• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    SABODA TIWITA: Sanatocin PDP sun fice daga Zauren Majalisar Dattawa

    Zaɓaɓɓun Sanatocin Arewa ta Tsakiya sun nemi a ba su Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ko a-yi-ta-ta-ƙare

    KIDAYA: An kashe naira biliyan 200 wurin shirye-shiryen fara ƙidayar jama’a – Shugaban Ƙidaya

    KIDAYA: An kashe naira biliyan 200 wurin shirye-shiryen fara ƙidayar jama’a – Shugaban Ƙidaya

    INEC ta rantsar da Isah matsayin kwamishina a karo na biyu

    INEC ta rantsar da Isah matsayin kwamishina a karo na biyu

    ƘAƘUDUBAR TALLAFIN FETUR: Buhari ya bukaci majalisar Dattawa ta amince masa ya tattago bashin dala miliyan 800

    AYYUKAN BAN-KWANA DA GWAMNATI: Buhari ya damƙa filin jirgin Kano da na Abuja ga Amurkawa

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    SABODA TIWITA: Sanatocin PDP sun fice daga Zauren Majalisar Dattawa

    Zaɓaɓɓun Sanatocin Arewa ta Tsakiya sun nemi a ba su Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ko a-yi-ta-ta-ƙare

    KIDAYA: An kashe naira biliyan 200 wurin shirye-shiryen fara ƙidayar jama’a – Shugaban Ƙidaya

    KIDAYA: An kashe naira biliyan 200 wurin shirye-shiryen fara ƙidayar jama’a – Shugaban Ƙidaya

    INEC ta rantsar da Isah matsayin kwamishina a karo na biyu

    INEC ta rantsar da Isah matsayin kwamishina a karo na biyu

    ƘAƘUDUBAR TALLAFIN FETUR: Buhari ya bukaci majalisar Dattawa ta amince masa ya tattago bashin dala miliyan 800

    AYYUKAN BAN-KWANA DA GWAMNATI: Buhari ya damƙa filin jirgin Kano da na Abuja ga Amurkawa

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

SAKACI: Yadda Gwamnatin ‘Yar’Adua, Jonathan da Buhari ke neman janyo wa Najeriya asarar naira Tiriliyan 3.2

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
August 22, 2019
in Rahotanni
0
Muhammadu Buhari

Muhammadu Buhari

Ranar Juma’a da ta gabata ne Kotun Sauraren Kararrakin Kasuwanci da Cinikayya ta Birtaniya, a karkashin Mai Shari’a J. Butcher, ta yanke hukuncin yanka wa Najeriya diyyar tarar dala bilyan 9.

Butcher ya umarci Najeriya ta biya kamfanin P&ID, wato Process Industrial Development Limited, zunzurutun kudade kwatankwacin naira tiriliyan 3.7.

Wadannan kudade an yanka wa Najeriya biyan su a matsayin karya yarjejeniyar kwangila da ta yi, tsakanin ta da P&ID.

Wannan kwangila dai tun zamanin mulkin Marigayi Umaru Yar’Adua aka bada ta. Amma daga bisani ta zama alakakai, har rikicin ya mirgina zuwa kotun Birtaniya.

DALLA-DALLA: Bayanin dangane da kokarin karya arzikin Najeriya Warwas

1 – An kakaba wa Najeriya biyan diyyar ce saboda kin cika alkawarin da ta yi, inda ta karya jarjejeniyar kwangila. Wannan laifi da aka tuhumi Najeriya da yi, ya haifar da dimbin asara ga kamfanin P&ID.

2 – Kwangila ce ta harkar gina masana’antun sarrafa gas da aka cimma yarjejeniya tun cikin gwamnatin marigayi Umaru ’Yar’Adua, cikin 2010.

3 – An ci Najeriya tarar a karkashin Dokar Haramcin Karya Yarjejeniyar Kwangiloli ta Ingila da Wales, ta 1996, da kuma Dokar Haramcin Karya Yarjejeniyar Cinikayya ta Najeriya, mai lamba: CAP A18 LFN ta shekara ta 2004.

4 – An yanke hukuncin ne bayan Najeriya ta shafe shekaru sama da biyar ta na sakacin kin daukaka kara.

5 – Idan har Najeriya ta kasa yin nasarar shawo kan wannan gagarimar matsala ta hanyar sasantawa ko kuma sa’ar yin nasara idan ta daukaka kara, to za a kwace dukiyar Najeriya da ke bankunan Ingila da Amurka, har kwatankwacin dala bilyan 9, wato naira tiriliyan 3.2 kenan, a damka wa kamfanin P&ID.

6 – Akwai matsaloli da mishkiloli a cikin kwangilar, wadda tsohon Ministan Fetur na zamani Umaru Yar’Adua, Rilwanu Lukman ya sa wa hannu. An sa wa kwangilar hannu a lokacin da Umaru ba shi da lafiya, ya na ta hakilon neman lafiyar sa tsakanin Ingila da Saudiyya.

