• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Ta Tabbata, Ba Wani Abu Yasa Suke Adawa Da Sarki Sanusi ba Illa Hassada! Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
June 16, 2020
in Ra'ayi
0
SALLAH: Hakimai Sun Bijirewa Sabbin Masarautun Ganduje A Kano, Daga Imam Murtadha Gusau

Sarkin Kano Sanusi

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai jinkai

Lallai dukkan godiya da yabo na Allah ne. Muna gode Masa, kuma muna neman taimakonSa da gafararSa. Muna neman tsarinSa daga sharrin kawunanmu, da munanan ayyukanmu. Lallai wanda Allah Ya shiryar, babu mai batar da shi, kuma wanda Allah Ya batar, babu mai shiryar da shi. Ina shaidawa babu abin bauta wa bisa cancanta, sai Allah, Shi kadai, ba Ya da abokin tarayya, kuma ina shaidawa Annabi Muhammadu (SAW), bawanSa ne kuma ManzonSa ne. Tsira da Amincin Allah su kara tabbata a gare shi da alayensa da sahabbansa baki daya.

Bayan haka, ya ku ‘yan uwa masu daraja, wani masani, mai hikimah yana fada a cikin wasu baitoci nasa masu cike da ilimi da hikimah cewa:

“Ana sa ran ko wace irin adawa ta kare, ta wuce, ta kwaranye, ta zama tarihi, a manta da ita, ta zamanto kamar ba’a yi ba, amma ban da adawar mutumin da yake adawa da kai saboda hassada, yace ita wannan adawa ba ta karewa har abada, matukar wanda ake yiwa hassadar yana raye, kuma yana ci gaba a rayuwarsa.”

‘Yan uwa masu girma, lallai idan muka dubi wadannan baitoci na hikimah, wallahi zamu ga cewa suna cike da ilimi da kuma gaskiya mai daci! Domin haka abun yake, in dai har ya kasance mutum yana adawa da kai ne haka siddan, babu wani dalili. Kawai yana adawa da kai ne saboda wata baiwa, ko wata daraja, ko wata daukaka da Allah yayi maka, to ban ga yadda za’a yi wannan adawa ta wuce ba, matukar kai da ake yiwa adawar kana nan cikin wannan daukaka da baiwa da ni’imah da Allah yayi maka.

‘Yan uwa na masu albarka, kowa yasan cewa na sha bayyanawa al’ummah cewa adawar da Gwamna Ganduje yake yi da Sarki Sanusi, wallahi adawa ce da ta samo asali daga hassadar da yake yiwa Sarkin, sanadiyyar daukakar da Allah yayi masa. A lokacin da nike fadar wannan magana, wasu suna ganin cewa ba gaskiya ba ne, to sai ga shi yanzu, alhamdulillah, muna raye, ya bayyana a fili karara cewa, abun da nike fadar ya tabbata gaskiya. Domin idan ba haka ba, a lokacin da Ganduje ya sha alwashin sai ya cire Sarki Sanusi daga sarauta, duk wani mutum mai mutunci da hangen nesa ya ja kunnen sa akan kar yayi haka, tun daga malamai da ‘yan siyasa, da manyan mu, da sauran su, amma ya ki ji, yaki ya saurare su, ya cire Sarki Sanusi. Bayan ya cire shi kuma, shi abun da yaso shine, ya ga Sarki Sanusi ya wulakanta, to sai Allah bai yarda da wannan mummunan nufi nasa ba, Allah ya kubutar da Sarki Sanusi, ya bar jihar Nasarawa ya koma birnin Legas. Tun a lokacin Ganduje yake ta yiwa Sarki Sanusi bita-da-kulli, a fili da kuma ta karkashin kasa, amma Allah yana dada kare shi daga dukkan wani abu da suka kulla.

Sannan duk duniya ta shaida hakuri da tawadu’u da tawakkali irin na Sarki Sanusi, domin duk wulakanci, da cin mutunci, da tozarci da suka yiwa Sarkin, suka cire shi daga gadon sarauta, sun zaci zai yi turjiya, yace bai yarda da sauke shi ba, ya tafi kotu, domin kalubalantar sauke shi din. To amma sai bai yi hakan ba, kuma ya dogara ga Allah tare da yin tawakkali gare shi, domin yasan shine mai yin komai. Kuma yayi jawabin goyon bayan wanda aka nada Sarki, kuma yayi kira ga dimbin magoya bayansa da masoyansa, cewa su goyi bayan wanda aka nada, kuma suyi masa fatan alkhairi, kuma yayi kira da kar wanda ya tada hankali, kuma alhamdulillah, an bi umurnin Sarki Sanusi akan wannan, kuma duk duniya ta shaida haka.

