Hukumar NCDC ta sanar da karin mutum 576 da suka kamu da cutar Coronavirus a Najeriya ranar Talata.
Alkaluman da hukumar NCDC ta fitar ranar Talata sun nuna cewa Jihar Legas ta samu karin mutum –88, Kwara-87, FCT-82, Filato-62, Ondo-39, Enugu-28, Oyo-26, Taraba-24, Kaduna-20, Ebonyi-20, Edo-17, Cross River-16, Kano-14, Rivers-11, Ogun-10, Delta-9, Nasarawa-8, Osun-8, Katsina-3, Imo-2, Kebbi-1 da Borno-1.
Yanzu mutum 37,801 suka kamu da cutar a Najeriya, mutum 15,677 sun warke, 805 sun rasu. Sannan kuma zuwa yanzu mutum 21,319 ke dauke da cutar a Najeriya.
Har yanzu dai jihar Legas ne ke da mafi yawan wadanda suka kamu da mutum 13,626 FCT – 3,211, Oyo – 2,219, Edo – 2,017, Delta – 1,435, Rivers – 1,546, Kano –1,430, Ogun – 1,184, Kaduna – 1,211, Katsina –713, Ondo – 964 , Borno –603, Gombe – 558, Bauchi – 531, Ebonyi – 699, Filato – 762, Enugu – 705, Abia – 526, Imo – 454, Jigawa – 322, Kwara – 672, Bayelsa – 322, Nasarawa – 289, Osun – 359, Sokoto – 153, Niger – 166, Akwa Ibom – 175, Benue – 294, Adamawa – 115, Anambra – 132, Kebbi – 90, Zamfara – 77, Yobe – 64, Ekiti – 86, Taraba- 54, Kogi – 5, da Cross Rivers – 29
Matakan da Zamfara ta dauka wajen dakile yaduwar Korona a jihar.
Kakakin gwamnan jihar, Zailani Bappa ya bayyana matakan da gwamnatin jihar ta dauka da ya sa aka samu nasarar dakile yaduwar cutar a jihar.
1 – Gwamnati Zamfara ta bi dokar gwamnatin tarayya sauda kafa tun da farkon bullowar cutar a kasar nan.
Mun rufe makarantun mu tunda wuri, mun rufe kasuwanni da iyakokin jihar mu, sannan mun saka dokar kowa ya saka takunkumin fuska dole-dole. Mun yi haka ne tun kadin cutar ta dira jihar mu ma.
2 – Kafin cutar ta bulla a Zamfara gwamtai ta kafa kwamiti biyu, daya domin wayar da kan mutane game da cutar dayan kuma domin basu tallafi
3 – Mun wadata wuraren da aka kebe domin kula da wadanda suka kamu da cutar a jihar. Mun samar da kadajen marasa lafiya akalla 100, na’aurar shakar iska, na’urar yin gwajin jutar da takunkumin fuska.
4 – kun yi wa kasuwanni feshin magani, makarantu da cikin gari baki daya.
5 – Ko a loacin da ake ta kokarin maidsa Almajirai jihohin su na asali, na mu da aka dawo da su sai da muka yi musu gwaji kafin suka shigo cikin gari.
Discussion about this post