Ministan Shari’a Abubakar Malami, ya bayyana cewa umarnin da ya bayar a yi gwanjon wasu tankokin jiragen ruwa da man da ke ciki ga kamfanin da ke gaban kotu ake tuhuma da harkalla da zamba, ba aibi ba ne, domin ya bada umarnin bai kauce wa doka ba.
Malami ya yi wannan raddi ne bayan an fallasa yadda yadda yadda bada umarni a sayar da wani dimbin man fetur da gas da ke da kare cikin wasu jiragen ruwan daukar mai har hudu.
Ya bada umarnin kamfanin Omoh-J Nigera Limited ya kwashe ya kwashe mai a matsayin cinikin kayan gwanjo, duk kuwa da cewa shi ma Omoh-Jay din kotu na tuhumar sa da satar danyen mai har metrik tan 120,000 dankare a cikin tankokin jiragen ruwa.
Cikin wata sanarwa da Kakakin Yada Labarai na Minista Malami, mai suna Umar Gwandu ya fitar, Malami ya ce, “umarnin a sayar da tankokin da man ya fito ne bayan kotu ta yanke huncin karshe cewa gwamnati ta kwace jiragen lodin danyen man danyen man da ke ciki, tare kuma da umarnin da Ofishin Shugaban Kasa ya bayar, a ranar 25 Ga Oktoba, 2018.
Da ya ke kare kan sa daga abin da al’ummar kasar nan ke kallon bahallatsa ce ya tabka, Malami ya ce ya yarda tabbas kotu na kan tuhumar Jerome Itepu mai tankokin jiragen daukar mai na kamfanin sa Omoh-Jay Nigeria Limited da laifin satar danyen mai, to ya kamata a lura ba a kai ga samun sa da laifi ba.
Saboda haka a cewar Malami, za a iya mu’amalar cinikayya da kamfanin, tunda ba a kai ga samun sa da laifi ba.
“Da an samu Minista Malami da karbar toshiyar baki ko kashe-mu-raba, ko hannu a cikin jarin kamfani, to shi ne zai zama abin damuwa.
Daga nan sai Malami ya bada bayanin tun asali yadda EFCC ta kama jiragen dakon man da kuma tsawon lokacin da kamfanin ya dauka su na kotu, shi da EFCC.
Haka Malami ya rika yanko bayanai daga wasu takardun bayanan da hukumomin da abin ya shafa suka rika fitarwa dangane da rikicin tankokin jiragen ruwan da kuma man, wanda aka kama tun a lokacin mulki Goodluck Jonathan.