Cutar Coronavirus na cigaba da yaduwa a kasashen gabas ta tsakiya musamman kasashen Kuwait, Qatar, Saudiyya da Egypt.
Ma’aikatar Kiwon Lafiya ta Kasar Saudiyya ta bayyana cewa bayan karin mutum biyar da aka samu sun kamu da cutar a kasar, yanzu an tabbatar da mutane 20 kenan da ke dauke da ita a kasar.
Cikin mutane biyar din da aka gano yau, hudu yan kasa ne. Uku daga cikin su sun dawo daga kasar Iran da Iraqi ne daya daga kasar Masar.
Saudiyya ta dakatar da fita da shigowan jirage daga kasashe 14 da suka hada da
United Arab Emirates (UAE), Egypt, Kuwait, Bahrain, Iraq, Lebanon, Syria, South Korea, Italy, Oman, France, Germany, Turkey da Spain.
Bayan haka kuma ta sanar da rufe makarantun kasar daga ranar litini.
Sannan kuma za a rika rufe masallatan Makka da na Madina bayan sallar Ishha’i, kuma gwamnati ta dakatar yin Umrah.
KUWAIT
Kasar Kiwait ta sanar da sabbin wasu mutum hudu da suka kama da ya kara ywan adadin mutanen da ke dauke da cutar a kasar zuwa 69.
QATAR
Akalla mutane 18 ne aka tabbatar sun kamu da cutar a kasar Qatar.
EGYPT
Kasar Masar wacce ita kasa ta farko a Nahiyar Afrika da aka bayyana shigar cutar, zuwa yanzu akalla mutane 59 ne ke dauke da cutar.
Firaye Ministan Kasar Mostafa Madbouli ya bayyana cewa an saka dokar hana taro da gangami a fadin kasar zuwa yanzu don kada a yada cutar.