• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba  sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad

    An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad

    An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed

    An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba  sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad

    An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad

    An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed

    An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Abun Al’ajabi, Dawowar Aminu Babba Dan Agundi Cikin Masarautar Kano! Daga Imam Murtadha Gusau

Mohammed LerebyMohammed Lere
July 9, 2020
in Ra'ayi
0
Abun Al’ajabi, Dawowar Aminu Babba Dan Agundi Cikin Masarautar Kano! Daga Imam Murtadha Gusau

Amin Ado Bayero

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jin Kai

Dukkan kyakkyawan yabo da godiya sun tabbata ga Allah ubangijin talikai, tsira da amincin Allah su kara tabbata ga Annabinmu Muhammad, da iyalansa da sahabbansa baki dayansu. Bayan haka:

Ya ku jama’ah, wato sau da yawa ban fiye yin magana akan wasu abubuwan ba, domin ba komai ne zaka mayar wa da mutane amsa akai ba, saboda mun san cewa wallahi wasu mutanen basu ma isa a mayar masu da martani ba. Kawai wani lokacin mukan yi magana ne domin yin shirun zai sa mutanen da basu san me yake faruwa ba, ba zasu fahimci gaskiyar al’amari ba, sai ayi masu karya, su dauka cewa karyar ita ce gaskiya, alhali kuwa sam ba haka ba ne. Kuma mu mun daukar wa kan mu alkawarin bayyanawa duniya gaskiya tsakanin mu da Allah, ba tare da jin tsoron zargin duk wani mai zargi ba.

Jama’ah, idan mafadin magana wawa ne, ai majiyinta ba zai zama wawa ba, ko akasin haka. Musamman a daidai wannnan lokacin, amma dai yana da kyau mutane su rinka fuskantar abubuwa da idon basirah da kuma dogon nazari akan irin abubuwan da suke faruwa a tsakaninsu.

Murtadha Gusau
Murtadha Gusau

A lokacin da Allah cikin ikon sa da kaddarawarsa ya bawa Mai Martaba Sarkin Kano Malam Muhammadu Sanusi ll Sarautar Kano, yazo ya tarar da rigingimu kala-kala, iri-iri, masu tarin yawa, wadanda cikin ikon Allah, saboda iliminsa da hikimarsa, da basirarsa da hangen nesansa, Allah ya taimake shi yayi iya kokarinsa don ganin ya warware iya abinda Allah ya bashi Ikon warwarewa. Kama daga bangaren Sarauta da ma abinda ya shafi sha’anin yau da kullum.

Sarautar Sarkin Dawaki Mai Tuta, wadda Alhaji Aminu Babba Dan Agundi yake kan ta, tana cikin irin rigingimun da Mai Martaba Sarki Muhammadu Sanusi ll ya tarar, wadda kuma alhamdulillahi, Mai Martaba Sarki yayi rawar gani don bin duk wasu hanyoyin da suka dace, na ganin bai kwayewa wanda ya gada, wato babansa, tsohon Sarki baya ba, akan irin hukuncin da ya yanke na yin awon gaba da rawanin Aminu Babba Dan Agundi din. Sarki Sanusi ya tabbatar da hukuncin da Sarki Ado ya yanke domin ya kare masa mutuncinsa da Martabarsa. Duk duniya ta san anyi haka.

Aminu Babba Dan Agundi yayi kokarin shiga jikin Mai Martaba Sarki Muhammadu Sanusi ll, don ganin burinsa ya cika na dawo masa da Sarautarsa, wadda marigayi Sarkin Kano Ado Bayero ya warwareta, amma a lokacin, Sarki Sanusi ya tabbatar masa da hakan ba zai taba yiwuwa ba, domin hukunci ne da Magabata suka yanke, wanda shi kuma ba zai warware shi ba. Bayan da yaga wannnan damar ba ta samu ba, sai yabi hanyoyin yin Shari’ah da Masarauta, wato zuwa kotu. Da ma tun tsohon Sarkin yana raye yake ta gurfanar dashi gaban Shari’ah, duk duniya ta shaida an yi haka.

