• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

El-Rufa’i Ya Ba Mara da Kunya, Daga Imam Murtadha Gusau

Mohammed LerebyMohammed Lere
September 24, 2019
in Ra'ayi
0
Capital School

Capital School

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jin kai

Assalamu Alaikum

Ya ku ‘yan uwana ‘yan Najeriya masu girma, masu daraja! Wallahi, Allah ya sani, kuma shine shaida, na dade ina kwakkwaran bincike da kuma bibiyar ayukka da tsare-tsare, da salon mulki irin na gwamnatin jihar Kaduna, karkashin jagorancin mai girma adalin gwamna, masoyin talakawa, mai kaunar kawo canji na gaskiya a cikin al’ummah, wato Malam Nasir Ahmad El-Rufa’i; sai daga karshe sakamakon bincike na ya tabbatar mani da cewa, lallai wannan mutum alkhairi yake nufi ga jihar sa ta Kaduna da kuma kasar nan baki daya. Na gano cewa wannan gwamna wallahi, wallahi, wallahi, talaka ne a gaban sa ba aljihun sa ba, kuma na gano, burin sa shine, yaya za’a yi a gyara tsarin kasar nan, ta dawo kamar yadda ake tafiya a can da, ya zamanto babu banbanci tsakanin dan mai kudi da dan talaka; tsakanin ‘ya ‘yan masu mulki da ‘ya ‘yan wadanda ake mulka.

Imam Murtada Gusau
Imam Murtada Gusau

Ya ku bayin Allah! A kasar nan ta mu mai albarka Najeriya, mun dade muna ta kiraye-kiraye zuwa ga gwamnati da dukkanin wani mai ruwa da tsaki a harkar ilimin kasar, cewa, wallahi idan ana so ilimin kasar nan ya gyaru, ya koma mai inganci kamar can da, inda da dan Sarki da dan gwamna da dan attajiri duk ajin su daya, to sai an cire son zuciya, ya zamanto an rusa duk wani tsari na makarantu masu zaman kan su (private schools), ko kuma a rage yawan su, abar masu inganci daga cikin su, sannan ya zamanto duk wani mai hali, da ‘yan siyasa, da manyan jami’an gwmnatoci, da sarakuna duk su kai ‘ya ‘yan su makarantun gwamnati tare da ‘ya ‘yan talakawa, kamar yadda tsarin karatu yake a can da. Wannan hanyar ce kadai idan Allah ya taimake mu, sai tsarin ilimin mu ya gyaru. Amma matukar aka ce makarantun ‘ya ‘yan manya daban, na ‘ya ‘yan talakawa daban, to wallahi har abada harkar ilimin mu ba za ya taba gyaruwa ba, wannan ita ce gaskiyar magana.

Idan zamu tuna a shekarar 2015, lokacin da ake Kamfen din neman kuri’un talakawa, gwamna Malam Nasir Ahmad El-Rufa’i ya dau alkawari, ya bayyana cewa idan Allah yasa yaci nasara, zai sa dan sa a makarantar gwamnati tare da ‘ya ‘yan talakawa.

Tun a wancan lokacin ‘yan adawa da sauran jama’ah suke ta ganin cewa gwamna El-Rufa’i ya fada ne kawai amma sam ba zai iya yin haka ba, saboda lalacewar makarantun gwamnati a kasar nan.

Sai ga shi ranar litinin, 23 ga watan Satumba 2019, a lokacin da aka bude makarantu, bayan hutun karshen zango da aka tafi, mai girma gwamna El-Rufa’i ya ba mara da kunya, ya cika alkawari, ya garzaya da dan sa na cikin sa, Abubakar Al-Sadiq mai shekaru shida (6), zuwa makarantar gwamnati ta Kapital School da ke Kaduna, kamar yadda yayi alkawari a can baya, a inda aka yi masa rajistar shiga aji daya; kuma yayi kira ga sauran jami’an gwamnati da ‘yan siyasa da su yi koyi da shi, su sa ‘ya’yan su a makarantun gwamnati kamar yadda yayi, domin ta nan ne kadai hanyar da ‘yan siyasa da hukumomi za su bi suyi hobbasa domin inganta ilimi.

