• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Jawo Hankalin Shugaban Kasa Da Jami’an Tsaron Najeriya: Gwamnan Kano Yana Neman Cinnawa Jihar Wuta! Daga Imam Murtadha Muhammad

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
September 22, 2019
in Ra'ayi
0
Buhari and Ganduje Aso rock

Buhari and Ganduje Aso rock

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jin Kai

Assalamu Alaikum

Ya Mai girma Shugaban Kasar Najeriya, Alhaji Muhammadu Buhari, ina fatan wannan sako na wa zai same ka cikin koshin lafiya da amincin Allah? Allah yasa, amin.

Ya mai girma Shugaban Kasa da jami’an tsaron Najeriya, bayan gaisuwa da girmamawa, wannan sako ne zuwa ga reku, domin sanar da ku abin da yake faruwa a Jihar Kano, domin ka da wani abu na rashin tsaro ya faru kuce ba’a sanar da ku ba, ko kuma kuce ba ku da labari. Allah ya kiyaye, ya zaunar da mu lafiya, amin.

Ya mai girma Shugaban Kasa, labari ya iso muna ta majiya mai karfi kuma mai tushe, cewa Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya gama shiri tsaf domin tsige Sarki mai daraja, Mai Martaba Sarkin Kano, Malam Muhammadu Sanusi II. Labari ya iso muna cewa, Gwamna za ya umurci Mai Martaba Sarki da ya koma garin Bichi, ko ya bar Sarautar gaba daya. Idan kuma ya ki zai cire shi daga Sarautar.

Ya mai girma Shugaban Kasa, Allah shine shaida, Allah ya kiyaye, wallahi ina mai ji muna tsoron tashin gobara a Jihar Kano, muna jin tsoron tashin wutar da za ta zama sanadiyyar rasa rayuka da dukiyoyi masu dimbin yawa na bayin Allah, talakawa. Wadanda a matsayin su na ‘yan Najeriya, kayi alkawari, kuma kayi rantsuwar kare rayukan su da dukiyoyin su.

Ya mai girma Shugaban Kasa, ina jin tsoron jawo abun da zai zama sanadiyyar ruguza kadarori marasa iyaka, na bayin Allah, talakawan ka.

Ya mai girma Shugaban Kasa, ina tsoron jawo barnar da, ba za ta tsaya a Jihar Kano kawai ba, a’a, barnar da za ta mamaye Arewacin Najeriya da kasar nan baki daya.

Ya mai girma Shugaban Kasa, ina jin tsoron tayar da wutar da za ta yi sanadiyyar ruguza wannan dimokradiyyar da muke tinkaho da ita.

Ya mai girma Shugaban Kasa, mutanen Jihar Kano cike suke da fushin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, saboda ire-iren halayen sa da dabi’un sa na musgunawa jama’ah; halayen sa da irin salon mulkin sa na jefa kanawa cikin talauci, rashin aikin yi, tare da hali na rashin mutunci da yake nuna masu kullum. Ya mayar da Jihar kamar ba Jihar Kano da aka sani ba!

Ya mai girma Shugaban Kasa, Mawakan Gwamna Ganduje za su yi waka, su zagi Mai Martaba Sarkin Kano, Malam Muhammadu Sanusi II, su ci mutuncin sa, su yi batanci zuwa ga re shi, su fadi abunda suke so akan sa, Gwamna yayi masu kyauta ta alfarma, yayi masu alkhairi shi da ‘yan bangar siyasar sa. Amma da zaran mawakan Mai Martaba Sarki sun yi waka, ba domin su zagi kowa ko su ci mutuncin kowa ba, a’a, sai don su kare Martabar Sarki, nan ta ke sai Gwamna yasa a kama su, aci masu mutunci, a kai su gidan yari a daure. Har yau mun kasa fahimtar wannan wane irin hukunci ne! A yanzu haka, Allah ne kadai yasan iyakar ‘ya ‘yan talakawan da Gwamna Ganduje yasa aka tsare.

Duk da wannan, mutanen Jihar Kano sun danne fushin su, suna zaune lafiya, suna ta addu’ar Allah ya kare su da kuma Arewacin Najeriya da kasar nan baki daya daga afkawa cikin irin abubuwan da suke faruwa na ta’addanci da rashin tsaro a wasu wurare. Allah ya kiyaye, amin.

Ya mai girma Shugaban Kasa, dukkanin mu mun yi imani da Allah cewa, ana yin mulki ne domin hada kan al’ummah da ciyar da su gaba. Mun san ana yin siyasa ne domin kawo wa jama’ah alkhairi da amfani. Mun san ana yin Shugabanci ne domin kare dukkan sharri da zai afkawa al’ummah. Amma a Jihar Kano gaskiya ba haka abun yake ba. Domin siyasar Jihar Kano a halin yanzu ta rarraba kan al’ummah, ta tarwatsa su, sannan kuma tana neman jefa Jihar cikin babbar damuwa idan ba’a dauki kwakkwaran mataki ba. Allah ya kiyaye, amin.

Ya mai girma Shugaban Kasa, muna masu sanar da kai cewa, tura fa tana neman kai wa ga bango! Domin Gwamna Ganduje a halin yanzu ba shi da tunani illa ya jawo rigima, ko ya jefa Jihar Kano cikin tashin hankalin da Allah ne kadai yasan karshen sa.

