• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Wallahi Zamfarawa Kuyi Hattara Da ‘Yan 419!!! Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
August 4, 2019
in Ra'ayi
0
Bello Matawalle

Bello Matawalle

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jin Kai

Assalamu Alaikum

Ya ku ‘yan uwana al’ummar jihar Zamfara, wannan wani irin muhimmin sako ne nike son isar wa zuwa ga re ku baki daya. Wannan sako ina mai isar da shi zuwa ga reku ne tsakanina da Allah, da kuma irin yadda Allah madaukakin Sarki ya fahimtar da ni gwargwado, game da abun da yake gudana na siyasar Jihar mu mai albarka ta Zamfara. Ya ku ‘yan uwa na, zan baku wannan shawara ne, zan isar da wannan sako zuwa ga re ku ne, ba don siyasa ba, ba don maganar jam’iyyah ba, ba don wani abun duniya ba, a’a, sai dai domin kishi na ga Jiha ta, tare kuma da bakin ciki na akan matsalar tsaro da muke fama da shi, wanda alhamdulillahi, ko hasidin iza hasada yasan da cewa, da ikon Allah, yanzu gwamnan talakawa, gwamna mai ci, Dr. Matawalle yana kokari matuka akai. Muna rokon Allah har kullum, da yaci gaba da agaza masa, yaci gaba da taimakon sa, akan wannan namijin kokari da yake yi, amin.

Imam Murtada Gusau
Imam Murtada Gusau

Ya ku Zamfarawa! Ina kiran ku da cewa na farko, kuji tsoron Allah. Ku sani, ya zama dole, tilas, wajibi ku bayar da dukkanin goyon bayan ku ga wannan Dan taliki, wato gwamna Matawalle. Ina mai yi maku rantsuwa da Allah, wanda babu abun bautawa da gaskiya sai shi, Mahaliccin kowa da komai, Allah wanda zan tashi a gaban sa domin yayi mani hisabi. Allah wanda ina sane zan amsa tambayoyi a gaban sa, cewa ban san gwamna ba kuma bai sanni ba, ban taba ganin sa ba, kuma bai taba gani na ba, ban taba yin wata hulda da shi ba, haka shi ma bai taba hulda da ni ba. Amma ina bai tabbatar maku, wallahi wannan mutum, wato gwamna Matawalle mai kishin ku ne, mai tausayin ku ne, mai son ci gaban Jihar Zamfara ne. Sannan dukiyar al’ummah ba ita ce a gaban sa ba. Don haka wallahi, mutum irin wannan, dattijo, bawan Allah, mutumin kirki ya zama dole ku taimaka masa, ku bashi dukkanin irin nau’in goyon baya da hadin kai da yake nema daga wurin ku. Sannan wallahi, ina mai jan kunne a gare ku, ina mai gargadin ku, ina mai hada ku da Allah, da kar ku yarda da dukkanin masu yiwa wannan gwamna zagon kasa da sunan siyasa ko wani abu wai shi adawa.

Ya ku ‘yan uwa na Zamfarawa! Ku sani, dukkanin ku kuna sane da irin halin da Jihar mu ta ke ciki, na kalubalen tsaro, talauci, rashin ingantaccen ilimi da rashin abubuwan more rayuwa. Dukkanin ku kuna sane da irin halin ka-ka-ni-ka-yi, halin ni ‘ya su, halin wayyo Allah da Jihar mu ta shiga, sanadiyyar halin ko’inkula, halin cuta da zalunci, da gwamnatin da ta shude ta jefa Jihar a ciki! Mun yi addu’o’i, mun yi ta azumi da alkunuti, domin Allah ya dube mu da idon rahama, ya kawo muna canji na alkhairi, ya kawo muna shugaban da muke so, yake son mu, muke yiwa addu’a, yake yi muna; wato irin shugaban da Manzon Allah (SAW) ya siffanta a cikin Hadisin Ka’ab Dan Malik, da ke cikin Sahih Muslim. Sai ga shi Allah ya taimake mu, ya agaza muna, ya kalli kukan mu, ya ceto mu daga hannun azzalumai, ya amsa addu’o’in mu, ya kawo muna zakakuri kuma jarumin gwamna, mai son talakawan jihar sa tsakanin sa da Allah.

Daga zuwan wannan bawan Allah, wallahi duk mun ga canji, aiki ba kama hannun yaro, biyan albashi ba wasa; ya mayar da hankali sosai matuka, wurin ganin Jihar mu ta samu cikakken tsaro mai dore wa.

Sai ga shi wai an samu wasu miyagun ‘yan siyasa, wadanda sune asalin wadanda suka jefa Jihar cikin mummunan hali a can baya, saboda salon mulkin su irin na fir’auna, wai da sunan adawa, suna sukar kokarin da wannan bawan Allah yake yi. Har nike samun labari, daga majiya kwakkwara, wai wadannan miyagun ‘yan siyasa, za su yi dukkan mai yiwuwa su ga cewa wai sun kawo cikas ga duk irin kokarin da wannan bawan Allah, gwamnan al’ummah, gwamnan talakawa, Alhaji Bello Matawalle yake yi a Jihar.

