• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Maganin Farin Jini Daga Bakin Manzon Allah (SAW), Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
July 5, 2020
in Ra'ayi
0
Imam Murtada Gusau

Imam Murtada Gusau

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jin Kai

Dukkanin kyakkyawan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Ubangijin talikai, tsira da amincin Allah su kara tabbata ga Annabin mu, Muhammad (SAW), da iyalansa da sahabbansa baki dayansu. Bayan haka:

Ya ku bayin Allah, wani Sarki ne wata rana ya fita kilisa da mutanensa da fadawansa, sai ya iske wani tsoho tukuf-tukuf yana shukar dabino. Sai Sarki yace a tsaya. Yasa aka kira tsoho, tsoho yazo yayi gaisuwa. Sarki yace tsoho:

“Wannan shuka taka ba ta makara ba kuwa? Yaushe har wannan dabino zai girma, har yayi ‘ya ‘ya kaci?”

Tsoho yace Allah ya taimaki Sarki:

“Ko ni ban ci ba ai na baya na za su ci. Mu dabinon da muke ci yanzu ba kakanninmu ba ne suka shuka suka bari, mu muke cin amfaninsa a yanzu? Mu ma ai ya zama dole mu shuka domin mu bar wa na baya, matukar muna son alkhairi ga kawunan mu.”

Sarki yaji dadin wannan magana ta tsoho yace:

“Gaskiyar ka tsoho.”

Sarki ya dubi shamaki yace ayi masa kyauta. Shamaki ya dauko dukiya ya bai wa tsoho. Tsoho ya fadi gaban Sarki yayi godiya yace:

“Ikon Allah, ranka ya dade, dabino shekara da shekaru ya kan yi kafin ya haihu amma ka ga ni nawa dabinon tun ban gama shuka shi ba yayi ‘ya ‘ya.”

Sarki yayi murmushi ya sake duban shamaki yace a kara masa. Tsoho ya karba ya sake godiya yace:

“Allah ya ja zamanin Sarki, duk girman dabino sau daya yake yin ‘ya ‘ya a shekara, amma nawa yanzun nan gashi har ya haihu sau biyu.”

Sarki yace a kara masa kyauta. Ana ba shi tun bai yi magana ba sai waziri ya dubi Sarki yace:

“Ranka ya dade, gara fa mu wuce mu bar wannan tsoho don sai ya kare duk abin da aka fito dashi da iya bakin sa.”

Sai tsoho ya dubi waziri yace:

“Ba iya baki ba ne, so nike da Sarki da mutanensa da sauran al’ummar duniya su fahimci cewa, ba’a makara da shuka alkhairi.”

Darasi a cikin wannan labari:

Akwai karantar wa akan cewa lallai abunda al’ummah ta ke son samu na ci gaban ta a can gaba, to tun a baya ne ta ke shuka shi. Sannan akwai yin kira game da alfanun da ke tattare da yin kyauta da shuka alkhairi, tare da kuma nuna munin rowa da marowata a cikin al’ummah.

Ya ku ‘yan uwa, mu yawaita kyautatawa da yin alkhairi, domin alkhairi yana kara dankon zumunci, yana kara soyayya, yana tara wa mutum dimbin masoya da magoya baya. Alkhairi yana sada zumunci. Alkhairi yana hana sharri, kuma yana tunkude sharrin makiya da mahassada da makircinsu. Alkhairi yana daukaka darajar mutum duniya da lahira. Alkhairi yana kara arzikin mutum. Alkhairi yana hana kiyayya. Alkhairi danko ne, baya faduwa kasa banza…etc, don haka mu yawaita alkhairi, mu guji rowa, domin rowa tana da hadari mai yawa a rayuwar dan Adam, kuma tana da mummunan tasiri ga mai yin ta!

Annabi (SAW) ya kasance yana yiwa hatta makiyinsa kyauta da alkhairi, har ya zamanto daga karshe, makiyin nan ya ji cewa baya da masoyin da ya kai Manzon Allah (SAW) a duniya, saboda kyautatawar da yake yi masa, da kuma yawaita alkhairin sa. Hatta makiya sun tabbatar da cewa, Annabi Muhammad (SAW) yana yin kyauta, irin kyautar mutumin da baya tsoron talauci. Kuma mu ga shi kullun muna ikirarin cewa mu mabiyansa ne kuma mu masoyansa ne. To anan ina biyayyar ‘yan uwa? Ina soyayyar ta ke? Ta yaya za’a yi marowaci ya zama masoyin Manzon Allah (SAW)? Ta yaya za’a yi kuma ya zama mabiyinsa? Kun ga wannan ba zai yiwu ba ko?

Sannan Manzon Allah (SAW) yace:

“Kuyi kyauta za’a so ku.”

Sannan ya sake fada a wani Hadisin cewa:

“Hannun da yake bayar wa shine a saman hannun da yake karba a koda yaushe.”

Ya ku ‘yan uwa, wadannan Hadisai sun karantar da mu cewa, lallai duk mai yin kyauta da yawaita alkhairi, wallahi za’a so shi, sannan kuma ba zai taba yin kasa ba, kullun zai kasance a sama ne da ikon Allah.