Sannan kamar yadda kowa ya sani ne, tun bayan hawan gwamna Malam Nasir Ahmad El-Rufa’i kujerar mulkin Kaduna ya fara aiki tukuru wajen ganin cewa ya gyara makarantun jihar, wanda a halin yanzu aka kusa kammalawa da yardar Allah.

Sanadiyyar kokarin sa, an samu karin dalibai masu shiga makarantu a fadin jihar, da kuma karin daukar malamai kwararru da yayi.

Da wannan ne nike cewa a gaskiya Allah ya taimaki jama’ar jihar Kaduna da zakakurin shugaba, jarumi, kuma adali, mai kishin talakawan sa. Ina rokon Allah yaci gaba da taimakon sa, da yi masa jagora, akan irin wadannan namijin kokari da yake yi wa jjhar sa, sannan ina rokon Allah ya ba shi ikon dare wa kan karagar mulkin Najeriya baki daya, domin irin wadannan shugabannin ne kasar nan ta ke bukata a halin yanzu; wadanda za su sa gaba wurin ganin talakawa sun ji dadi. Allah ya taimake shi, yayi masa jagora, amin.

Ya ku ‘yan uwana! Idan za ku iya tunawa, a shekarun baya, mutanen jihar Kaduna sun fada cikin rudani sanadiyyar yawan barkewar rikice-rikice da tashe-tashen hankula a jihar, musamman a wurare irin su Kasuwar Magani da sauran su; rikicin da yake yin sanadiyyar rasa rayukan mutane da dama da kuma dukiyoyin su; sannan ga garkuwa da ake yi da mutane domin karbar kudin fansa, ga rashin zaman lafiya da aka yi fama dashi a fadin jihar, wanda yasa mutane da dama sun fada cikin dimuwa da fargaba a wadancan lokuttan.

Cikin taimakon Allah, mai girma gwamna Malam Nasir Ahmad El-Rufa’i, ya tashi tsaye haikan, da yake Allah ya dubi kyakkyawar niyyar sa, sai ya taimake shi, ya kawo karshen wadannan rikice-rikice.

Sanadiyyar Allah ya azurta jihar Kaduna da jarumin gwamna, marar tsoro, wanda ya kasa zaune ya kasa tsaye don ganin rikici a jihar bai fi karfin gwamnati ba kamar yadda yakan faru a da can baya, da sai an yi dimbin kashe-kashe, an kona gidaje da dakunan Ibadah kafin a kawo wa mutane dauki, wannan karon gwamna Malam Nasir Ahmad El-Rufa’i yayi namijin kokari da tsayuwar daka, wurin ganin hakan bai sake faruwa ba da ikon Allah da taimakon sa.

Da kansa ya rika fita titunan jihar, kwararo-kwararo, sako-sako, lungu-lungu, kauye-kauye, karkara-karkara yana kokarin tabbatar da ganin ana bin doka da oda, sannan kuma mutane basu dauki hukunci da doka a hannun su ba.

Ya ku ‘yan Najeriya! Lallai, babu shakka, irin wannan salon gudanar da mulki irin na mai girma gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufa’i, ya nuna cewa, shi ya cika gwani kuma abin alfaharin kowa, duba da yadda ya tabbatar da cewa, ya zama zakaran gwajin dafi cikin takwarorin sa gwamnoni, kuma garkuwa ga al’ummar sa ta jihar Kaduna.

Tun bayan rantsar da shi a karon farko, da shigar sa Ofis, a shekarar 2015, a matsayin zababben gwamnan jihar Kaduna, karkashin tutar jam’iyyar APC, Malam Nasir Ahmad El-Rufa’i ya tarar da jihar cikin kangin fatara da talauci gami da tabarbarewar al’amurran tsaro, da na ilimi, hadi da kiwon lafiya, biyo bayan kura-kurai da tabargazar da gwamnatocin baya suka tafka. Amma cikin hanzari da himma, mai girma gwamna ya sanya kaimi domin magance dukkan matsalolin da suke addabar jihar.

