• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Abubuwan da ya kamata a sani game da tsarin amfani da dabaru biyu wajen yin rajistar masu zabe – Nazarin DUBAWA

    INEC ba za ta rufe rajistar zaɓen 2023 a ƙarshen Yuni ba – Farfesa Yakubu

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Teacher

    Gwamnati ta umarci makarantu su fara amfani da Tsarin Ƙara wa Malamai Shekarun Ritaya

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Abubuwan da ya kamata a sani game da tsarin amfani da dabaru biyu wajen yin rajistar masu zabe – Nazarin DUBAWA

    INEC ba za ta rufe rajistar zaɓen 2023 a ƙarshen Yuni ba – Farfesa Yakubu

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Teacher

    Gwamnati ta umarci makarantu su fara amfani da Tsarin Ƙara wa Malamai Shekarun Ritaya

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya ta gurfanar da Wadume gogarman garkuwa da mutane da mutum 6 a kotu

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
June 8, 2020
in Manyan Labarai
0
Hamisu Wadume

Hamisu Wadume

A ranar Litinin din nan ce Gwamnatin Tarayya ta gurfanar da gogarman masu garkuwa da mutane a jihar Taraba mai suna Bala Hamisu a gaban kotu.

An gurfanar da Hamisu wanda aka di sani da sunaWadume tare da wasu mutane shida, bayan sun shafe watanni goma cur a tsare.

An kama Wadume a Kano, bayan da ya tsere daga hannun ‘yan sanda, lokacin da sojoji suka bude musu wuta a wani gari mai suna Gidan Waya a jihar Taraba, cikin watan Agusta, 2019.

A Litinin din Nan bayan Mai gabatar da kara Shuaibu Labaran ya yi wa Mai Shari’a Nyako bayani, ya ce mutanen da ake zargin su 16 ne, amma bakwai kadai suka kama.

Dalilin Haka ne aka rage tuhumar da ake yi musu,daga 16 zuwa 13. Don haka sai ya nemi Mai Shari’a da ya same ranar da za a fara sauraren kara ka’in da na’in.

Wadanda aka gabatar din sun hada da Hamisu Bala (Wadume), Aliyu Dadje, Sufeto Umar Bala, Uba Bala, Bashir Waziri, Zubairu Abdullahi da kuma Rayyan Abdul.

Dukkan su bakwai din dai sun shaida wa kotu cewa ba su aikata laifin yin garkuwa, karbar naira milyan 106 kudin fansa, mallakar bindigogi 6 samfurin AK 47 ba tare da lasisin amincewa ba, da sauran su.

Sai dai kuma Sufeton ‘Yan Sanda na Kasa da Ministan Shari’a sun karbi gabatar da Shari’a har an yi masu karin tuhumar su da laifin fashi da kisa.

Kotu ta aza ranar 22 Ga Yuni za a fara sauraren shari’ar gadan-gadan.

WAIWAYE: Yadda Wadume Ya Tsere Kafin A Sake Kama Shi A Kano

An buga wannan bayani da ke Kasa tun a ranar 15 Ga Agusta, 2019.

DALLA-DALLA: Yadda gogarman masu garkuwa da mutane, Wadume ya tsere a kwale-kwale.

Wannan wani sabon binciken kwakwaf ne da PREMIUM TIMES ta gudanar, inda ta bankado harkalla, kulle-kulle da kisan-fin-karfin da sojoji suka yi wa zaratan ‘yan sanda uku, sannan suka kubutar da gogarman mai garkuwa da mutane daga hannun ‘yan sanda. Dama Hausawa na cewa “makashin ka na gindin ka.” Ku karanta ku ji yadda wannan jarida ta baje muku komai a kan faifai.

An yi wa wadannan zaratan ‘yan sanda masu zakulo masu garkuwa da mutane su uku kisan-gilla ne a daidai kauyen Gidinwaya, wanda ke tsakanin garin Ibi da Wukari a Kudancin Jihar Taraba.

Akwai shingen sojoji a kan kwalta, daidai Gidinwaya, kuma sojojin da ke tsaro da binciken motoci masu wucewa a Gidinwaya din ne suka bude musu wuta. Sojojin daga Bataliya ta 93 da ke Takum ne aka tura su domin aiki a shingen na kan kwalta.

Wannan kisan-gilla ya haifar da babbar barazana ga lamarin tsaron kasar nan tare kuma da haifar da rashin jituwa mai tsami tsakanin Sojojin Najeriya da ‘yan sandan Najeriya.

Jami’an ‘yan sandan da aka bude wa wuta sun a tafiya ne a cikin wata fatar mota bas, sun fito ne daga Ibi, inda suka kamo wani rikakken mai garkuwa da mutane mai suna Hamisu Bala, wanda aka fi sani da Wadume.

