• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Hadarin Girman Kai, Jiji Da Kai Da Raina Mutane, Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
June 8, 2020
in Ra'ayi
0
Murtadha Gusau

Murtadha Gusau

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jin Kai

Dukkan godiya ta tabbata ga Allah mabuwayi, tsarkkaken Sarki. Tsira da aminci su tabbata ga fiyyayyen halitta, Annabin karshe, Annabi Muhammad (SAW), da alayensa da Sahabban da kuma wadanda suka bi su da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.

Ya ku bayin Allah, wallahi, har kullun, ni dai ni kan yi mamaki idan na kalli dabi’u da halaye na wasu mutane, wadanda Allah ya jaraba da mummunar dabi’ar nan ta girman kai da jiji da kai da wulakanta mutane, ko kuma daukar mutane ba bakin komai ba.

Ya ku jama’ah, wallahi wadannan dabi’u munana ne ga ko wane Musulmi, ko ma in ce ga ko wane dan Adam, amma dai sun fi muni ga malamin addinin Musulunci, ko kuma wanda ya kira kan sa malami. Sam bai kamata ace malami ya tasirantu da wadannan dabi’u ba! Domin duk malantar malami da zarar Allah ya jarabe shi da wadannan dabi’u, to sai ka ga ya zama shirme wallahi.

Haba jama’ah, ace wai saboda girman kai da jiji da kai da raina mutane, sai ka ga mutum wai shi ba zai bari ace shi malami ba ne, a’a, da karfi da yaji sai ya nuna shi malami ne, wasu kuma ba malamai bane, wace irin dabi’a ce wannan? Kuma duk wannan ba komai yake jawo shi ba Illa, بطر الحق da غمط الناس wato KIN GASKIYA DA WULAKANTA MUTANE KO RAINA SU. Ina rokon Allah Subhanahu wa Ta’ala ya shirye mu, amin.

Ya ku bayin Allah, wallahi girman kai da jiji da kai, da wulakanta mutane dukkansu dabi’u ne munana wadanda addinin Musulunci ya yake su, kuma dabi’u ne ababen zargi masu kai mutum ga halaka cikin kankanin lokaci, banbanci da ke tsakaninsu kadan ne kamar haka:

Daga cikin alamun girman kai dai sun hada da, ka rinka ganin fifikon kan ka akan wani, ka rinka jin kafi wane, kai abu kaza ne, kafi karfin ko kuma ka wuce matsayin wane, kafi karfin sauraronsa, kafi karfin a hada ka da shi, da dai makamantan haka. Jama’ah kun ga a irin wadannan dabi’u babu tawadu’u, babu koyi da rayuwar Annabi (SAW) a cikin malanta, alhalin duk wani malami, komai girman sa, Annabi (SAW) yake gado kuma shine abun koyin sa; bai isa ya wuce gaban Annabi (SAW) wurin malanta ba, da zarar kuma yayi hakan, to sai muce ya halaka, Allah ya shirye shi!

Hoton rayuwar Manzon Allah (SAW) ita ce abun koyin mu, Annabi (SAW) shine abun son mu kuma abun kaunar mu.

Shi ma misalin jiji da kai shine, ka rinka jin kana da wani abu da waninka ba ya da shi. Dukkansu dai munanan laifuka ne da suke dauke bawa daga godewa Allah zuwa godewa kai, da jin cewa wayon mutum ko iyawarsa sune suke yi masa abu. Sannan suna hana mutum yabon Allah da gode masa kamar yadda ya kamata, sai mutum ya koma yabon kan sa, da mamakin kan sa, da kuma kin kaskantar da kai ga Mahalicci, da ruduwa da kai, da kin girmama mutane, da sanin matsayinsu, zuwa hantararsu, da danne masu hakkokinsu.

Sannan na daga illolin da jiji da kai yake haifarwa, akwai rusa ayyuka kyawawa, da kuma boye masu kyau, da kuma jawo zarge-zarge, da rashin yarda da rashin aminci tsakanin mutane.

Sannan hukuncin jiji da kai dai mun san haramun ne a Musulunci, domin nau’i ne na shirka kamar yadda malamai suka bayyana. Shaikhul Islam Ibn Taimiyyah yace:

“So da yawa riya tana da kusanci da jiji da kai. Ita riya tana babin shirka da halittu, shi kuma jiji da kai yana babin shirka da kai, wannan shine halin mai girman kai, mai riya, wanda bai tabbatar da fadin Allah madaukakin Sarki ba:
“ﺇﻳﺎﻙ ﻧﻌﺒﺪ”

Mai jiji da kai kuma bai tabbatar da fadin Allah madaukin Sarki ba, wato:
“ﻭﺇﻳﺎﻙ ﻧﺴﺘﻌﻴن”

Duk wanda ya tabbatar da fadin Allah “ﺇﻳﺎﻙ ﻧﻌﺒﺪ” zai fita daga riya, wanda kuwa ya tabbatar da fadin Allah
“ﻭﺇﻳﺎﻙ ﻧﺴﺘﻌﻴﻦ”
Zai fita daga jiji da kai.”

Ya ku jama’ah, lallai dabi’ar jiji da kai abun zargi ne a cikin Alkur’ani da Sunnah. Allah Madaukakin Sarki yace:

“ﻭﻳﻮﻡ ﺣﻨﻴﻦ ﺇﺫ ﺃﻋﺠﺒﺘﻢ ﻛﺜﺮﺗﻜﻢ ﻓﻠﻢ ﺗﻐﻦ ﻋﻨﻜﻢ ﺷﻴﺌﺎ”

Ma’ana:

“Da ranar yakin hunaini, lokacin da yawanku ya burge ku, kuma bai tsinana maku komai ba.

