• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

RANAR ‘YANCI: Muhimman Abubuwa 11 dake kunshe a jawabin Buhari

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
October 2, 2019
in Babban Labari, Rahotanni
0
Muhammadu Buhari

Muhammadu Buhari

A ranar Talata ne Shugaba Muhammadu Buhari ya yi dogon jawabi, domin tuna Ranar Samun ‘Yancin Najeriya, shekaru 59 da suka gabata.

Sai dai kuma tun ba a je ko’ina ba, da dama na ganin cewa kamata ya yi Buhari ya yi magana a kan halin da yankin Arewa maso Yamma, wato shiyyar sa ke ciki dangane da yawaitar ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane. Buhari bai yi wannan magana ba.

Akwai Zamfarawa da Sakkwatawa da Katsinawa sama da 40,000 da yanzu haka ‘yan bindiga suka tilasta yin gudun hijira cikin Jamhuriyar Nijar. Banda kuma dubban wadanda Boko Haram suka kora zuwa Nijar daga Barno da Yobe. Duk wadannan Buhari bai ce komai a kan su ba.

Idan aka koma a cikin jawabin sa, za a iya fahimtar yadda Buhari ya rika bayani ya na ci gaba da dora wasu laifuka a kan gwamnatocin da suka gabata.

1 – DALA BILYAN 42.5 KIMSHE A ASUSUN NAJERIYA:

Buhari ya yi bayanin cewa a yanzu a zamanin sa akwai har Dala Bilyan 42.5 a Asusun Najeriya da ke kasashen Turai.

Sai dai kuma Buhari bai yi wa ‘yan Najeriya bayanin tulin bashin da gwamnatin sa ta ciwo ba. Bashin da ya ciwo cikin shekaru hudu ya nunka wanda ya taras ana bin Najeriya gaba daya.

Buhari ya gaji bashin da bai kai Dala Bilyan 30 na. Amma ya zuwa watan Yuli, 2019, ana bin Najeriya bashin Dala Bilyan 81.27, kwatankwacin naira Tirilyan 24.95.

Daga 2018 zuwa 2018 an ciwo kusan naira Tirilyan 2.66. Dukkan wadannan bayanai Dirakatar Ofishin Kula Da Bilyan Basusssuka, Patience Oniha ce ta yi su.

2 – LAIFIN GWAMNATOCIN BAYA

Shugaba Buhari ya dora wa gwamnatocin baya da suka gabata cewa ba su maida hankali a kan wasu fannonin samun kudin shiga ba, baya ga man fetur.

Sai dai kuma wani abin dubawa shi ne, kokarin da tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya yi, a farkon hawan sa, inda ya yi amfani da kyakkyawar diflomasiyya aka yafe wa Najeriya basussukan da ake bin ta. Wadannan bashi kuwa ba Obasanjo din ne ya ciwo su ba, gadon su ya yi daga gwamnatocin baya.

3 – KURAKURAN GWAMNATOCIN BAYA A KAN FETUR

Buhari ya yi bayanin cewa a yanzu gwamnatin sa ta dauki darasi daga kurakuran da gwamnatocin baya suka yi a fannin fetur. Shi ya sa a yanzu gwamnatin ta sa ke ririta abin da ake samu daga fetur.

To sai dai kuma babban kuskuren gwamnatocin baya bai wuce biyan kudin tallafin fetur ba, wato ‘subsidy’. Ita ma gwamnatin Buhari a yanzu ta na biya, kuma ‘yan Najeriya sun fi shan fetur da tsada a gwamnatin sa.

4 – ‘YANCIN FADAR ALBARKACIN BAKI

Buhari ya yi bayanin cewa gwamnatin sa ta bada damar fadar albarkacin baki. Wannan magana kuwa jama’a da dama za su yi watsi da ita, idan aka yi la’akari da yawa-yawan mutanen da ake kamawa a tarayya da jihohi idan furta albarkacin bakin su. Yadda tarayya ta yi kaurin suna, haka jihohi da dama suka yi kaurin suna, musamman su a kan masu sukar gwamnatocin su a soshiyal midiya.

5 – YAKI DA CIN HANCI DA RASHAWA

Buhari ya yi bayanin irin hobbasar da gwamnatin sa ta yi a kan yaki da cin hanci da rashawa. Sai dai kuma wadansu matakai da dama wadanda gwamnatin sa ta rika dauka, sun san tuni jama’a da dama sun rika yi wa yaki da cin hanci da rashawa kallon shirin tatsuniya.

Irin yadda Buhari ya cika gwamnatin sa da rikakkun ‘yan PDP, jam’iyyar da ya rika cewa ta kashe kasa, ya haifar da mamaki sosai a kasar nan. Da yawan su kuma da sauran kashi a gindin su, wanda kotu ba ta gama yi musu wankan tsarki ba.

Yadda kotu ta yi gaggawar wanke Sanata Danjuma Goje, cikin kankanin lokaci, bayan daukar shekaru kusan goma ana shari’a, shi ma jama’a na yi masa kallon ‘shari’a-sabanin-hankali.’