Ya mai girma Shugaban Kasa, muna rokon da ka ja wa Gwamna Ganduje kunne, ka sa masa linzami, kafin ya jawo muna masifar da ba mu san a inda zata tsaya ba! Allah ya tsare kuma ya sawwake, amin.

Haka nan ma muna roko ga hukommin tsaron kasar nan, da su sa kaimi, su tabbata sun gargadi Gwamna Ganduje. Kuma su nuna masa cewa, yayi hankali kar ya jefa Jihar Kano cikin masifa. Allah ya kiyaye, amin.

Mun san duk dai duniya tana kallo, kuma tana ji, kuma tana sane da cin mutunci da tsokana da wulakanci kala-kala, iri-iri, daban-daban da Gwamna Ganduje yake nunawa Mai Martaba Sarkin Kano, Malam Muhammadu Sanusi II.

Kwanan nan, don rainin hankali, Gwamna Ganduje yasa aka jera hotunan wasu hakimai guda hudu tare da hoton Mai Martaba Sarkin Kano, Malam Muhammadu Sanusi II, a dakin taro na Coronation Hall da ke gidan gwamnatin Jihar Kano, ba don komai ba sai don tsokana da neman tayar da hankalin Kanawa da aka sani da hakuri da son zama lafiya. A da hoton Mai Martaba Sarki ne kawai a wurin, amma yanzu sai aka jera hotunan wadannan hakimai da na Sarki, kuma aka mayar da hoton Mai Martaba Sarki a karshe da nufin cin mutuncin Sarki! Sun manta da cewa, duk wanda Allah ya rufa wa asiri, kuma yayi masa sutura, to fa babu mai iya yi masa komai!

Duk wasu mutane masu mutunci da daraja, tun daga Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar III, har zuwa manyan Sarakunan mu na Arewa, har zuwa babban Dan kasuwar Afirika, mai daraja Alhaji Aliko Dangote da Mai girma Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufa’i da mai girma Gwamnan Ekiti, Kayode Fayemi, sun sa baki a cikin wannan magana, amma Gwamna Ganduje yayi biris, yayi kunnen uwar shegu da duk maganganun su, yaci gaba da bita-da-kullin da ya saba yiwa Mai Martaba Sarki. Sai kace ba Musulmi ba, sai kace ba Dan Arewa ba, sai kace ba Dan Kano ba!

Duk duniya ta shaida, Mai Martaba Sarkin Kano yayi hakuri iya hakuri, amma wannan Gwamna, sam, har yanzu bai dai na cin mutuncin masarautar Kano ba mai dimbin tarihi, wadda tana daya daga cikin masarautun da Shehu Usman Dan Fodiyo yayi jihadi domin kafawa.

Ya mai girma Shugaban Kasa, kwanan nan aka yada wasu rade-radi, cewa fadar Shugaban Kasa ta samu matsala ta rashin jituwa tsakanin ta da mataimakin Shugaban Kasa, wato Farfesa Yemi Osinbajo, amma nan ta ke, wallahi, sai dukkan Sarakunan kasar yarbawa suka fara shirye-shirye, tare da kokarin daukar mataki domin su kare Dan uwan su. ‘Yan siyasar kudu har kullun, suna kallon Sarakunan su da mutunci, suna girmama su, suna ganin darajar su. Amma shin me yasa wasu ‘yan siyasar mu na Arewa ba su girmama Sarakunan mu ne, kuma ba su san darajar su ba?

Ya mai girma Shugaban Kasa, muna rokon da ka sa baki cikin wannan badakala, ka ja kunnen Gwamna Ganduje. Ya kamata ya mayar da hankalin sa wurin ci gaban Jihar Kano da Kanawa baki daya, ba kawai yayi ta kashe dukiyar Jihar Kano wurin fada da Mai Martaba Sarki ba!

Ya mai girma Shugaban Kasa, wallahi, ka sani, Kanawa basu jin dadin wannan abun da Gwamna Ganduje yake yiwa Mai Martaba Sarki. Sun yi fushi, sun fusata, sun harzuka matuka! Don haka don Allah muna rokon da ka sa baki domin kauce wa fitina da tashin hankalin da ke neman faruwa a Jihar Kano!

Muna rokon Allah ya zaunar da Jihar Kano lafiya da Najeriya baki daya. Allah ya gina muna katangar karfe, kuma ya shiga tsakanin mutanen Jihar Kano, masu son zaman lafiya, masu kaunar Sarkin su, daga mugun tanadin dukkan wani mutum makiyin zaman lafiya, amin.

Wassalamu Alaikum,

Daga Dan uwan ku, Imam Murtadha Muhammad, ya rubuto ne daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa a adireshi kamar haka: gusaumurtada@gmail.com ko kuma: 08038289761.

Tags: AbbaAbdulahi GandujeGandujeGusauKanoMohammedMurtadhaNajeriyaSarki
Previous Post

Kada ka kuskura ka kara mata idan baka da halin rike su- Inji Sarki Attahiru

Next Post

Mahara sun kashe mutane biyu a Adamawa

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
Boko Haram

Mahara sun kashe mutane biyu a Adamawa

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • TATTALIN ARZIKI: Ɗanyen man Najeriya ya fara kwantai a duniya, bayan Chana, Turai da Indiya sun koma sayen na Rasha mai rahusa sosai
  • HAJJI 2023: Hukumar Alhazai ta gindiya sabbin sharuɗɗan adadin kwanakin ziyara Madina
  • HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125
  • KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu
  • DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.