Hukumar NCDC ta sanar da karin mutum 653 da suka kamu da cutar Coronavirus a Najeriya ranar Asabar.
Alkaluman da hukumar NCDC ta fitar ranar Asabar sun nuna cewa Jihar Legas ta samu karin mutum –115, Kwara-85, Enugu-80, FCT-78, Rivers-36, Ondo-35, Oyo-30, Katsina-28, Kaduna-19,Abia-19, Nasarawa-18, Filato-17, Imo-16, Ogun-9, Ebonyi-9, Benue-9, Kano-9, Delta-8 Bauchi-7, Ekiti-6, Gombe-4, Bayelsa-4, Adamawa-4, Osun-4, Cross River-1, Yobe-1, Borno-1 da Zamfara-1.
Yanzu mutum 36107 suka kamu da cutar a Najeriya, mutum 14938 sun warke, 778 sun rasu. Sannan kuma zuwa yanzu mutum 20,391 ke dauke da cutar a Najeriya.
Har yanzu dai jihar Legas ne ke da mafi yawan wadanda suka kamu da mutum 13,341 FCT – 2,957, Oyo – 2,106, Edo – 1,885, Delta – 1,423, Rivers – 1,516, Kano – 1,395, Ogun – 1,168, Kaduna – 1,118, Katsina –1,087, Ondo – 912 , Borno –598, Gombe – 544, Bauchi – 529, Ebonyi – 655, Filato – 620, Enugu – 675, Abia – 479, Imo – 452, Jigawa – 322, Kwara – 535, Bayelsa – 322, Nasarawa – 254, Osun – 332, Sokoto – 153, Niger – 145, Akwa Ibom – 162, Benue – 194, Adamawa – 115, Anambra – 101, Kebbi – 88, Zamfara – 77, Yobe – 64, Ekiti – 84, Taraba- 30, Kogi – 5, da Cross Rivers – 13.
Matakan da Zamfara ta dauka wajen dakile yaduwar Korona a jihar
Kakakin gwamnan jihar, Zailani Bappa ya bayyana matakan da gwamnatin jihar ta dauka da ya sa aka samu nasarar dakile yaduwar cutar a jihar.
1 – Gwamnati Zamfara ta bi dokar gwamnatin tarayya sauda kafa tun da farkon bullowar cutar a kasar nan.
Mun rufe makarantun mu tunda wuri, mun rufe kasuwanni da iyakokin jihar mu, sannan mun saka dokar kowa ya saka takunkumin fuska dole-dole. Mun yi haka ne tun kadin cutar ta dira jihar mu ma.
2 – Kafin cutar ta bulla a Zamfara gwamtai ta kafa kwamiti biyu, daya domin wayar da kan mutane game da cutar dayan kuma domin basu tallafi
3 – Mun wadata wuraren da aka kebe domin kula da wadanda suka kamu da cutar a jihar. Mun samar da kadajen marasa lafiya akalla 100, na’aurar shakar iska, na’urar yin gwajin jutar da takunkumin fuska.
4 – kun yi wa kasuwanni feshin magani, makarantu da cikin gari baki daya.
5 – Ko a loacin da ake ta kokarin maidsa Almajirai jihohin su na asali, na mu da aka dawo da su sai da muka yi musu gwaji kafin suka shigo cikin gari.