• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Kano State Assembly

    Dan majalisar dokoki na jihar Kano ya doka ‘Ribas’ bayan ya tsunduma lambun jam’iyyar NNPP, ya ya rungumi tsintsiyar sa ya dawo APC

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Dalilin da ya sa Buhari ya dakatar da Akanta Janar ɗin da ake zargi da kantara satar naira biliyan 80

    Nigerian Pilgrims

    HAJJIN BANA: Duk wanda ya zarce shekaru 65 bashi ba Hajji bana – Hukumar Alhazai

    Beggars

    Almajirai da mabarata sun kwararo Abuja – Mahukunta

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Kano State Assembly

    Dan majalisar dokoki na jihar Kano ya doka ‘Ribas’ bayan ya tsunduma lambun jam’iyyar NNPP, ya ya rungumi tsintsiyar sa ya dawo APC

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Dalilin da ya sa Buhari ya dakatar da Akanta Janar ɗin da ake zargi da kantara satar naira biliyan 80

    Nigerian Pilgrims

    HAJJIN BANA: Duk wanda ya zarce shekaru 65 bashi ba Hajji bana – Hukumar Alhazai

    Beggars

    Almajirai da mabarata sun kwararo Abuja – Mahukunta

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Mai Martaba Sarkin Kano, Malam Muhammadu Sanusi II Allah Ne Madogarar Sa, Daga Imam Murtadha Muhammad

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
January 17, 2020
in Ra'ayi
0
Mai Martaba Sarkin Kano, Malam Muhammadu Sanusi II Allah Ne Madogarar Sa, Daga Imam Murtadha Muhammad

Da sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jin Kai

Dukkan godiya da kyakkyawan yabo sun tabbata ga Allah. Tsira da amincin Allah su kara tabbata ga Annabi Muhammad (SAW), da Iyalan sa da Sahabban sa baki daya.

Allah Mai girma! Tsarki ya tabbata ga Allah, mai kowa mai komai. Mai kashe wa, mai raya wa. Mai daukaka wa kuma kaskanta wanda yaso. Mai bayar da mulki, kuma ya kwace mulki daga wanda yaso.

Ya ku jama’a, don Allah ku kalli yadda wasu mutane suke kokarin hada kawunan su da Allah! Sai kace sune masu bayar da mulki da karbe wa ba Allah ba! Ya Allah ka nuna masu kai baka da tamka ko mataimaki, kuma ka nuna masu kai ba azzalumi bane, kuma baka bari ayi zalunci, amin.

Murtadha Gusau
Murtadha Gusau

Jiya Alhamis ne, ranar 16/01/2020, mataimaki na musamman (wato SA) ga gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ta bangaren yada labarai, mai suna Salihu Tanko Yakasai, ya shiga kafafen yada labaran Jihar Kano yayi wasu maganganu na awa daya, aka yada su, kowa yaji shi. Yaci mutuncin Mai Martaba Sarki, yaci mutuncin masarautar Kano mai dimbin tarihi, mai daraja, mai albarka. Ya fadi iya maganganun da yake so na batanci, don ya farantawa mai gidan sa rai.

Cikin maganganun sa yake cewa, wai sun dauki alkawari, kuma sun sha alwashin cewa in dai har sunyi nasara a hukuncin kotun koli da za’a yanke jibi ranar litinin, to ba zasu taba kyale Mai Martaba Sarki akan karagar sarautar Kano ba, sai sun sauke shi! Ga maganar da yayi a takaice:

“Mu a matsayin mu na gwamnati, ba zamu taba yafe wa wannan mutum ba, ba zamu taba hakura ba. Domin shine ya jawo muna dukkan bakin jinin da muka samu kan mu a ciki. A cikin Jihar Kano da wajen Jihar, mutane basa girmama gwamnan mu, basa ganin girman sa, saboda wannan akun Sarkin surutu! Zamu kawo karshen sarautar tasa, in yaso mu ga yaya zai yi shi da magoya bayan nasa! Wannan Sarkin cikin birnin yana ganin cewa yana da goyon bayan jama’ah a duniya, to mu kuma zamu nuna masa muna da karfi da zarar mun ci nasara a kotu!”

Wannan fa ya ku ‘yan uwa masu girma, kadan ke nan daga cikin maganganun da wannan mutum yayi na cin mutunci da batanci ga Mai Martaba Sarki, da kafatanin masarautar Kano, da Kanawa baki daya.

Tun da aka fara rikicin nan, mutanen nan basu da aiki koda yaushe illa cin mutuncin wannan bawan Allah mai daraja.

Su zage shi, suyi masa sharri, suyi masa kazafi, su ce yayi abu alhali bai yi ba, suce yace alhali bai ce ba, idan ya fadi magana su canza ko su juya ta, ko kuma suyi mata mummunar fassara, duk don kawai su bata masa suna, amma saboda Allah Subhanahu wa Ta’ala yayi shi mai hakuri, babu abunda yake ce masu.