Aminu Babba Dan Agundi yaci nasara a kotu, ya kayar da Masarauta a kotun farko ta Kano (wato High court) da kotu ta biyu, wato kotun daukaka kara kenan (Appeal court), wannan ya faru ne lokacin marigayi Sarki Ado, Allah ya jikansa da rahama, amin.

Da Allah ya kawo Mai Martaba Sarki Muhammadu Sanusi II sai yasa a daukaka kara zuwa kotun koli, ya canza lauyoyi kwararru wadanda za su wakilci masarauta, shine kotun koli tayi watsi da hukunce-hukuncen da aka yi a kotunan kasa, kotun koli ta ce abinda Sarki Ado yayi daidai ne, na sauke rawanin Aminu Babba Dan Agundi.

In dai takaita maku bayani, haka suka yi ta bugawa da Mai Martaba Sarki Sanusi II, kuma shi yasan cewa fadan yafi karfin sa. Shari’ah ta kai su har kotun koli, kuma kotun kolin kamar yadda na fada, ita ma dai kwanan nan ta tabbatar da wancan kuduri na marigayi Sarki Ado, wanda Sarki Sanusi II yace shi ba zai sauka akai ba, domin yin hakan tamkar yaye wa Sarki Ado zane ne a kasuwa! Duk duniya ta shaida hukuncin da kotun kolin ta yanke, domin na san har wasu daga cikin ku ma sun ga takardun hukuncin da aka yanke.

To a kwana a tashi, dama Malam bahaushe yace da dan gari akan ci gari. Kuma da ma ance naka-ke-bada-kai, kwatsam wata matsala ta zo ta sabani tsakanin Gwamnatin jihar Kano da Mai Martaba Malam Muhammadu Sanusi ll a wancan lokaci kenan, kuma kamar yadda duniya ta shaida, wannan rikici ya faru ne saboda gaskiyar da Mai Martaba yake akai, kuma yake fada masu, su kuma mutane ne wadanda basu son gaskiya, kuma suna adawa da ita.

Abubuwa sun faru marasa dadi, wanda shi Gwamnan jiha, a wancan lokacin ya samu hadin kan wasu daga cikin ‘yan uwan Mai Martaba Sarki Sanusi, kuma zuri’ar gidan Dabo, wadanda suke hassadar Sarki saboda baiwa da Allah yayi masa, wannan ya jawo Ganduje yayi abinda yayi, kamar yadda kuka sani.

Kowa ya sani, Aminu Babba Dan Agundi ya taka muhimmiyar rawa wurin fada da Sarki Sanusi, ya basu goyon baya dari-bisa-dari, da shi aka yi duk abunda suka yi, ba don komai ba, sai don ganin cewa burinsa ya cika, na dawowarsa kan Sarautarsa.

Yabi duk hanyoyin da yake ganin zai bi don yayi nasara, ya hada kai da Gwamnati, ya hada kai da duk wani wanda yasan cewa yana hassadar Sarki Sanusi. Domin wallahi da kan su, suna fadar irin gudunmawa da hadin kai da ya basu wurin cimma burin su, har dai abinda Allah ya kaddara zai faru yazo ya faru.

Kuma majiya mai tushe ta tabbatar da cewa da ma bai yi masu aikin ba sai da sharadin cewa za’a dawo da shi cikin Masarautar Kano. To bayan kura ta lafa ne, sai ya dawo da maganarsa, tare da neman a cika masa alkawarinsa. To da ma fa ‘ya’yan Baba ne, Gwamna ya basu umurnin a cika masa alkawarinsa, saboda gudummawar da ya basu wurin yaki da Sarki Sanusi II, duk da kotu ta yanke hukunci akai. Dama kuma kun san halin wasu ‘yan siyasar, basu mai da doka komai ba, duniya tana kallon su suka yi watsi da hukuncin kotu.

