• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Kadan Daga Dabi’u Da Halayen Sarki Muhammadu Sanusi II, Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
July 1, 2020
in Ra'ayi
0
Sarki Sanusi

Sarki Sanusi

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jin Kai

Dukkanin yabo da godiya sun tabbata ga Allah ubangijin talikai, tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabin mu Muhammad (SAW), da iyalansa da sahabbansa baki dayansu.

Ya ku al’ummah, wallahi a duk lokacin da nike magana akan Sarki Muhammadu Sanusi II, to lallai ku sani ina magana ne akan manyan halayensa masu kyau da dabi’unsa wadanda duniyar tarihi ta shaida, tun zamanin baya da zamanin da muke ciki yanzu. Dabi’u ne da halaye nagari, wadanda da ace duniya za ta rikesu, tayi koyi da su, to lallai da duniya ta zauna lafiya, a samu alheri da ci gaba. Wadannan dabi’u da halaye nasa kuwa, shi kan sa ya same su ne sanadiyyar koyin sa da fiyayyen halitta, wato Manzon tsira, Annabi Muhammad (SAW). Daga cikin dabi’u da halayen Sarki Muhammadu Sanusi II, akwai cewa:

Sarki Muhammadu Sanusi II, mutum ne mai hankali, mai hakuri da yafiya, kuma yana mai neman sakamakon haka a wurin Allah Subhanahu wa Ta’ala. Shi mutum ne mai yin abu domin Allah (wato da ikhlasi), mai kyakkyawar mu’amala ne ga mutane da kuma iyalan gidan sa. Mutum ne mai son gyara a koda yaushe, mutum ne shi mai umurni da aikata kyakkyawan aiki da kuma hani akan aikata mummunan aiki. Sarki Sanusi mutum ne mai son tsarki, mai tsafta, sannan shi mutum ne mai yawan kiyaye harshensa daga surutu da maganganun banza marasa amfani, sai fa idan a wurin fadar gaskiya ne. Sarki Muhammadu Sanusi mutum ne mai yawan ibada, mutum ne mai tausayi da saukin kai, mutum ne da Allah yayi masa kyawon sura da kyawon halitta, mutum ne mai tsantseni a rayuwar duniya, mutum ne da baya hana abun da aka tambayeshi, sai fa idan baya da shi, mutum ne mai karfin imani da tawakkali, mutum ne mai tausayi da son yara, mutum ne mai yin rangwame ga mutane, sannan shi mutum ne mai tsoron Allah da kamewa.

Imam Murtada Gusau
Imam Murtada Gusau

Ya ku jama’ah, wallahi Sarki Muhammadu Sanusi II mutum ne mai ciyar da abinci ga mabukata, mutum ne mai son taimako, mutum ne mai fadin gaskiya komai dacinta, kuma ko meye zai same shi akan hakan. Shi mutum ne mai kokari wurin girmama iyakokin Allah, mutum ne mai sakin fuska ga mutane, mutum ne mai rikon amana da cika alkawari, mutum ne jarumi, mai jarumta da rashin tsoro ko kokwanto, mutum ne mai karamci da jurewa akan haka, kuma shi mutum ne mai kunya.

Ya ku bayin Allah, Sarki Muhammadu Sanusi II mutum ne mai kankan da kai, mai tawadu’u, kuma shi mutum ne mai nuna rahama, tausayi da jin kai ga talakawa, kuma mutum ne mai saukin kai. Sarki mutum ne mai yafiya da hakuri kuma adali, mutum ne mai tsananin tsoron Allah, kuma shi mutum ne mai wadatar zuci da hakuri da kadan.

Daga cikin dabi’un Sarki Muhammadu Sanusi II, ya kasance shi mai son yin alheri ne ga kowa, kai hatta makiyansa. Sannan sai kusancinsa da fadawansa da talakawansa da kuma cudanya da su, da sauraren koke-koken su. Sannan sai kokarinsa wurin zuwa gai da marasa lafiya, ya biya kudin maganinsu, kuma yayi masu alheri, musulmi ne su ko kuma wadanda ba musulmi ba. Sannan sai rashin girman kan sa, da yin godiya ga duk wanda ya aikata masa alheri, da kuma kokarin saka masa shi ma, da abunda zai iya. Shi mutum ne mai son dukkanin wani abu mai kyau da tsabta da kuma kamshi, wato turare. Shi mutum ne mai son shiga tsakani da kuma kokarin yin sulhu a cikin dukkanin ayyukan alheri. Shi Mutum ne mai kokari wurin yiwa kansa hidima.

Jama’ah, wadannan kadan ke nan daga cikin halaye da dabi’un Sarki Muhammadu Sanusi II, wadanda duk wanda yayi hulda da shi, ko yake hulda da shi, to zai shaida hakan. Kuma kamar yadda nayi bayani, wallahi wadannan dabi’u da halaye, Allah ne yayi shi haka, ba shine yayi wa kan sa su ba. Sannan kuma ya same su ne sakamakon kokarinsa wurin bin umurnin Allah, na yin koyi da fiyayyen halitta, Annabi Muhammad (SAW). Sakamakon haka, a lokacin da yake kan gadon sarautar Kano, Kanawa da arewa suka ji dadi, suka yi murna da farin ciki. Aka wayi gari yana son su, suna son sa, kuma suna jin maganarsa, domin sun san ba zai yaudare su ba, kuma ba zai yi masu karya ba, kuma ba zai taba yarda a hada kai da shi a cuce su ba!