Abdullahi Dan Mas’ud yace:

“Halaka tana cikin abubuwa biyu: cire tsammani daga Allah da kuma jiji da kai.”

Ya ku bayin Allah, ku sani, wallahi hadarin jiji da kai ya kai hadari, domin idan ba ayi hankali ba yakan kai mai yin sa zuwa ga kafirci da fita daga addinin Musulunci, kamar yadda shaidan yayi alfahari da asalinsa, da ibadarsa, wannan yasa yayi wa Allah girman kai, kuma ya halaka.

Imam Ibn Qudamah yace:

“Ka sani jiji da kai yakan kawo girman kai, domin yana cikin dalilan da ke kawo girman kai, a cikin girman kai kuwa akwai masifu da yawa, akwai tsakaninka da halittu da kuma tsakaninka da mahaliccinka.”

• Abubuwan da suke sa a gane mai jiji da kai, kuma da zarar mutum yana da su, to lallai Allah ya jarabe shi da wadannan munanan dabi’u, sune kamar haka:

1. Kin gaskiya, da kin karbar ta, da kuma hantarar mutane.

2. Raina mutane.

3. Rashin shawartar masu hankali da manya a cikin al’amurra.

4. Yin rangwada, takama ko yanga a cikin tafiya, da nuna ji da isa.

5. Ganin girman biyayyar da mutum yake yiwa Allah, da kuma ganin yawanta.

6. Alfahari da ilimi da kuma yin gori dashi.

7. Alfahari da dukiya da dangi da kyawun halittar mutum.

8. Raina kokarin wasu Malamai masu ikhlasi da tsoron Allah.

9. Dawwama akan kuskure da kin karbar gyara.

10. Karancin sauraron ilmi ko mika wuya ga masu shi, da lazimtarsu, ko kuma kokarin yaudarar kai cewa shi yanzu ya gama karatu, alhali wannan karya ce.

11. Aga cewa kullun mutum yana hantarar masu sabo da masu zunubi, maimakon kokarin shiryar da su su daina.

12. Manta zunubai, da raina su, da ganin karancinsu.

13. Kokarin sabawa sauran mutane da gangan, don jin isa ko nuna isa.

• Abubuwan da ke janyo jiji da kai:

1. Jahilci.

2. Karancin tsantseni da tsoron Allah.

3. Raunin jin cewa Allah yana tare da kai kuma yana kallon ka.

4. Karancin wadanda za suyi wa mutum nasiha.

5. Mummunar niyyah.

6. Mutum ya rinka yawan jin dadin yabon mutane, ko kuma yin abu don samun yabon su, da kuma taimakon shaidan akan haka.

7. Fitinuwa da son duniya, da bin son zuciya.

8. Karancin tunani.

9. Karancin godewa Allah.

10. Karancin Ambaton Allah.

11. Rashin tadabburin Alkur’ani da kuma Hadisai.

12. Amintuwa da azabar Allah da dogara da afuwarsa da gafarar sa kadai.

Daga karshe, ‘yan uwa Musulmi, maganin girman kai da jiji da kai, da wulakanta mutane, ko raina su, shine, tuna ni’imomin Allah a kan mu, da kuma tuna yadda mutum yake a baya kafin ya kai matsayin da yake a halin yanzu, da kuma tuna tarihin al’ummomin da suka gabata, da kokarin karanta rayuwar Manzon Allah (SAW) da Sahabbansa, tare da kokarin yin koyi da su.

Ya Allah, muna tawassali da sunayenka tsarkaka, ka tausaya muna, ka karbi tuban mu, ka azurta mu da hakuri, juriya, jajircewa da ikon cin jarabawarka a duk inda muka samu kawunan mu, amin.

Ya Allah, kayi muna gafara, ka shafe dukkan zunuban mu, don son mu da kaunar mu ga fiyayyen halitta, Annabin rahmah (SAW).

Ina rokon Allah ya kyauta, ya kawo muna mafita ta alkhairi, amin.

Dan uwan ku, Imam Murtadha Muhammad Gusau, ya rubuto daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa a lambar waya kamar haka: 08038289761.

Tags: GusauHausaJiji da kaiLabaraiMurtadhaNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

KORONA: Daga 16 jihar Abia ta samu karin mutum 67 cikin kwana daya, Abuja 40, Yanzu mutum 12, 486

Next Post

Gwamnan Abia, Ikpeazu ya kamu Korona

Next Post
Gwamnan Abia, Ikpeazu ya kamu Korona

Gwamnan Abia, Ikpeazu ya kamu Korona

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Yadda ‘Ƴan bindiga suka sace fastocin cocin katolika biyu a Katsina
  • Dandazon Ƙudan zuma sun kashe wani ɗalibin makarantar Firamare a Kano
  • KOTUN KOLI TA KIRA WA AMAECHI RUWA: Dole ya bayyana gaban kwamitin Wike don amsa zargin handame naira Biliyan 98
  • HIMMA DAI MATA MANOMA: Rashin samun tallafi da lamuni daga bankuna bai hana mata hoɓɓasa wajen shiga harkokin noma ba
  • RAHOTO: Sama da mutum 3036 ke jiran a zartas masu da hukuncin kisa a Najeriya

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.