Kuma su basu isa suyi musun maganar Gwamna ba, na umurnin da ya basu na dawowa da Aminu Babba Dan Agundi kan Sarautarsa, tun da dama su Sarakunansa ne ba na jama’ah ba. Nan take suka amince da dawo masa da Sarautar. Wanda kuma yin hakan, sabawa ne tare da warware alkawari, da hukuncin da Mahaifinsu yayi. Kun ga anan, sai duniya ta kara shaida cewa, lallai albasa ba tayi halin ruwa ba ke nan!

Kuma ‘yan uwana masu daraja, abu ne da kowa ya sani, cewa Aminu Babba Dan Agundi tun da marigayi Sarki Ado ya cire shi daga sarauta, shekara sama da goma, har Allah yayi wa Sarki Ado rasuwa, yawo yake yi yana zagin sa, yana cin mutuncinsa. Alhali Sarki Ado shine ya nada mahaifinsa, wato Babba Dan Agundi Sarkin Dawaki Mai Tuta, ba tare da ya gaje ta ba. Kuma tun mahaifinsa Babba Dan Agundi yana da rai, marigayi Sarki Ado ya nada dan nasa Aminu, kuma ya ba shi ‘yarsa ya aura, daga baya yayi mata wulakanci, ya sake ta. Sannan kuma ya nuna wa Sarki Ado rashin da’a da ladabi, aka cire shi daga sarautar. Ko kotun koli ma ta tabbatar da cewa rashin ladabin da yayi shi yasa aka cire shi, kuma Sarki Ado yayi daidai.

Jama’ah ku sani, Gwamna Ganduje ma ya dade yana tursasawa Sarki Muhammadu Sanusi II lamba, akan wai ya mayar da Aminu Babba Dan Agundi kan kujerarsa ta sarauta, amma Sarki Sanusi yace ba zai yi ba saboda irin abinda yayi wa Sarki Ado na cin mutunci da rashin da’a, amma wai yau, ga wanda yake da’awar cewa wai shi dan Sarki Ado ne, ya kasa kare masa mutuncinsa da martabarsa, ya mayar da Aminu Babba Dan Agundi sarautar da yasan mahaifinsa Sarki Ado ya cire shi. Inna lillahi wa inna ilaihi raaji’uun!

Duk da cewa lauyoyin Sarki Muhammadu Sanusi II sun samu nasara a kotun koli, yau Aminu Ado yayi biris da wannan hukuncin, ya shafawa mahaifinsa Sarki Ado Bayero toka a fuska, ya karrama makiyinsa, ya mutunta wanda bai san girmansa ba.

Allahu Akbar! Wallahi dadin abun duk zamu mutu, mu koma ga Allah yayi hukunci!

Allah ya sawwake, Allah yasa mu gama lafiya da magabatanmu, kuma duk abun da zai sa muci mutuncin magabatanmu, ya Allah kar ka sa mu aikata shi, amin.

Ina rokon Allah ya kyauta, ya kawo muna mafita ta alkhairi, amin.

Dan uwan ku, Imam Murtadha Muhammad Gusau, ya rubuto daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa a lambar waya kamar haka: 08038289761.

Tags: AbujaAminuDan AgundiHausaKaniKanoLabaraiMasarautarNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

ZAMAN KOTU: EFCC ta kasa nuna cin hancin $25,000 da take zargin Shehu Sani ya karba daga ASD

Next Post

FYADE: Ko ka gina kangon ginin ka, ko gwamnati ta daure ka – Gwamnatin Kano

Next Post
FYADE: Ko ka gina kangon ginin ka, ko gwamnati ta daure ka – Gwamnatin Kano

FYADE: Ko ka gina kangon ginin ka, ko gwamnati ta daure ka - Gwamnatin Kano

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • ZARGIN HARƘALLAR NAIRA BILIYAN 98: Bincike ba kaina farau ba, kuma kotun koli wanke ni ta yi – Amaechi
  • An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • El-Rufai ya lashe Zaben fidda gwani na kujerar majalisar tarayya, zai gwabza da Samaila Suleiman
  • An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed
  • Yadda ‘Ƴan bindiga suka sace fastocin cocin katolika biyu a Katsina

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.