Sannan bayan wannan, tun da aka sauke Sarki Sanusi daga sarauta, babu wanda yaji yayi wata mummunar magana ga gwamnatin jihar Kano ko ga masarautar Kano. Ya manta da abun da ya faru, yaci gaba da harkokin sa.

Amma yanzu kwatsam, kuma sai muka ji Gwamna Ganduje yana cewa wai hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano za ta ci gaba da binciken Sarki Sanusi. Ko akan meye? Oho!

Domin babban sakataren yada labaran gwamnatin jihar Kano, mai suna Abba Anwar, shine ya fitar da wannan sanarwa jiya litinin, 15/06/2020 wadda ya sanya wa hannu. A ciki ya tabbatar da cewa Ganduje ne ya fadi wannan a ganawar da yayi da ‘yan jaridu a sashen gidan Afrika da ke gidan gwamnatin jihar Kano, ranar litinin 15/06/2020 (wato jiya kenan).

Sannan labarin da muka samu daga majiya mai tushe, kuma kwakkwara shine, cewa an yi wani taro ne domin a lalubo kuma a zakulo duk wata hanya da za’a yi amfani da ita a kullawa Sarki Sanusi sharri, kuma a kama shi da wani laifi don a tozarta shi. Kuma wannan labari ya tabbatar da cewa, Gwamna Ganduje ne yake tursasawa shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa na jihar Kano da yabi Sarki Sanusi da sharri, kuma ayi duk yadda za’a yi a zakulo wani laifin da za’a kama shi da shi, amma shi shugaban hukumar yana ja da baya, kuma yana dari-dari da lamarin, domin ya gano cewa jama’ah sun san cewa zaluntar Sarki Sanusi kawai aka yi, kuma bashi da wani laifi.

Ya ku ‘yan uwa masu daraja, abun tambaya anan shine, shin wai ba Gwamna Ganduje bane yake cewa Muhyi Magaji mutum ne mai cikakken ‘yanci, kuma wai yana cewa babu wanda yake sa shi ya binciki wani? To idan har abun da yake fada gaskiya ne, me yasa yanzu yake bashi umurnin ya binciki wani? Wannan ya nuna cewa kenan al’amarin duk siyasa ce kawai, kuma wannan ya nuna dama can shine yake sa su suci mutuncin mutane saboda wata manufa tasa ta siyasa.

Ya ku al’ummah, wallahi ku sani, duk wannan bita-da-kulli da suke yiwa Sarki Sanusi ba komai bane illa hassada. Domin idan ba haka ba, mutanen nan sun sauke shi daga sarauta, amma dai har yanzu ace sun ki su kyale shi, ba don komai ba sai don saboda dama can adawa ce ta hassada? Haba jama’ah! Wace irin al’ummah ce wannan da bamu nufin junan mu da alkhairi kullun, sai sharri?

Ya kamata dai mu sani, wallahi ita hassada ba ta da kyau, kuma wani mugun ciwo ne da ke nukurkusar mai yinta a cikin zuciyarsa shi kadai. Hassada ita ce jin zafi, daci, ko bacin rai a yayin da kaga wani dan’uwanka, ko makwabcinka, ko abokinka ko ma wani kawai da ka sani a duniya ya samu daukaka, ko wace iri ce. Kuma hassada ta kasu gida uku:

1. Akwai hassadar ganin kyashi, shine mutum yaji a zuciyarsa cewa don me wani zai fi shi wani abu a rayuwa; kudi, mulki, ilimi, daukaka ko kuma baiwa ko mukami ko wani matsayi.

2. Mutum yaji shi baya son kowa ya samu wani abun alkhairi ko wata karuwa sai shi kadai.

3. Mutum yaji cewa idan dai shi ba zai samu abu ba to gara kar kowa ya samu. Irin su sune suke yin a fasa kowa ya rasa. Kuma irin wannan hassadar tafi ko wace hassada muni da hadari.

Ya ku jama’ah, domin in fito maku da al’amarin a fili, don kowa ya fahimce shi, hassada ita ce ganin kyashi, ko nunkufurci, ko kiyayya. Kuma yawanci wanda ake yiwa hassada shine mutum mai abin hannu, ko mai ilimi, ko mai mulki, ko mai wani matsayi na addini ko na duniya. Kuma yawanci abin da yasa mutane suke yin hassada shine, rashin imani da tsoron Allah, rashin yarda da hukunci da kaddarar Allah, rashin kyakkyawan tunani, izza, ji-ji-da-kai, son girma, son shugabanci ko son nuna isa, da kazantar zuciya, mugunta, zalunci, rashin tarbiyyah da kuma mummunar dabi’a. Ina rokon Allah ya kare dukkanin Musulmi daga cutar hassada, amin.