Cikin wadannan shekaru, duk wanda yasan Kaduna, wallahi yasan cewa mai girma gwamna ya samu gagarumar nasarar ciyar da jihar Kaduna gaba ta fannoni daban-daban, sai fa idan mutum ya kasance shi dan adawar siyasa ne, to anan irin wadannan kuwa ba za su taba ganin gaskiya ba balle har su bi ta. Malam Nasir Ahmad El-Rufa’i ya bayar da gudummawa sosai a wurare da dama, misali:

1. Fannin Tsaro

2. Fannin Ilimi

3. Fannin Tattalin Arziki

4. Fannin Kiwon Lafiya

5. Fannin Siyasa

6. Rikicin Fulani Da Makiyaya da sauran su.

Haka zalika, duba da nagartar sa, da kuma irin ayyukan alkhairin da ya shuka a jihar sa, yasa mai girma shugaban kasa, Alhaji Muhammadu Buhari ziyartar jihar sau da dama domin kaddamar da ayukka tare kuma da yaba masa kan yadda yake kokari wurin tabbatar da zaman lafiya da hadin kan ‘yan jihar.

Duk wadannan batutuwa, kadan ne na zazzakulo maku daga kowane fanni da mai girma gwamna, Malam Nasir Ahmad El-Rufa’i ya tabo cikin shekarun da yayi yana jan ragamar mulkin jihar Kaduna. Domin wannan shafi yayi kadan matuka wurin iya zayyano komai a cikin lokaci guda.

Shakka babu, gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufa’i ya cika jarumi kuma gwarzon namiji, kuma ya cika shugaba nagari abin koyi. Don haka ina ganin ya zama dole in yaba wa wannan jajirtacce, gwani, zakaran gwajin dafi cikin takwarorin sa gwamnoni, kuma abin alfaharin talaka, wanda ya cancanci ya jagoranci kasar nan zuwa tudun-mun-tsira da yardar Allah!

Duba da wannan, yasa nike ganin cancantar ‘yan Najeriya su tashi tsaye gaba dayan su, da rokon Allah da addu’o’i, domin ganin cewa Allah yasa wannan bawan Allah ya zama shugaban kasar Najeriya, domin kowa yaji dadi, ya amfana! Ya Allah ka amsa muna, amin.

Wassalamu Alaikum,

Dan uwan ku, Imam Murtadha Muhammad Gusau, ya rubuto daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa ta adireshi kamar haka: ko kuma 08038289761.

Tags: Abubakar Al-SadiqGwaniHausajajirtacceNasir Ahmad El-Rufa'iPREMIUM TIMESRa'ayi
Previous Post

Sabon rikici tsakanin gwamnati da kamfanonin wutar lantarki ya tirnike

Next Post

ZABEN 2019: Atiku ya garzaya Kotun Koli

Next Post
Atiku and Buhari

ZABEN 2019: Atiku ya garzaya Kotun Koli

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Dandazon Ƙudan zuma sun kashe wani ɗalibin makarantar Firamare a Kano
  • KOTUN KOLI TA KIRA WA AMAECHI RUWA: Dole ya bayyana gaban kwamitin Wike don amsa zargin handame naira Biliyan 98
  • HIMMA DAI MATA MANOMA: Rashin samun tallafi da lamuni daga bankuna bai hana mata hoɓɓasa wajen shiga harkokin noma ba
  • RAHOTO: Sama da mutum 3036 ke jiran a zartas masu da hukuncin kisa a Najeriya
  • MAFARAUTAN APC A SAKE SHIRI: Kotu ta wanke Jonathan fes, ta ce zai iya fitowa takarar 2023

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.