Ya ku jama’ah, wallahi wadannan kadan ke nan daga cikin hujjojinmu da dalilanmu na nuna kaunar mu da soyayyarmu ga wannan bawan Allah, da kuma kokarin kare mutuncinsa da martabarsa daga makircin makaryata, masu son bata masa suna. Jama’ah, bamu kadai ba ma, ni nayi imani da Allah cewa, duk wani mahaluki a duniya, duk wani mai gaskiya, duk wani mai son ci gaban al’ummarsa, mai ilimi da hangen nesa, wallahi dole yaso Sarki Muhammadu Sanusi II, ba don komai ba, sai don wadannan halaye da dabi’u nasa kyawawa, da Allah Subhanahu wa Ta’ala ya azurta shi da su. Ina rokon Allah yasa mu dace, amin.

Amma yau an wayi gari, tun da aka dau alhakinsa, babu wanda duniya zata kalla a Kano, wanda za ayi domin sa kuma a bari domin sa.

Kamar yadda kuka sani ne, a koda yaushe al’ummah ta kan tafi ne bisa jagorancin mutum daya, wanda ya kasaita, kuma yake da jajircewa da kokari akan abinda ya shafi jama’arsa da talakawansa, kuma yake son ci gabansu, sanadiyyar haka sai a samu zaman lafiya, kwanciyar hankali, da ci gaba mai dorewa da izinin Allah.

Amma babban abin taikaici, tun da Khalifah Mai Martaba Sarki Malam Muhammadu Sanusi II ya bar kujerarsa birnin Kano yake nema ya zama baya a idon duniya, an rasa ina aka dosa a birnin, kowa yayi tsit, komai yayi shiru, talakawa sun rasa gata. Komai ya lalace, ba ga sarauta ba, ba ga gwamnati ba, komai ya daina dadi, kuma baka bukatar ace ma da Sarki a Kano ko babu, duk dan Kano wallahi, yasan halin da birnin yake ciki, sai fa idan za mu munafunci kawunan mu ne, mu boye gaskiya, wannan kuma wani abu ne daban!

Ya ku jama’ah, abin alfahari ne ga dukkan dan Kano, ace a majalisar dinkin duniya, Sarki Sanusi yana da kujera tasa ta kansa, wadda duk taro na duniya idan ya tashi, za’a gayyace shi, kuma a gayyaci shugaban kasa, wanan ya ishi duk dan Kano alfahari.

Sarki Muhammadu Sanusi II, a yau duniya kalar sa take nema, kuma take bukata, domin shi din, dole sai da ire-iren su, kuma wannan matsayin daga Allah ya same shi, ba wai yin kan sa bane, a’a.

A dalilin sa ya sake daukaka darajar Kano a idon duniya, amma yanzu Kano sai kokarin komawa baya take yi, saboda an kawo wani iri, wanda an rasa ma ina ya dosa, babu Sarauta, babu karatun, bare ace Kano za ta ci gaba. Allah ya sawwake, amin.

Wannan bawan Allah, Sarki Muhammadu Sanusi II, ya sanya Kano ta zama abin alfahari a idon duniya, kuma babu kamar sa har yanzu.

Muna rokon Allah ya saka masa da alkairi, kuma ya ci gaba da kare shi, ya kare masa mutuncinsa da martabarsa, daga sharrin miyagu, mahassada, magauta da makiya, amin.

Ya Sarki Sanusi, wallahi kai ne Sarki a wurin talakawa, ko yau ko gobe, ko jibi, ko anjima, ko yanzu Kanawa basu da kamar ka.

Ya Allah mun tuba, ka yafe laifukan da muka yi maka, ka dawo muna da Sarkin mu, mai son ci gaban jihar Kano da arewa da Najeriya, kuma mai kaunar talakawa, amin.

Ina rokon Allah ya kyauta, ya kawo muna mafita ta alkhairi, amin.

Dan uwan ku, Imam Murtadha Muhammad Gusau, ya rubuto daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa a lambar waya kamar haka: 08038289761.

Tags: AbujaGusauMuhammadu SanusiMurtadhaNajeriyaNewsPREMIUM TIMESWakafi
Previous Post

Kungiyar Jami’an Kula Da Lafiya ‘JOHESU’ za su tafi yajin aiki

Next Post

FALLASA: Minista Keyamo dan jagaliya ne, shi ya sa ya yi bambami a Majalisa – Sanata Ubah

Next Post
FALLASA: ‘Yan majalisar Kasa sun wawushe kashi 15% na ma’aikatan da gwamnatin tarayya za ta dauka 774,000

FALLASA: Minista Keyamo dan jagaliya ne, shi ya sa ya yi bambami a Majalisa - Sanata Ubah

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • AN YANKA TA TASHI: A biya ni naira miliyan 21 kuɗin fom ɗin takarar gwamna da na siya a PDP – Ɗan takarar gwamna
  • ZARGIN ƘARFA-ƘARFA A SIYASAR ENUGU: Sanata Ekweremadu ya saka takalmin ficewa daga PDP zuwa APC
  • TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’
  • KATSINA TA DAGULE: An bindige manoma 12 a gona, an sace ‘limaman’ Cocin Katolika biyu da yara biyu
  • Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.