• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Ba ni da ra’ayin takarar shugaban kasa, lokacin da aka zabe ni gwamnan Kaduna gashin kai na baki wul yanzu duk furfura – El-Rufai

    KALAMAN ƁATANCI GA ANNABI: Duk wanda ya yi zanga-zangar addini a Kaduna zai ɗanɗana kuɗar sa – Gargaɗin El-Rufa’i

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    Malami ya janye daga takarar gwamnan Kebbi duk da kurin da ya rika yi wai jama’a suka tilasta shi ya fito

    Chris Ngige

    Ngige ya janye takarar shugaban ƙasa, ya zaɓi ci gaba da zama ministan Buhari

    ZAƁEN 2023: APC za ta iya faɗuwa zaɓe idan ba ta tashi tsaye ba -Buhari

    ALAMOMIN WATSEWAR ƊAURIN TSINTSIYA A KANO: Mataimakin Kakakin Majalisa ya fice daga APC, ya koma PDP

    Ƴan Tiwita sun ce ba za su zaɓi Atiku ba saboda ya goge sakon yin tir da kisan Deborah da ta yi Ɓatanci ga Annabi

    Ƴan Tiwita sun ce ba za su zaɓi Atiku ba saboda ya goge sakon yin tir da kisan Deborah da ta yi Ɓatanci ga Annabi

    ƁATANCI GA MANZON ALLAH: Gwamnatin Sokoto ta rufe kwalejin Ilmi na Shehu Shagari

    ƁATANCI GA MANZON ALLAH: Gwamnatin Sokoto ta rufe kwalejin Ilmi na Shehu Shagari

    ‘Kowa Ya koma Gona’, amsar Buhari da aka ce masa bai taɓuka komai a bunƙasa tattalin arziki ba

    Buhari ya umurci Gwamnan CBN, Emefiele da jami’an gwamnati da ke takarar kujerun siyasa su ajiye aiki

    gunmen

    ‘Yan bindiga sun saki faston cocin Katolika da suka sace bayan an biya miliyoyin naira kuɗin fansa

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Ba ni da ra’ayin takarar shugaban kasa, lokacin da aka zabe ni gwamnan Kaduna gashin kai na baki wul yanzu duk furfura – El-Rufai

    KALAMAN ƁATANCI GA ANNABI: Duk wanda ya yi zanga-zangar addini a Kaduna zai ɗanɗana kuɗar sa – Gargaɗin El-Rufa’i

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    Malami ya janye daga takarar gwamnan Kebbi duk da kurin da ya rika yi wai jama’a suka tilasta shi ya fito

    Chris Ngige

    Ngige ya janye takarar shugaban ƙasa, ya zaɓi ci gaba da zama ministan Buhari

    ZAƁEN 2023: APC za ta iya faɗuwa zaɓe idan ba ta tashi tsaye ba -Buhari

    ALAMOMIN WATSEWAR ƊAURIN TSINTSIYA A KANO: Mataimakin Kakakin Majalisa ya fice daga APC, ya koma PDP

    Ƴan Tiwita sun ce ba za su zaɓi Atiku ba saboda ya goge sakon yin tir da kisan Deborah da ta yi Ɓatanci ga Annabi

    Ƴan Tiwita sun ce ba za su zaɓi Atiku ba saboda ya goge sakon yin tir da kisan Deborah da ta yi Ɓatanci ga Annabi

    ƁATANCI GA MANZON ALLAH: Gwamnatin Sokoto ta rufe kwalejin Ilmi na Shehu Shagari

    ƁATANCI GA MANZON ALLAH: Gwamnatin Sokoto ta rufe kwalejin Ilmi na Shehu Shagari

    ‘Kowa Ya koma Gona’, amsar Buhari da aka ce masa bai taɓuka komai a bunƙasa tattalin arziki ba