Ya ku jama’ah, ku sani, wallahi rowa ba ta da kyau, kuma tana jawo wa mutum mummunan bakin jini, da yawaitar makiya da mahassada. Sannan rowa tana hana kofofin alkhairi su bude wa mutum, ta mayar da shi baya, yaki ci gaba a rayuwar sa, kullun ya ta yin baya. Allah ya sawwake, amin.

Hadisi ya tabbata daga Abu Hurairah (Allah Ya kara masa yarda), yace:

“Wani mutum yazo wurin Manzon Allah (SAW) yace, “Ya Ma’aikin Allah, wace irin sadaka ce ta fi?” Sai Manzon Allah (SAW) yace, “Ita ce wadda ka bayar a lokacin da kake lafiyayye, kuma kana kankame da dukiya (wato kana tsumulmularta), kana tsoron talauci, kana sa ran zama attajiri! (ita ta fi). Yace kada ka yi jinkiri har sai ka kusa mutuwa ka rika cewa, “Wannan a kai wa wane da wane; waccan a kai wa wane da wane.” Alhali ta kai lokacin da ta zama dukiyar wane da wane!” [Buhari da Muslim ne suka ruwaito Hadisin]

Kuma sannan abu ne sananne cewa, babu yadda za’a yi wanda yake bayar wa ya rasa, da izinin Allah, domin Annabi Muhammad (SAW), mai gaskiya kuma abun gaskatawa. Wanda ba ya magana da son zuciyarsa, kuma duk abunda ya fada wahayi ne daga wurin Allah, yace:

“Ku tausayawa bayin Allah da suke a bayan kasa, ku kuma Allah da yake sama sai ya tausaya naku.”

Wannan ya nuna kenan matukar kana taimakawa bayin Allah, kana tausaya masu, kana yi masu kyauta da alkhairi, to da ikon Allah kai ma Allah ba zai manta da kai ba.

To ko bature ma me yace? Ba cewa yayi “GIVERS NEVER LACK” ba? Ka ga wannan magana haka take ko Dan uwa?

To saboda haka ni ban ga yadda za’a yi mai bayarwa ya rasa ba, sai fa idan wata jarabawa ce ta zo daga wurin Allah, wadda yayi nufin jaraba bawan sa da ita, to sai muce wannan kuma wani al’amari ne daban. Sannan haka kuma ban ga yadda za’a yi marowaci ya rabu da talauci da damuwa ba, domin da rowa da talauci Dan Jumah ne da Dan Jumai, babu yadda za’a yi ka iya raba su. Duk inda rowa tayi katutu, to zaka tarar talauci da rashin wadatar zuci sun yi kaka-gida, kuma sun samu gindin zama a wurin.

Daga cikin abubuwan da Allah da Manzon sa (SAW) suka ki, suka kyamata, kuma suka haramta, akwai rowa. Ayoyin Alkur’ani da Hadisai masu tarin yawa sun tabbatar da hakan, wanda yanayin lokaci ba zai bani damar kawo wa ba. Kai hatta Malaman Musulunci ma sun yi rubuce-rubuce akan yabon masu kyauta, masu alkhairi, da kuma suka akan masu rowa wato ذم البخل. Don haka yaku jama’ah, ya kamata mu fahimci cewa rowa bala’ice kuma masifa ce. Kuma duk wanda yake marowaci, zaka tarar jama’arsa ma duk sun watse masa, sun guje shi, domin ai kuda basa bin mai kayan gawayi. Mai bayarwa kuwa, kullun ba zaka raba gidansa da al’ummar Annabi Muhammad (SAW) ba. Allah yasa mu dace, amin.

Dan uwan ku, Imam Murtadha Muhammad Gusau, ya rubuto daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa a lambar waya kamar haka: 08038289761.

Tags: AbujaFarinHausaJiniKarantaLabaraiMaganiNajeriyananPREMIUM TIMES
Previous Post

KORONA: Abuja 73, Kaduna 20, Kano 2, yanzu mutum 28, 167 suka kamu a Najeriya

Next Post

SUNAYE: Dakarun Kwamandan PDP, Wike da Baradan APC da za su gwabza a Zaben Edo

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
ZABEN EDO: Tsakanin Ganduje da Wike, wanda ya raba fada bai yi kallo ba

SUNAYE: Dakarun Kwamandan PDP, Wike da Baradan APC da za su gwabza a Zaben Edo

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • RIGIMAR SHUGABANCIN MAJALISA: Zan yi aiki tare da duk waɗanda su ka zama shugabannin majalisa – Tinubu
  • DUNIYA JUYI-JUYI: Yadda SSS suka kama Emefiele, suka jefa shi magarƙama bayan Tinubu ya dakatar shi
  • Yadda sabon Gwamna ya ƙwato motoci 40 da Matawalle ya yi walle-walle da su
  • ƘARYAR CBN TA ƘARE: Tinubu ya dakatar da Emefiele, gogarman da ya yi wa Naira fentin zabibi, bayan dala ta kai Naira 750 a ƙarƙashin sa
  • ƘARFIN HALI: Na san Kwankwaso na Villa yau, amma da mun haɗu da na gaura masa mari – Ganduje

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.