Don haka, muna isar da sako zuwa ga wadannan miyagun ‘yan siyasa su sani cewa, wallahi ta Allah ba ta su ba, kuma da ikon Allah Zamfarawa ba wawayen mutane ba ne, kuma ba gidadawa ba ne, kuma ni nasan ba kidahumai ba ne. Wallahi ina sane da cewa za su yi iya kokarin su domin ganin sun baiwa wannan bawan Allah goyon baya, domin ciyar da jihar mu mai albarka gaba. Duk wani yunkuri na su na sharri, da duk wani makirci na su, da yardar Allah Subhanahu wa ta’ala ba za su taba cin nasara ba. Allah zai taimaki gwamna Matawalle da Zamfarawa da Jihar Zamfara akan su. Ai an sha mu mun warke. Irin azaba da gwale-gwale da Zamfarawa suka sha a hannun ku sun isa haka nan. Malam bahaushe yake cewa, ‘KIFI NA GANIN KA MAI JAR KOMA.’

Ya ku al’ummar Jihar Zamfara! Ku sani, lallai gwamna Matawalle na bukatar goyon bayan ku, da gudummawar ku, da hadin kan ku, domin ya kawo ci gaba mai dorewa a wannan Jiha ta mu mai albarka. Kar ku yarda da ‘yan 419 da sunan adawar siyasa, kar ku yarda da duk wani da zai mayar maku da hannun agogo baya. Ya zama dole ku so Matawalle, domin shine ya fara nuna maku kauna. Kuma shine yake son Jihar ku ta ci gaba kuma ta zauna lafiya.

Ya ku jama’ar Jihar Zamfara! Don Allah kuyi wa kan ku adalci mana, ku duba ku gani, don girman Allah yaushe rabon da ka ga ma’aikatan jihar Zamfara suna turereniya wurin sayen ragunan layyah? Wallahi har an mance da wannan a Jihar Zamfara, saboda halin tagayyara da azzalumai suka jefa al’ummah a ciki! Amma yau ka tafi Jihar, kayi fira da talakawa, kayi fira da ‘yan kasuwa, kayi fira da manoma, kayi fira da mata, kayi fira da matasa, kayi fira da ma’aikata, ka tafi kasuwa ka ga yadda ma’aikata suke murna da farin ciki. Ai wallahi yabon gwani ya zama dole!

A tarihin kirkiro Jihar Zamfara, gwamnan mulkin soja, Jibril Bala Yakubu yayi kokari matuka, a lokacin da yake gwamna. Haka, bayan shigowar siyasa, gwamna Ahmad Sani Yariman Bakura shima wallahi yayi iya nasa kokari a lokacin sa. Haka nan gwamna Mamuda Aliyu Shinkafi, shima Allah ya sani, yayi kokari matuka. Amma wallahi, ina mai rantsuwa da Allah, gwamna Abdul’azizi Yari, babu abun da yayi in ba ruguzawa tare da rusa Jihar Zamfara ba! Don haka mu ba abun da zamu ce masa, illa Allah ya isa! Kuma wallahi sai Allah yayi muna sakayya akan cin amanar Jihar mu da yayi.

Mu ba ruwan mu, wallahi duk mutumin kirki zamu bayyana shi domin mutane su san shi kuma su so shi, suyi masa addu’a da fatan alkhairi. Haka nan mutumin banza zamu bayyana shi domin mutane su guje shi, kuma su yi Allah waddai da shi da mugun halin sa. Wannan shine maganar gaskiya.

Zamfarawa kuyi hattara! Gwamnan talakawa Matawalle lallai ya nuna maku halacci, saboda haka ya zama dole, ya zama tilas, ya zama wajibi ku nuna masa halacci. Kar ku yarda da duk wani mai soki-burutsu, dan 419; wanda zai nuna maku cewa gwamna Matawalle mutumin banza ne. Duk wanda ya gaya maku haka kuce karya yake yi, ko shi wanene, domin kun gani a kasa!

Allah ya taimake mu, ya zaunar da yankin mu na arewa lafiya, ya zaunar da Jihar mu ta Zamfara lafiya, da dukkanin sauran Jihohi, da ma Najeriya baki daya, amin.

Nagode,

Dan uwan ku:

Imam Murtadha Muhammad Gusau, daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa a lamba kamar haka: 08038289761 ko kuma gusaumurtada@gmail.com

Tags: AbujaAikiBelloGusauHausaihar KogiLabaraiMatawalleMuhammadNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

SHARI’AR EL-ZAKZAKY: An tsaurara matakan tsaro a Kaduna

Next Post

Kotu ta bada belin El-Zakzaky

Next Post
El-Zakzaky in Court

Kotu ta bada belin El-Zakzaky

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • KADUNA 2023: Uba Sani ya zaɓi Hadiza Balarabe mataimakiyar sa
  • ‘Yan bindiga sun kashe Sojoji 30, ‘yan sanda 10 da farin hula 12 a makon jiya
  • Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki
  • MAIDA HANNUN AGOGO BAYA: ‘Yan-ta-kife sun banka wa ofishin INEC wuta a Enugu
  • SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.