    Buhari ya umurci Gwamnan CBN, Emefiele da jami’an gwamnati da ke takarar kujerun siyasa su ajiye aiki

    gunmen

    ‘Yan bindiga sun saki faston cocin Katolika da suka sace bayan an biya miliyoyin naira kuɗin fansa

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

ƘALUBALEN TAFIYATA DAGA KANO ZUWA ABUJA: Yadda manyan titinan Najeriya suka zama kasuwar hada-hadar naira tsakanin direbobi da jami’ai

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
May 30, 2020
in Babban Labari, Ra'ayi
0
ƘALUBALEN TAFIYATA DAGA KANO ZUWA ABUJA:  Yadda manyan titinan Najeriya suka zama kasuwar hada-hadar naira tsakanin direbobi da jami’ai

Ko shakka babu, kowa zai yadda da ni cewa dokar zama wuri ɗaya (lockdown) a sakamakon cutar Kwaronabairus ta tada ƙura tuli wadda ta sa mutane ba sa iya ganin gabansu balle kuma sanin ina suka nufa a sakamakon hakan an samu ƙalubale masu yawa ta fuskar kasuwanci da rashin kewayawar kuɗi a hannun al’umma tare da ma rashin samun albashi ga masu aiki a kanfanoni da masana’antu da makarantun masu zaman kansu.

Sannin kowa ne cewa gwamna Nasir El-Rufa’i na jihar Kaduna na sawun gaba-gaba wajen yaƙi da cutar da al’umma kansu har yau ke kokwanton ko ma akwai ta a gaske a garuruwansu ko dai ita ma cutar tana yin abin nan ne na “mutuwa ɗauki ran matsokaninki” saboda tana kama masu ziyare-ziyaren ƙasashen waje kaɗai da muƙarrabansu. Wannan ta sa wucewa ta Kaduna daga Kano zuwa Abuja tamkar tsallaka siraɗi ne mai ƙarfin tsarga zuciyar matafiya da damuwa. Wannan ta sa a yau nake son ba ku labarin irin ƙalubalen da na sha a wannan hanya ta Kano-Kaduna-Abuja tare da bayyana ra’ayina a kan wasu muhimman al’amura kamar haka:

Kamar kodayaushe, bayan sallar Asuba, a kan ɗan sake rintsawa. Hakan kuwa ce ta faru a wannan rana ta Juma’ar 19 ga watan Mayu, 2019. Inda, da misalin ƙarfe 6:30 na hantse baccina tare da miƙewa don yin shirin karyawa. Saidai na fara da saka cajin waya domin na kwana wayata na ƙugin “battery low” kamar cikkunan talakawan Nijeriya saboda yunwa.

Kwatsam! Sai tunanin yin tafiya ta faɗo min kasancewar a baya na yi niyyar tafiya kuma har mota na hau a tasha, amma tun a hanya motar ta lalace, ga kuma batun rufe hanya da aka yi. Wannan ta sa dole muka yo mi’ara-koma-baya. A yau, sai na ce bari na kira ɗan kamashon motocin hayar don jin ko ya yanayin tafiya take tun da Kano a buɗe take? Nan take Muhamman Sani ya tabbatar min da cewa har mota ɗaya ta yi gaba, ma’ana akwai tafiya kenan. Wannan ta sa ni yin gaggawar sanar da mahaifiyata don tahowa. Nan kuwa ta amince kuma na yi futar burgu sai tashar Na’ibawa da ke Kano ba tare da sanar da aminina ba Abdulhadi wanda tare da sauran abokaina kan raka ni hawa adaidaita-sahu.

Da zuwa na tarar da fasinjoji danƙam kamar waɗanda suka taru don karɓar tallafin gwamnati na hatsi ko kuɗi.

