Mahara sanye da kayan sojoji sun yi garkuwa da Hakimin Birnin Gwari, Yahaya Abubakar, a hanyar a hanyar sa ta zuwa Birnin Gwari.
Haka kuma masu garkuwan sun arce da tsohon sakataren ilimi na karamar hukumar Ibrahim Musa, da ke tare da Hakimin a motar da aka yi garkuwa da su.
Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta tabbatar da aukuwar wannan mummunar Al’amari, inda ta sanr cewa an yi garkuwa da hakimin ne a kauyen unguwar Yako bayan wadannan mutane sun taida su.
Bayan haka Kakakin rundunar ya kara da cewa an yi garkuwa da wasu mutane uku a unguwan Sabon tasha dake Kaduna.
Wadanda aka yi garkuwar dasu sune, Jonathan Obi, Joakin Obi da Benjamin Obi. Ya ce dukkan su suna zama ne a unguwa daya.
” Bayan an sanar da rundunar yin garkuwa da wadannan mutane, jami’an mu sun fantsama cikin dazukan da ke zagaye da unguwar domin kamo wadanda suka aikata wadannan mahara.
Discussion about this post