6 – KOKARIN MAIDO WA NAJERIYA DALA MILYAN 300 DAGA KUDIN ABACHA

Cikin bayanin Buhari, ya ce Najeriya da Amurka na tattauna yadda za a maido wa kasar nan da Dala Milyan 300, wadanda Abacha ya sata, ya kimshe. Sai dai kuma a fili ta ke cewa Buhari ba sau daya ba, bayan ya hau mulki ya rika cewa Abacha ba barawo ba ne, bai saci kudin Najeriya ba. Duk kuwa da cewa an maido wa Najeriya makudan kudaden da aka ce Abacha din ne ya sace su.

7 – BUKATAR KARA WA DABEN FANNIN SHARA’A SIMINTI

Buhari ya yi bayani akan fannin shari’a. Amma tuni jama’a da dama musamman masu rajin kare hakkin jama’a da ‘yancin Dimokradiyya na ganin cewa labari ne kawai, idan aka yi la’akari da yadda gwamnatin sa ke take umarnin kotu. Ko kotu ta ce a saki wanda ke tsare, sai gwamnatin Buhari ta yi biris.

Cikin wadanda wannan biris ta yi wa burki, akwai Ibrahim El-Zakzaky, matar sa Zeenat, Sambo Dasuki da kuma na baya-bayan nan, Omoyele Sowore.

8 – BATUN DAKILE BOKO HARAM

Yayin da Shugaba Buhari ke jawabin cewa an dakile Boko Haram, wani dan Majalisar Tarayya daga Jihar Barno ya ce har yanzu Boko Haram na wandaka da warisa a kananan hukumomi takwas na Jihar Barno.

Sannan kuma kwana daya kafin jawabin Buhari, Hukumar Tsarin Sojojin Kasar nan, sun fitar da sanarwar yin gagarimar addu’o’i daga mabiya addinai, domin yi wa matsalar Boko Haram taron-dangi.

9 – CI GABA A FANNIN NOMA

Jawabin Buhari ya nuna irin ci gaban da aka samu a fannin noma a shekaru hudu da rabi da ya yi a kan mulki. To sai dai kuma ba jama’ar kasa ba kadai, ita gwamnatin na sane da cewa har yanzu ana fama da kuncin talauci da yunwa.

Har yau a kullum matasa ‘yan Arewa sai kwarara suke kudanci da tsakiyar Najeriya su na ayyukan kananan sana’o’in ci da kai da kyar. Dako, wankin takalmi, yankan farce, jari-bola duk matasan Arewa ne, kuma a kullum sai kwarara su ke yi.

10 – TUTIYA DA BUNKASA HANYOYIN SAMUN KUDIN SHIGA

Cikin jawabin Buhari, ya yi tutiya kan yadda gwamnatin sa ta fadada hanyoyin samun kudaden shiga, wato harajin cikin gida, yadda za a rika rage dogaro da fetur kawai.

To wannan ma jama’a na ganin cewa ba a yi kokari fiye da gwamnatin baya ba, idan aka yi la’akari da wata wasikar da aka yi zargin Ofishin Shugaban Ma’aikatan Gidan Gamnatin Tarayya, Abba Kyari ya aika wa Shugaban Hukumar Tara Kudaden Harajin Cikin Gida (FIRS), Babatunde Fowler.

Wasikar ta nuna damuwa kan yadda kudaden shigar da ake tarawa ba su ma kai na wasu shekaru a lokacin mulkin Jonathan ba.

11 – SAMAR WA MATASA SAHIHIYAR MADOGARA

Buhari ya ce gwamnatin sa ta Gina matasa ta hanyar samar musu hanyoyin dogaro da kai daga abin bukatun su wajibi. Tuni masu adawa na ganin ai har yau Buhari bai yi irin kokarin da Jonathan ya yi ba, wanda ya gina wa matasa jami’o’in gwamnatin tarayya har guda 14.

BAYAN SHEKARU 59: Jiya Najeriya ta cika shekaru 59 da samun ‘yanci. Sai dai kuma sama da shekaru 15 kenan ba ta da kamfanin zirga-zirgar jiragen sama na ta.

Wadanda suka durkusar da Nagerian Airways na nan ba a hukunta su ba. Duk kuwa da cewa gwamnatin Buhari ta biya tsoffin ma’aikatan kamfanin kudaden albashi da fanshon su na baya da su ke bi.

Sauran shekara daya mu cika shekara 60 da samun ‘yanci. Me za a yi cikin wannan shekara daya, wanda a cikin shekaru 59 ba a yi ba?

Mu na ji, mu na gani, mu na kuma saurare.

Tags: AbujaBuhariHausaLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

KURUNKUS: Buhari ba zai yi takara a 2023

Next Post

NDLEA ta kama masu safarar miyagun kwayoyi 15 a jihar Gombe

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
NDLEA

NDLEA ta kama masu safarar miyagun kwayoyi 15 a jihar Gombe

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN KASA: Atiku ya kai wa kotu tulin hujjoji daga na’urar BVAS a zaɓen 2023
  • Dikko Radda zai saka tsarin TSA a duka harkokin shige da ficen kudaden jihar Katsina
  • Dalilin da ya sa na canja sunan titin Raba zuwa titin ‘Nasir El-Rufai – Gwamna Uba Sani
  • KOKAWAR ƘWACE KUJERAR TINUBU: Kotu ta karɓi kwafen takardun zargin Asiwaju ya yi harƙallar muggan ƙwayoyi
  • SIYASAR KANO: Gwamna Abba ya soke naɗe-naɗe, ya ƙwace filaye da kadarorin da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.