Tallafin da minista Sadiya ta Hukumar ba da Agaji tai iƙirarin tana rabawa, amma fa irin rabon nan na namu-namu su tattaho, sannan na nasu-nasu su warwatse domin kuwa kam cikin garin Kano ina tabbatar da ba wanda ya ga ko ƙeyar wanda ya ga wanda ya karɓi wannan tallafi. Kamar dai yadda ba wanda ya san wanda ya san wanda ya san wanda ya kamu da cutar Kwarona kuma aka kwantar da shi a Kano. Na matsa muka gaisa da Muhamman Sani wanda ya nuna min motar da zan hau tare da cewa an yi min ragi na 1000 a maimakon 5,000 da ake biya. Ni ko daɗi ma ban ji ba, domin ko a baya ma da man fetur ke tsada ainun kamar guzurin mayya, ina biyan naira 2,000 ne kuma ko da lokacin Kintsa-Mushe ne, to ba ya wuce 3,000, ba yanzu da man fetur ya karye warwas. Haka nan na biya kuma na shiga mita kamar sauran fasinjoji a kan tsadar kuɗin mota. Shi kuwa direban, wani farin matashi mai hanci, ustazu, domin ko a mota karatun ƙur’ani ya sa mana duk da aljihun baya na da yawa a motar bai gajiya ba wajen ba mu haƙuri da cewa; “ba ku san ya hanyar nan take ba ne.” Mu kuwa, wasunmu na amsawa da, “ba wani nan. Kawai dai don kun ga Kwarona ne.”

Tun a hanya, ƴan karota suka karɓe wata takarda mai ɗauke da sunayenmu wacce ta ke kamar tikitin kulob wacce in ba ita ba shiga, in ba ita ba fita. Tun kafin fita daga Kano direban nan fa ya yar da hanya ya ɗau wata da ta nausa jeji.

Kamar kodayaushe, ina gaban mota, don ban cika girma da tsayi ba, don haka gaban mota daga tsakiya ke kasancewa wajen zamana. Nan na tambaye shi mai ya sa, sai ya ce min, “akwai kotun tafi da gidan ka da kuma jami’an tsaro. Muna zuwa za su tattare mu da maka mana tara ta dubu goma. Nan ma fa kowa yai tsit, aka zuba wa saurautar Allah ido. Shi kuwa ya yi ta bin daji da ƙauyuka da muke ta ratsawa wanɗanda ta kaici ya kamani nake cewa; “ko ina masu neman wa za su taimaka wa? Ga masu neman taimako nan kuma musulmai!

A haka muka ɓulla Zariya kuma muka fara cin karo da ƴan sanda waɗanda ke karɓar a ƙalla daga naira 200 zuwa sama. Kai! Jami’in tsaro na farko ne ya fi ɗaure min kai shi ne na hukumar FRSC wanda ya tubure kan cewa shi ba zai karɓi komai ƙasa da ɗari biyar ba, haka ya karɓi muƙullin motar tare da shan kunu. Nan na jiyo su kamar ƴan kasuwa suna ciniki da direbanmu har aka daidaita a ɗari bakwai.


Haka nan duk inda muka tsaya, dama jawabin shi ne “yi abin arziƙi ka wuce.” Kaina bai gama ɗauruwa tamau ba, sai da muka zo cikin Kaduna, inda muka tarar da KOTUN TA FI DA GIDANKA sun kafa rumfa a bakin hanya ga kuma jami’an tsaro sun cike ko’ina, sai hayaniya da tsawar muryarsu ake ji, sun ma mance da haƙƙin ɗan’adam na kar a tsorata shi haka nan.

Bayan mun isa na ga hankalin direbanmu ya dugunzuma sosai kamar wanda ƴan boko haram suka tare a Damaturu, sai na tambaye shi me ya faru, nan fa ya shaida min cewa, to a mun zo kotu, kuma sai mun biya naira 10,000 ko ma fiye za mu wuce.

