar ajalin sa.

Tags: AbujaAPCBuharigwamnatiHausaKeyamoLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMESTarayya
Previous Post

Amurka ta koro ‘yan Najeriya sama da 3,000 da suka aikata muggan laifuka

Next Post

Korona ta yi ajalin Kwamishinan lafiyar jihar Ondo

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
KORONA: Najeriya ta samu karin mutum sama da 500 da suka kamu a ranar Asabar

Korona ta yi ajalin Kwamishinan lafiyar jihar Ondo

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Kano ta hana lika fastoci a ginegine a fadin jihar
  • Sojoji sun kashe ‘yan ta’adda 58, sun kama wasu 161 a cikin makonni biyu a yankin Arewacin Najeriya
  • Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa
  • SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Dalilin da ya sa INEC ta yi wa kotu jayayyar kwafe-kwafen bayanan da Atiku da Obi su ka gabatar – Lauyan INEC
  • HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.