Idan ba manta ba sanata Abiola Ajimobi ya rasu a wani asibiti a jihar Legas, bayan fama da yayi da rashin lafiya na gajeran lokaci.
Kafin ya rasu Ajimobi ne sanatan da ke wakiltar Shiyyar jihar Oyo a majalisar dattawa.
An yi jana’izar sa da 12 na rana ne a Oke-Ado, dake ibadan.
Wadanda suka halarci jana’izar sun hada da Kunle Saani, Sheikh Muideen Bello, babban limamin masallacin Ibadan, Sheik Abubakri Abdulganiyu Agbotomokere da wasu manyan malamai.
Ya rasu ya bar matar sa Florence Ajimobi da kuma ya’ya biyar.
Daya daga cikin ‘ya’yan sa Idris Ajimobi ya auri diyar gwamnan Kano Abdullahi Ganduje, Fatima Ganduje.
Allah ya ji kan sa, Amin.