Su fa kotun ta fi da gidanka a bisa tsari na aikinsu kamar yadda na ji wani masani ya faɗa shi ne, su kama masu karya doka tare da yi musu tara wanda gwamnati za ta sanar da kuɗin, sannan kuma su tabbata masu ababen hawan sun biya tare da JUYAWA BAYA SU KOMA INDA SUKA FITO, amma ina, a wannan kotu, na ga yadda ake zabga ciniki kamar a kasuwar ƙwari. Domin da farko direbanmu kasancewar sa Bakano ne mai son naira, sai ya fara da ƴan dabaru, inda ya ajiye motarsa tare da takawa har wurin. Da ƙarasawarsa ya dubi wani jami’in tsaro ya karanta masa bayani, shi kuwa da yangarsa ya sanar masa cewa, to fa in yana so ya taimaka masa wajen biyan 5,000 a matsayin kuɗin tara, to fa “ya yi abin arziƙi,” wato sabuwar hanyar karɓar na goro. Nan fa direban ya ciro dubu guda masu dattijai biyu ya sinna musu ita. Da amshewarsa kuwa, sai ya ce, “yanzu ka yi magana!”

Alƙalan dai su uku ne zaune a kan kujerar roba suna ta hada-hada, nan fa suka shiga daka tsawa suna cewa ina motarka? Shi kuma yana amsawa da tana baya saboda “go slow.” Abin ka da masu haɗin baki, sai jami’in nan ya yi masa raɗa kunnensa. Raɗa kuwa tun muna yara muke ji ana cewa, “mai raɗa, mai raɗa ɗan wuta, mai ji, mai ji kafiri.” Amma haka nan suka yi suka gama. Da ƙyar da tsawa, wai su ga masu gaskiya, suka yadda suka karɓi naira 5,000 tare da ce masa ya je. Amma Bakano da wayo, sai ya ce, “yallaɓai ina rasiti?” Sai fa yallaɓai ya ɓata fuska ya rubuta ya miƙa masa. A jiki na ga an sa naira 10,000, amma fa mu 5,000 muka biya. Da dawowa wurin mota, sai ya ce kowa ya shiga, nan muka wuce, babu wanda ya ma tuna da wata “social distancing,” domin a motar huɗu-huɗu-uku aka yi irin na ƴan ƙwallo.
Abin takaici kuma shi ne, na ɗauka batun cin hanci ya ƙare, amma sai na ga duk inda muka tsaya sai su ce mana ina rasiti? Direbanmu kuma ya nuna, sai ka ga sun yi wata bazaurar dariya sun ce “yauwa, wannan na laifin shigowa ne, sauran kuma alherinmu!” Kuma su fa ba sa karɓar naira 100 sai fa manyan kuɗi kamar 500 zuwa sama. Nan na ji tausayin direba ya kama ni. Duk da na san ya karya doka na ɗaukar mu ya biyo hanya saboda dokar kulle, to amma su kuma jami’ai da kotunan can su kuma mene ne HUKUNCINSU? Abin ɗaure kai kuma wasu jami’an, ko takunkumi ba sa sawa, balle wani tazara. Wasu direbobin dai kan dakata ne daga nesa, har zuwa biyar na yamma bayan kotunan kan hanya sun ci kasuwarsu sun tashi, sannan sai su zo su wuce salin-alin, sai fa sauran jami’an tsaro waɗanda da ka ba su “abin arziƙi” to ko bindigogi ne direba ya ɗebo zuwa Katsina ko ma Sakkwato inda ake ta KASHE al’umma, to fa ya sha kenan, in ji yara masu wasan langa. Kuma ko da a daren ranar Alhamis a kano, haka ƴan sanda suka tare mu a mashin mai-ƙafa-uku bayan mun dawo da misalin ƙarfe 10:00 na dare daga duba ɗan uwanmu da ya karye kuma babu wani bincike, sai suka ce mana mu yi abin arziƙi kawai mu wuce. Ba sa son mu ɓata musu lokaci. Ya Ilahi, ta haka za a samu CIKAKKEN TSARO A ƘASA BAYAN JAMI’AN ABIN DA YA DAME SU SHI NE NA GORO KAWAI.

