• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Mu yi koyi da tawali’un Manzon Allah (SAW), Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
May 5, 2020
in Ra'ayi
0
Imam Murtada Gusau

Imam Murtada Gusau

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jin Kai

Dukkan godiya ta tabbata ga Allah mabuwayi, tsarkakakken Sarki. Tsira da aminci su tabbata ga fiyayyen halitta, Annabin karshe, Annabi Muhammad (SAW), da alayensa da sahabbansa da kuma wadanda suka bi su da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.

Ya ku ‘yan uwa na masu girma, masu albarka, masu daraja, lallai mu sani, Manzon Allah (SAW) ya kasance mai gayar tawali’u, mai gayar kankan da kai. Yazo a cikin tarihinsa cewa, saboda gayar tawali’unsa, mafi yawan lokuta shi yake yiwa kansa hidima, kuma yakan taimaka wa iyalinsa a cikin ayyuka na yau da kullum na cikin gida. Akwai ma wani Sahabinsa da yake cewa, sun je kasuwa tare da Manzon Allah (SAW), sai yayi sayayya, sai yayi nufin ya rike masa abin da ya saya din, sai Manzon Allah (SAW) yace, a’a, sai dai ya rike da kansa. Har yake ce masa ma’abocin abu shi yafi cancanta da ya dauki abinsa. Haka nan yazo a kan cewa, akwai lokacin da Annabi (SAW) ya ziyarci Sahabinsa mai suna Sa’ad Dan Ubadah, da zai koma sai ya kawo dabba domin Manzon Allah (SAW) ya hau, sai ya hada shi da dan sa mai suna Qais domin ya raka shi.

Sai Manzon Allah ya hau dabbar yace wa Qais din ya hawo. Sai Qais din yace, a’a. Sai Manzon Allah (SAW) yace masa ko dai ya hawo, ko ya koma. Wato saboda Manzon Allah (SAW) ba ya son ya kasance shi yana tafiya kan dabba alhali shi kuma Qais yana bin sa a kasa. Wannan shi ma ya nuna tawali’u na Manzon Allah (SAW).

Akwai wani lokacin da suna cikin tafiya da Abdullahi Dan Abbas, sai ya kasance yana tafiya a bayansa, sai Manzon Allah (SAW) yace masa yazo daura da shi, sai abin yayi wa Abdullahi Dan Abbas nauyi, amma kasantuwar ya ga haka Manzon Allah (SAW) yake so, sai yazo daura da shi din suka ci gaba da tafiya, wanda shi ma wannan yana alamta muna tawali’un Manzon Allah (SAW).

Akwai lokacin da Manzon Allah (SAW) yayi tafiya shi da wasu Sahabbansa, sai suka bukatu da su yanka dabba, sai wani cikinsu yace shi zai yanka dabbar, wani yace shi zai yi fida, wani kuma yace shi zai daddatsa ta, sai Manzon (SAW) yace; “Ni kuma zan nemo itacen da za’a dafa naman.” Mu dubi irin wannan tawali’u na Manzon Allah (S’AW). Akwai misalai da dama na tawali’unsa (SAW) ta fuskoki daban-daban, da lokaci ba zai bani damar kawo wa ba.

Ya ku jama’ah, wallahi Annabi (SAW) ba ya raina kowa. Ba ya wulakanta Dan Adam, sannan yana ba wa kowa girmansa da hakkinsa. Lallai da ace mutanen duniya za su yi koyi da tawali’un Manzon Allah (SAW), to da duniya ta zauna lafiya da taimakon Allah!

Sannan Manzon Allah (SAW) ya kasance bai taba cewa da mai yi masa hidima don me kayi kaza ba, sai dai yace; da kayi kaza da yafi.

Annabi (SAW) yana kiran kowa da kinayarsa domin girmamawa, yana sanya kinaya ga marasa kinaya, yana bawa wanda ya shigo wurinsa da matashinsa, idan kuwa yaki amincewa sai ya rarrashe shi har sai ya karba.

Manzon Allah (SAW) yana fitowa bayan bullowar rana, domin yanayin addu’a ne tsakanin alfijir da bullowar rana. Sannan idan ya shiga gida sai ya zauna a farkon wurin da ya samu a kowa.

Abun tambaya anan shine, shin don Allah yanzu haka muke? Shin don Allah muna yin koyi da Manzon Allah (SAW) a halayensa da tawali’un? Ya Allah, ka ba mu ikon yin koyi da halaye irin na Manzon Allah (SAW), amin.