Kuma hassada ita ce mutum yayi burin abin da ke wurin wanda yake yiwa hassadar na alkhairi, na abin duniya ne ko addini, ya gushe. Wannan haramun ne, domin yana cutar da jiki da addini. Allah, saboda Ya nuna tir din Sa da wannan dabi’a da masu yin ta, sai yace:

“Ko suna hassadar mutane ne a kan abin da Allah Ya ba su daga falalarSa…? [Suratun Nisa’i: 54]

Kuma Allah Mai girma da daukaka, Ya ja hankalinmu da neman tsari daga sharrin mai hassada, inda Yace:

“Da sharrin mai hassada, idan ya yi hassada.” [Suratul Falak: 5]

Kuma Manzon Allah (SAW), ya gargade mu kan matsalar hassada da irin illar da ke tattare da ita, a inda yace:

“Kashedin ku da hassada, saboda tana cinye kyawawan ayyuka kamar yadda wuta take cinye kiraruwa.” [Abu Dawuda ne ya ruwaito shi]

Sannan kuma ana neman tsari daga mai hassada a lokacin da ya bayyana mummunar manufarsa ta yin hassadar, domin mai hassada yana iya yin komai domin ganin ya cimma burinsa na sharri da mugunta.

Daga karshe dai ya kamata duniya ta fahimci abun da yake faruwa. Wadannan mutane sun sha alwashin sai sun ci mutuncin wannan bawan Allah, wato Sarki Sanusi. Sun sauke shi daga sarauta, sun dauka cewa hankalinsu zai kwanta, amma tun lokacin da suka sauke shi hankalinsu dada tashi kawai yake yi kullun, kuma talakawa sun gano su, shine yanzu suke kokarin fito da wata hanya kuma, don su huce haushin su akan Sarki Sanusi.

To su sani, in Allah yaso ba zasu taba cimma burin su ba. Domin shi dai Sarki Sanusi ba ya da kowa sai Allah. Kuma bai riki kowa ba sai Allah. Duk kuwa wanda ya rike Allah, to cin nasara akan sa zai yi wahala.

Kuma wai ma wani abun mamaki shine, su mutanen nan, duk wannan hali da arewa ta ke ciki na rashin tsaro, da yunwa, da talauci, da cututuka, sam bai dame su ba. Domin idan ba haka ba, yaya za’ayi a lokacin da ake ta kokari da fadi-tashin ganin arewa ta samu mafita daga halin da take ciki a yau, a samu lafiya da zaman lafiya, a samu hadin kai da kwanciyar hankali, wai a lokacin ne wadannan miyagun mutane za su fito da wata magana, wai za’a ci gaba da binciken Sarki Sanusi, kuma ba don komai ba sai domin mummunar manufarsu ta siyasa! Kai ma ka san cewa, wallahi wadannan mutane basu nufin Kano da arewa da alkhairi!

Daga karshe ina rokon Allah, muna tawassali da sunayensa tsarkaka, ya tausaya muna, ya karbi tuban mu, ya azurta mu da hakuri, juriya, jajircewa, zaman lafiya da ikon cin jarabawar sa a kan mu.

Ya Allah, kayi muna gafara, ka shafe dukkan zunuban mu, ka azurta mu da cikakken tsaro a yankin mu na arewa mai albarka, da ma Najeriya baki daya, don son mu da kaunar mu ga fiyayyen halitta, Annabin rahmah, Muhammad (SAW).

Ina rokon Allah ya kyauta, kuma ya kawo muna mafita ta alkhairi, kuma yayi muna maganin duk wani makiri, amin.

Dan uwan ku, Imam Murtadha Muhammad Gusau, ya rubuta daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa a lambar waya kamar haka: 08038289761.

Tags: AbujaAknoHausaLabaraiNajeriyaNewsSanusiSarki
Previous Post

ANA WATA GA WATA: Sirikin Ganduje, Sanata Ajimobi ya zama shugaban jam’iyyar APC

Next Post

Kare Rayuwa Da Dukiyoyin Al’umma Shine Amfanin Gwamnati Na Farko A Duniya, Daga Mustapha Soron Dinki

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
Mustapha Soron Dinki

Kare Rayuwa Da Dukiyoyin Al'umma Shine Amfanin Gwamnati Na Farko A Duniya, Daga Mustapha Soron Dinki

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati
  • Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki
  • TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna
  • Gwamnatin Kano ta hana lika fastoci a ginegine a fadin jihar
  • Sojoji sun kashe ‘yan ta’adda 58, sun kama wasu 161 a cikin makonni biyu a yankin Arewacin Najeriya

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.