Ni dai da haka na iso Suleja, na gode wa Allah. Tun da dai Kanon ma kasuwancin ya tsaya ga ƴan kuɗaɗena na albashi sun tasamma ƙarewa saboda zaman ƙulle na dole. Wai a haka, ma ni da sauƙi sosai.

Domin ma’aikatan da gwamnati ta zabtare wa albashi na san yanzu sun ɗan cinye abin da ya shigo musu na watan; maimakon su ga tallafi, sai ma su ke ba wa gwamnatin tallafi. Wannan ne fa mara ƙarfi ya ƙarawa mai ƙarfi ƙarfi duk da kuwa uban basussuka da gwamnatin tarayya ke jidowa kamar mai shirin sayar da ƙasar nan.

Tambayoyin su ne:

Wani yunƙuri Hukumar Daƙile Yaɗuwar Cututtuka (NCDC) ke yi wajen gamsar da al’umma da bayanai na gani ya kori ji ga kan wannan cuta domin har yanzu jama’ar garuruwan Nijeriya ba su amince da alƙaluman da suke wallafawa ba a shafukansu na sada-zumunta?

Wane Yunƙuri gwamnatin Tarayya mai iƙirarin yaƙi da cin hanci ke yi da gwamnatocin jihohi da kuma Hukumar Rundunar Ƴan sanda wajen magance karɓar na goro da jami’an tsaro ke yi a hanyoyi daban-daban? Shin ba sa karɓar wadataccen albashi ne ko kuma dai tsabar kunnen ƙashin ne na saɓawa ƙa’idojin hukumomin tsaron?

Dama biyan tara Idan matafiya suka karya doka har aka gurfanar da su a gaban kotun tafi da gidanka wani lasisi ne na cigaba da tafiya zuwa inda za su ko kuma dai so ake su juya da baya su koma inda suka fito? Ya kamata irin waɗannan kotunan su yi wa al’umma bayani in har da gaske ne gwamnoni na ƙoƙarin magance matsalar wannan annoba kamar yadda gwamna Nasir El-Rufa’i ke iƙirari.

Shin yaya kuwa kuke kallon gudunmawar dokar zaman gida dole wajen magance matsalar yaɗuwar wannan annoba ta Kwaronabairus?

Ya batun gaskiyar cewa Hukumar EFCC za ta fara binciken ministar Hukumar ba da Tallafi mai raba tallafin rage raɗaɗi kan zaman gida dole a sakamakon wannan annoba? Ya batun ciyar da yara ƴan makaranta abinci kamar yadda ta alƙarwanta? An fara ko kuwa da sauran rina a kaba, don ni dai ban ga yaran unguwanninmu na ci irin waccen ta-tsotse ba?

Daga, Anas Ɗansalma. Jihar Kanon Nijeriya.

Tags: AbujaHausaLabaraiNajeeiyaNewNewsPREMIUM TIMESSuleija
Previous Post

Tsohon Shugaban NNPC, Maikanti Baru ya rasu

Next Post

Yadda Coronavirus ta hana IPOB bukukuwan tuna cikar Yankin Biafra shekaru 50

Next Post
IPOB women

Yadda Coronavirus ta hana IPOB bukukuwan tuna cikar Yankin Biafra shekaru 50

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • FARMAKIN JIRGIN ƘASA: ‘Yan ta’adda sun saki ɗaya mai cikin saboda tausayin laulayin da ta ke yi
  • APC TA YI RASHI: Dalilin ficewa ta daga APC na koma jam’iyyar mai alamar kayan marmari -Abdulmumin Jibrin
  • RUBUBIN TAKARAR SHUGABAN ƘASA A 2023: Yadda Buhari ke gwara kawunan ‘yan takarar APC
  • KALAMAN ƁATANCI GA ANNABI:Ƴan siyasan mu sun yi shiru tsit, kowa na tsoron ya fito ya fadi gaskiya – Tilde
  • Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.