A ranar Talata gwamnatin Kasar Italiya ta sanar cewa mutane 168 sun rasu cikin awa 24 a kasar.
Mahukunta sun ce mutane 631 sun rasu tun barkewar cutar sannan sama da mutane 10,000 sun kamu da cutar.
Wannan matsala ya razana gwamnatin kasar da mutanen kasar inda an dakatar da ayyuka da dama har da makaranta.
Wannan shine mafi yawan rayuka da aka rasa bayan kasar Chana da cutar ta samu asali daga.
Kashen Afrika da cutar ta bayyana sun hada da DR Congo, Algeriya, Burkina Faso, South Africa, Senegal, Tunisia, Togo, Egypt, Cameroon, Najeriya, da Morocco.
A kasar Iran ma, an sanar da Hana fitowa salloli da sallar Juma’a da duk wasu tarorruka da zai Tara jama’a.
Kasar Italiya ce ta uku da cutar ta fi yaduwa.
Baya ga kasar Chana da Koriya Ta Kudu da sune ke kan gaba sai kasar Italiya.
Hatta wasan kwallon kafa an dage su, wadanda za a buga su kuma, za a buga ne babu yan kallo.
Akalla Sama da mutum 197 suka rasu a kasar Italiya zuwa yanzu. Haka itama kasar Faransa cutar ya ci gaba da yaduwa da ya kai ga an dage wasan kwallon kafa daya da ya kamata a buga shi yau.
Hukumar Kula da Lafiya da ke karkashin Majalisar Dinkin Duniya, ta bada sanarwar cewa masana daban-daban na duniya, sun fantsama kirkiro sinadaran magance cutar Conronavirus.
WHO ta ce har ma wasu masu aikin kirkirar magungunan sun kai ga matakan yin gwaje-gwajen gane tabbaci da kuma ingancin kwayoyin maganin.
Da ya ke har yau babu takamaimen maganin cutar, ya zuwa Asabar ta yadu a kasashe har 49, kuma sama da mutum 2,000 ne cutar ta kashe daga Disamba zuwa karshen watan Maris.
Kasashen Denmark, Estonia, Lithuania, Netherlands da Najeriya duk sun bayyana an kamu da cutar daga kasar Italy a cikin kasashen su.
Ita ma Iran kamar yadda jami’in WHO mai suna Ghebreyesus ya bayyana, mutum 92 daga cikin daruruwan da suka kamu, duk daga waje aka shigar musu da ita.
Tun bayan bullar cutar ce Hukumar Lafiya ta Majalisar Dunkin Duniya (WHO) ta hada kai da Chana, su na hakilon nazarin ainihin yadda cutar ke shiga dan Adam, daga inda can ne asalin ta da kuma irin yadda ta ke mamayewar jiki da kuma irin illar da take yi.
Tun bayan barkewar cutar ne WHO ke ta kokarin wayar da kan kasashen da ta bulla da inda ba ta bulla ba, wajen sanar da su hanyoyin bi domin kauce wa wannan cuta da ta zama ruwan-dare cikin watanni uku.
WHO ta ce ta na wannan kokarin ne kafin jiran magungunan da masana suka dukufa binciken samarwa da kirkirowa.