Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya (Food and Agricultural Organisation),wato FAO, ta kara jaddada cewa matsawar dai cutar Coronavirus ba ta tsagaita a Afrika ta Yamma ba, to akwai yiwuwar mutum milyan 50 su fuskanci mummunar masifar yunwa a yankin.
Haka wani babban jami’in Hukumar FAO ya jaddada.
Coumba Sow, babban kodinaton Dakile Yunwa na FAO a Afrika ta Yamma, ya bayyana a cikin wata tattaunawa da aka yi da shi cewa idan ba tashi tsaye aka yi da Gaggawa ba, to milyoyin jama’a a Afrika ta Yamma ya su shiga matsin yunwa a wannan halin da tuni wasu har sun kai ga shiga wannan mawuyacin hali saboda cutar Coronavirus da rikice-rikicen da ke kara ruruwa a yankin.
“Ganin yadda yawancin kasashen Afrika ke fama da cututtuka da kuma rikice-rikice, to mafita a wajen mu ita ce mu ci gaba da tallafawa wajen inganta hanyoyi da dabarun bunkasa noma a wannan damina mai sauka a yanzu. Wannan zai rage radadin mawuyacin halin da milyoyin mutane ke ciki sanadiyyar matsalar abinci yayin Coronavirus.”
Wannan yanki ciki har da Najeriya a yanzu ya na cikin mawuyacin hali ganin yadda cutar Coronavirus ta na ta kara darkakar say ta na fantsama.
Sama da mutum 170, suka kamu da cutar a Afrika ta Yamma, yankin da ke koma baya wajen karancin abinci a duniya. Ga kuma faman da yankin ke yi da rikice-rikicen Boko Haram, ISWAP da ‘yan bindiga.
So ta ce yanzu haka a kasashenBurkina Faso, Mali da Nijar, akwai kimanin mutum milyan 4 da ba su day cin yau balle na gobe. FAO na tsoron Nan da kwanaki kadan adadin su zai iya karuwa su kai mutum milyan 5.5 nan zuwa watan Agusta.
Rahoton 2020 ya nuna a Najeriya akwai mutum milyan 5.1 masu bukatar agajin abinci a Najeriya. Milyan 1.4 a Barno, milyan 1 a Yobe da kuma 500,000 a Adamawa.
“Abin ya zame wa wasu milyoyin mutane goma-ashirin. Wasu baya ga yunwar, an raba su da garuruwan su. Ko kone gidajen su. An karkashe wadanda suka dogara da su wajen ciyar da su.” Haka Sow ta bayyana.
Makonni biyu da suka gabata, FAO ta yi gargadin cewa Farin-dango sun darkako Afrika ta Yamma baki daya.
Hukumar Abinci ta Majisar Dinkin Duniya (FAO), ta bayyana cewa farin-dango na daf da mamaye ilahirin gonakin Yankin Afrika ta Yamma, nan da cikin watan Yuni mai kamawa.
FAO ta ce yanzu haka milyoyin farin-dango za su gaba da haihuwa da kyankyashe milyoyin ‘ya’ya a kasashen Ethiopia, Kenya, Sudan, Somalia da yankin Afrika ta Yamma.
“Milyoyin farin-dango na ci gaba da kyankyashe ‘ya’ya su na zugar nausawa Sudan. Abin tsoron shi ne idan suka nausa suka mamaye yankin Sahel na Afrika ta Yamma.”
Darakta Janar na FAO, QU Dongyu ya kara da cewa duk wani kokarin daukar matakan da za a iya yi, zai dauki lokaci kafin aiwatarwa.
Ya ce wannan fargabar ta biyo bayan la’akari da irin barnar da farin-dangon suka yi a Sahel har zuwa yankin Yemen.
Ya ce annonar farin ta samu ne sakamakon ruwan sama mai tarin yawa da aka samu shekaru biyu da suka gabata, inda hakan ya bai wa farin sukunin kyankyashe ‘ya’ya masara iyaka.
Kumanin farin-dango bilyan 200,000 suka mamaye kasar Kenya. Kuma an kiyasta cewa a rana daya sukan iya cinye abincin da mutum milyan 84 za su iya cinyewa.
Farin sun yi mummunar barnar dubban daruruwan hektocin gonaki a Afrika ta Gabas.
Hukumar FOA na fargabar cewa yawan farin zai iya nunkawa sau 500 cikin watan Yuni, su yi yawan da za su iya mamaye amfanin gonakin Afrika ta Yamma baki daya, ko ma a ce kasashe 30.
Tuni dai an fara kokarin kaddamar da gidauniyar talladin dala milyan 311.6 domin a yi wa farin-dangon taron-dangi kisa da maganin kwari.
“Mu na bakin kokarin mu, amma aikin akwai wahala kuma zai iya daukar lokaci, tunda dai farin yawon mamaya su ke yi daga nan su nausa can. Za a dauki watanni kafin a kai ga samun nasara.”
Dongyu ya yi maraba da shirin samar da dala milyan 500 da Majalisar Dinkin Duniya ke kokarin yi domin yaki da farin-dango a Gabas ta Tsakiya da kuma Afrika.
Daga nan ya yi rokon ci gaba da bayar da gudummawa daga masu bayar da gudummawa a duniya.
Fargabar da ake ci gaba da yi shi ne, yadda a yanzu bilyoyin farin-dangon ke ci gaba da kyankyashe bilyoyin ‘ya’ya. Su kuma wadannan ‘ya’yan, nan da cikin watan Yuni za su yi girman da za su rika cinye shuke-shuke komai yawan su a duk gonakin da suka dira.
Hakan inji rahoton zai kara kawo mummnan matsanancin karancin abinci.
“Abin ya zama bugu biyu. Ga annobar Coronavirus ga kuma annobar farin-dango. Su duka za su kawo bala’in karancin abinci.” Cewar Dongyu.
Farin dango a wani rahoton za su cinye abincin mutum milyan 25 a Afrika ta Gabas, a Yemen za su cinye amfanin gona na abincin mutum milyan 17.