Rahoton Wakilin PREMIUM TIMES daga wurin da aka yi kisan

Wakilin PREMIUM TIMES ya ziyarci har wurin da sojoji suka kashe ‘yan sandan a Gidinwaya da ke kan titin Ibi zuwa Wukari.

Binciken da ya yi a can da za ku karanta a yanzu, har da ikirarin da mutanen kauyen suka yi, wadanda ya tattauna da su dangane da yadda abin ya faru.

Binciken PREMIUM TIMES a kauyen ya sha bamban da abin da sojohi suka bayyana cewa ya faru a kauyen na Gidinwaya.

A halin da ake ciki a yanzu, kauyen Gidinwaya kewaye ya ke da sojoji, wasu a kwak-kwance cikin shirin damarar yaki a cikin daji, tsallaken inda aka bindige ‘yan sandan. Sun sa-ido sosai su na lura da yadda mazauna kauyen ke gudanar da harkokin su.

Mutanen kauyen su kuma su na cikin tsaro da fargabar abin da zai iya samun su idan suka fai gaskiyar abin da ya faru dangane da kisan Sufeto Mark Ediale, Sajen Usman Danzumi da Sajen Dahiru Musa. Sai kuma wani farar hula mai suna Jibrin da shi ma a lokacin sojojin suka harbe su tare.

SOJOJI KO ‘YAN SANDA: Wa ya fara buɗe wuta

A sanarwar da Kakakin Yada Labarai na Sojojin Najeriya, Sagir Musa ya fitar ranar Larabar makon jiya, ya bayyana cewa sojoji sun yi tsammanin masu garkuwa da mutane ne. Kuma an tsayar da su, amma suka ki tsayawa. Sannan kuma Sagir ya ce ‘yan sandan ne suka fara bude wa sojojin wuta.

Wasu shaidu guda biyu sun tabbatar wa PREMIUM TIMES cewa ‘yan sandan ba su bude wa sojoji wuta ba, kamar yadda su mahukuntan sojojin suka yi ikirari.

Amma kuma shaidun sun tabbatar wa wakilin PREMIUM TIMES cewa ‘yan sandan ba su tsaya a shingen sojojin ba.

An bindige ‘yan sandan kamar mita 100 daga inda shingen sojojin ya ke.

Yadda yaran Wadume Suka riƙa bin Ƴan sanda a baya tun daga Ibi

“Wato su yaran Wadume sun rika bin motar da ‘yan sanda suke ciki dauke da ogan su tun daga Ibi, bayan da suka kamo shi daure da ankwa.” Haka wata kwakkwarar majiya ta shaida wa PREMIUM TIMES, kuma majiyar ta ce a kan idon ta al’amarin da ya faru a Gidinwaya ya faru.

“Su yaran Wadume ne suka shaida wa sojojin da ke shingen bincike a nan Gidinwaya cewa farar mota bas da ke a gaban su, masu garkuwa da mutane ne suka sato Alhaji Hamisu Wadume. Dama kuma shi Hamisu Wadume din sojoji duk sun san shi farin sani, za su iya yin komai domin su kare lafiya ko ran sa.”

Majiyar ta ce daga nan ne sai sojojin suka shaida wa abokan aikin su da ke shingen kan hanya da ke daidai Gidinwaya cewa wato shinge na biyu, wadanda su din ne suka bi su, suka bindige su.

Majiyar PREMIUM TIMES ta shaida wa wakilinmu cewa farar hular da aka kashe mai suna Jibrin, wani magini ne, kuma ya ma san shi sosai. Ya ci gaba da yi wa wakilin mu karin bayanin cewa Jibrin ya na kwarmata wa ‘yan sanda masu kamo ‘yan garkuwa duk wani sirrin yadda za a kamo su.

Tags: AbujaKidnappedKidnappersNajeriyaPREMIUM TIMESTarabaWadume
Previous Post

Buhari ya dakatar da fara aiki da Dokar Tilasta Cin-gashin-kan Majalisu da Bangaren Shari’ar Jihohi -Gwamna Fayemi

Next Post

Sama da mutum 500 cikin mutum 979 da suka rasu a Kano duk Korona ce sanadi

Next Post
KORONA: An samu karin mutum shida da suka rasu a Kano

Sama da mutum 500 cikin mutum 979 da suka rasu a Kano duk Korona ce sanadi

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Ka zo ka yi mini mataimaki kawai – Kwankwaso ga Peter Obi
  • RIKICIN KWANCE WA ATIKU ZANI A KASUWA: Rundunar PDP ɓangaren Wike sun nemi a tsige Ayu, Shugaban Jam’iyya
  • YADDA KALLO YA KOMA OGUN: Obasanjo ya karaɗe Abeokuta ya na ɗaukar fasinja da Keke NAPEP
  • Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo
  • Mutum 77 sun kamu da Kanjamau a jihar Taraba

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.