Sannan har kullun su ganin suke yi, bakin jinin da suke da shi Mai Martaba Sarki ne ya jawo masu shi, alhali kuwa ba haka bane wallahi. In ban da hauka da rashin hankali irin nasu, ya za’a yi ba zaku yi bakin jini ba? Kun taba tushen addinin mutane da al’adunsu masu kyawo da tarihin su na wurin shekaru dubu, kuna neman ku tarwatsa su, kuyi masu tonon silili, ku raba kan al’ummah, bayan kun tarar da su kawunan su a hade, sannan kuce ba zaku yi bakin jini ba? An gaya maku wannan abun da kuka yi, na rusawa da ruguzawa da tarwatsa masarautar Kano mai dimbin tarihi, karamin laifi ne? Sannan manyan mutane daban-daban, dattijai, shehunnai, malaman addini, sarakuna, ‘yan siyasa, maza da mata masu kima da daraja, masana masu ilimi, ‘yan kasuwa, duk sun ja kunnen ku akan wannan aika-aika da kuke son yi na cin mutuncin masu mutunci, sun gaya maku gaskiya, sun baku shawara ta gaskiya akan ku hakura, ku janye wannan kuduri naku, amma kun yi biris, kun yi kunnen uwar shegu da su, to ku fada mani, don Allah ta yaya ba zaku yi bakin jini ba? Ai wallahi bakin jini kadan ma kenan. Sai kun kasance ma baku kan mulki, a lokacin ne zaku san meye ake kira bakin jini!

Mai Martaba Sarki sam wallahi bai dogara da komai ba in ba Allah ba. Ya san da cewa Allah ne ke yin komai. Mai Martaba Sarki mutum ne da a gaban sa ba boka, ba Dan bori, kuma ba tsafi. Allah ne gatan sa, kuma shine mai yi masa komai. Kuma duk wannan farin jini, da daukaka, da daraja da kuke gani a wurin sa, Allah Subhanahu wa Ta’ala ne ya bashi shi, saboda Allah ya hangi zuciyar sa yaga bata dauke da komai na sharri sai alkhairi ga kowa da kowa. Don haka Allah ya mallaka masa jama’ah a ciki da wajen Jihar Kano. Kuma da ikon Allah, wannan daukaka ta Mai Martaba Sarki, sai dai abunda yayi gaba da izinin Allah.

An zo an gaya wa Annabi Muhammad (SAW) cewa, ga makiya can sun taru a kan ku, sun sha alwashin ganin bayan ku, sai Annabi (SAW) yace, HASBUNALLAHU WA NI’MAL WAKIL. Haka Annabin Allah Ibrahim (AS), makiyan sa sun jefa shi cikin wuta da ransa, da nufin su halaka shi su huta da shi, sai shima ya karanta, HASBUNALLAHU WA NI’MAL WAKIL. Haka muma masoyan mai Martaba Sarki bamu da abunda ya wuce Allah. Don haka mu shine madogarar mu, kuma wallahi ya ishe mu.

Duk wanda yake kuma ganin shi yafi karfin Allah, ko kuma yake ganin kamar shine Allah, ko kuma yake ganin zai iya dora wanda yake so kan mulki, kuma ya sauke wanda yake so, mu ba abun da zamu ce da shi illa, GA SHI GA ALLAH DIN. Zamu gani, da shi da Allah wane ne yafi karfin wani!!!

Kuma mu har kullun, muna kira ga irin wadannan ‘yan siyasar, cewa su gyara dabi’un da halayen su, kuma suyi kokari su gyara mu’amalar su da jama’ah, da kuma mu’amalar su da talakawansu. Domin duk wannan bakin jinin da suke ganin suna da shi, wallahi sune suka jawo wa kan su shi. Idan kuma sun gyara, to sai Allah yasa mutane su kaunace su.

Daga karshe, ina mai mika dimbin godiya ta ga dukkanin Kanawa, da dukkanin ‘yan arewa, da dukkanin ‘yan Najeriya, saboda irin so da kauna da kuke nunawa mai Martaba Sarkin Kano, Malam Muhammadu Sanusi II. Babu abunda zamu ce da ku illa Addu’ar Allah yasa ku gama lafiya, ku da iyalan ku duka. Kuma Allah ya biya maku bukatun ku duniya da lahira. Allah ya kare ku daga dukkan sharri da fitina, amin.

Kuma don Allah muna rokon ku, da kuci gaba da nuna soyayyar ku da kaunar ku ga mai Martaba Sarkin Kano, Malam Muhammadu Sanusi II. Allah ne kadai zai biya ku, kuma yayi maku sakayya duniya da lahira In Shaa Allah.

Shi kuma mai Martaba Sarki, ina rokon Allah Subhanahu wa Ta’ala da yaci gaba da kare muna kujerar sa, mutuncin sa, da Martabar sa, da imanin sa, amin.

Wassalamu Alaikum,

Dan uwan ku, Imam Murtadha Muhammad Gusau ne ya rubuto daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa a wannan lambar waya kamar haka: 08038289761.

Tags: Abdulahi GandujeGusauKanoMutadhaNajeriyaPREMIUM TIMESSanusiSarki
Previous Post

Da so samu ne in kasance cikin makusantan Buhari na kud-da-kud ‘Cabal’ – Shettima

Next Post

BOKO HARAM: Najeriya ta siyo jiragen sama masu aman wuta

Next Post
Airforce Chief

BOKO HARAM: Najeriya ta siyo jiragen sama masu aman wuta

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Dan majalisar dokoki na jihar Kano ya doka ‘Ribas’ bayan ya tsunduma lambun jam’iyyar NNPP, ya ya rungumi tsintsiyar sa ya dawo APC
  • Walikan Filato na Amaechi ne, babu haufi, babu tantama babu kila wa kala – In ji Lalong
  • MATSALAR TSARO: Nan da wata biyu za a ƙara ɗaukar kuratan ‘yan sanda 10,000 -Dingyaɗi
  • Duk da an ƙara wa Magu girma, za a hukunta shi idan bincike ya tabbatar da laifi a kan sa -Dingyaɗi
  • FASHEWAR TUKUNYAR GAS A KANO: Ministar Jinƙai na so a ɗau matakan hana aukuwar bala’o’i

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.