Gwamnatin jihar Kaduna ta maida Almajirai ‘yan asalin jihar Zamfara 45 zuwa garin Gusau.
Kwamishinan harkokin yara, mata da ci gaban al’uma Zainab Lawal ta karbi wadannan almajirai a madadin gwamnati jihar Zamfara.
Duka wadannan almajirai an taho da su ne daga garin Zariya inda daga cikinsu akwai maza 28 da mata 17 kuma an karbe su a sansanin alhazai dake garin Gusau ranar Litini.
Ta kuma ce gwamnan Bello Matawalle ya kafa kwamiti domin kula da walwala da kuma ganin cewa duk almajiran da za a dawo da su an kai su ga iyayensu.
Zainab ta yi kira ga iyaye da su daina tura ‘ya’yansu wani gari ko kuma jihar yin barace-barace da sunan karatun addini.
Bayan haka kwamishinan yada labarai Sulaiman Tunau ya ce an yi wa duk almajiran gwajin cutar korona kuma dukkan su basu dauke da cutar.
Discussion about this post