Ya ku ‘yan uwa na masu daraja, kar mu zamanto marasa tawali’u, kar mu zamanto masu girman kai, kar mu zamanto masu raina bayin Allah ko masu wulakanta su saboda Allah ya bamu ilimi, kudi ko mukami. Mu sani, komai kudin ka, komai ilimin ka, haka ko wane irin mukami kake dashi, wallahi idan ka mutu ba’a rufe ka da ko kwabo. A yau kana iya sa shaddar dubu dari, amma da zaran ka mutu, da yadin dari biyu za’a rufe ka dashi. Ka mallaki bene hawa bakwai, amma idan ka mutu kabarinka bai wuce tsawon kafa biyu. Jikin nan naka da kake ta faman yiwa kwalliya, ka sani, da zarar ka mutu zai zamo abincin tsutsa ne. Komai kyawon halittar ka sai ka rube kamar yadda abinci ke rubewa ya zamo datti.

Kuma munin halittar ka ba yasa ayi maka likkafani dabam da na saura, wai don kadan ji sassauci.

Komai ilimi, kudi, mulki, karfi ko sarautarka, ba yasa a kara maka koda dakika idan kwanan ka ya kare. Komai dabarar ka sai ka mutu, don haka ‘yan uwa, mu rinka ganin darajar junanmu, kada mu bari duniya ta shagaltar damu har mu kai ranar da wani zai yi muna wanka sabanin kan mu, wani yasa muna tufafi sabanin kan mu, wani yayi muna tsarki sabanin kan mu, mu kasance a saman kafafun mu maimakon tafiya da kafafun wani, don ita duniya ba madawwama bace, don haka komai dadin kasuwa dole ta watse haka ma komai dadin duniya dole mu bar ta, ko muna so ko bamu so. Fatan mu shine, Allah yasa mu lashe jarrabawar duniya kamar lomar tuwo. Amin.

Ya Allah muna rokon ka, don tsarkin Sunayen ka, don so da kaunar da muke yiwa Manzon ka (SAW), Ya Allahu, Ya Rahmanu, Ya Hayyu, Ya Qayyumu, Ya Zal Jalali Wal Ikram, Ya Allah, muna tawassuli da ibadar da muke yi maka ta azumin wannan wata na Ramadan, Ya Allah ka kawo wa al’ummar Jihohin Zamfara da Kano, da dukkanin Jihohin Najeriya, da dukkanin ‘yan Najeriya baki daya dauki na musamman daga wurinka. Ya Allah, mun tuba, mun tuba, mun tuba, ka karbi tuban mu, ka gafarta muna, ka yafe muna, ka jikan mu, ka tausaya muna, ka dauke muna wannan jarabawa, ka yaye muna wannan musiba ta wannan annobar cutar coronavirus.

Ya Allah, mun yarda, mun amince, mun yi ikirari, cewa mu masu laifi ne, mu masu zunubi ne, mu ba kowa bane, mu masu rauni ne, Ya Allah, mun saba maka, mun kauce hanya, mun yi ba daidai ba, mun ki bin umurninka, Ya Allah ka tausaya muna, ka yaye muna wannan cuta ta annobar covid-19. Ya Allah, bamu da karfi, bamu da wayo, bamu da dabara, ina rokon ka, duk wanda ka jaraba da wannan cuta ta wannan sabuwar annoba, ya Allah, ka yaye masa ita. Ya Allah, duk wanda ka saukar wa wannan ibtila’i a gare shi, Ya Allah, ka warkar da shi. Ya Allah, duk Musulmin da suka rasu a cikin wannan jarabawa, Ya Allah duk wadanda ka karbi ran su sanadiyyar wannan cuta, Ya Allah, ka jikan su, ka yafe masu, ka haskaka kabarinsu, ka karbi shahadarsu, kayi masu sakamako da Aljannah Firdausi. Ya Allah, ka ba wa iyalansu, da ‘yan uwansu, da abokan arziki hakurin jure wannan rashi, amin.

Ina rokon Allah ya kyauta, ya kawo muna mafita ta alkhairi, amin.

Dan uwan ku, Imam Murtadha Muhammad Gusau, ya rubuto daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa a lambar waya kamar haka: 08038289761.

Tags: AbujaHausaLabaraiManzon AllahNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

CORONAVIRUS: A daidai a na sassauta dokar hana walwala, Najeriya na tattagar karin wadanda suka kamu fiye da a baya

Next Post

Kashi 90% na wadanda suka kamu da Coronavirus a Kaduna Almajirai ne da aka jijjibo daga Kano

Next Post
Muyiwa, Hadiza and El-Rufai

Kashi 90% na wadanda suka kamu da Coronavirus a Kaduna Almajirai ne da aka jijjibo daga Kano

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • KATSINA BA DAƊI: Mahara sun buɗe wa tawagar Buhari wuta a yankin da su ka bingige Kwamandan ‘Yan Sandan Dutsinma
  • Takardun sakandare na sun yi layar-zana, amma ina da sakamako mafi kyau -Okowa, mataimakin takarar Atiku
  • HAJJIN BANA: Hankulan maniyyatan Kano 1,238 ya tashi saboda kasa kwashe su kan lokacin rufe filin jirgi Jeddah
  • IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi
  • 2023: Ka zaɓi El-Rufai mataimaki, ‘ka yi nasara a zaɓe kamar yankan wuka’ – Kira ga Tinubu

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.