7 – Kotu ta rattaba hukuncin ne tun cikin 2015, watanni biyu bayan Shugaba Muhammadu Buhari ya hau mulki.

8 – Shugaban lokacin Goodluck Jonathan ya bar wa Buhari gadon warware matsalar, saboda har ya sauka lauyoyin Najeriya sun tsaya Turanci, maimakon maida hankali wajen warware matsalar.

9 – Buhari ya yi sakacin rashin nada ministoci kan lokaci, wanda hakan ya sa Najeriya ta rasa ministan shari’a da zai bai wa Buhari shawara cikin gaggawa dangane da yadda za a shawo kan lamarin, kafin kotu ta yanke hukunci.

10 – Wadanda su ke kewaye da Buhari a lokacin, watau fadawan sa ‘yan-ba-ni-na-iya, sun nuna masa cewa matsalar gwamnatin PDP ce.

11 – Duk da cewa a yanzu Najeriya ta farka daga likomon gare da ta ke yi, ta na ta gwagwagwar ganin ta yi nasarar rashin biyan diyyar, duk wanda ya nakalci yadda rigimar ta ke, zai tabbatar da cewa da wahalar gaske dan akuya ya kayar da kura a kokawar tsakiyar dokar jeji.

12 – Najariya ta yi sakacin gaske tun daga zamanin Yar’Adua da Jonathan har zuwa yanzu zamanin Buhari. Saboda a wannan kasar ba a dauki karya doka ko karya yarjejeniya a matsayin babban laifi ba, su Turawa bah aka su ke ba.

13 – Haka ba a damu da hukunta manyan da suka karya doka a Najeriya ba, kamar yadda Najeriya ba ta damu ba idan ta karya doka a cikin kasar ta.

14 – Kasashen Turai sun dauki komai da muhimmanci. Inda wani ya yi rawar banjo a Najeriya aka ba shi kudi, idan ya yi wannan rawar a wata kasa, to dukan tsiya zai sha.

KWANGILAR GAS: Yadda Kilu Ta Jawo Wa Najeriya Bau

1 – Najeriya ta kulla yarjejeniya da kamfanin P&ID, mallakar wadansu Turawa biyu, Micheal Quinn da kuma marigayi Brendan Cahill. Kamfanin ya kai shekaru 30 da kafuwa, kuma kwararre ne wajen iya aikin sa.

2 – An kulla yarjejeiyar tsakanin PID cikin watan Janairu, 2010 domin gina masana’antar sarrafa gas a Najeriya. Kwangila ce aka kulla ta tsawon yarjejeniyar shekaru 20.

3 – Rilwanu Lukman, wanda ya rasu cikin 2014 ne ya sawa kwangilar hannu a matsayin sa na Ministan Fetur lokacin Umaru Yar’Adua ya na kwance asibitin Saudiyya ya na jiyya.

Yaya aka kulla Yarjejeniyar Kwangilar?

1 – An kulla cewa Najeriya ke da kashi 85 bisa 100 na tataccen gas wanda za a rika amfani da shi wajen samar karfin hasken lantarki da inganta masana’antu.

2 – Shi kuma P&ID zai rika karbar kashi 15 bisa 100 kenan tare da cin moriyar sinadaran ‘methane, ‘propane’ da ‘butane’, wadanda za su rika fitarwa kasashen waje.

3 – Ita ma Najeriya za ta amfana da kashi 10 bisa 100 daga sinadaran uku da P&ID zai rika fitarwa su sayar a kasashen waje.

Ka’idojin da Najeriya da P&ID suka gindaya wa juna

A cikin wannan jarjejeniya dai akwai cewa: Najeriya za ta rika samar da gas mai yawan ma’aunin scf milyan 150 ga masa’antar wadda P&ID za ta gina. Idan tafiya ta yi nisa kuwa, za a kai har ana samar wa masana’antar da gas jejin scf milyan 400. Kamfanonin hako mai ne ke samar da gas a kasar nan.

Yadda aka fara yi wa kwangilar ‘SHILLON-BILYA’

1 – An amince a rubuce cewa Najeriya za ta gina ko ta shimfida bututun da za a rika tunkuda gas zuwa masana’antar da P&ID zai gina a Adiabo, cikin Karamar Hukumar Odukpani, a Jihar Cross Rivers. Gwamnati ce za ta rika samar wa P&ID gas din da kan ta, daga rijiyar mai ta OML 67 da ta 123 wadda kamfanin Addax Petroleum ke har mai a ciki.

2 – To daga nan ne labari ya sha bamban, al’amurra suka sakwarkwace, ko kuma aka sakwarkwatar da al’amurran.

3 – Ita dai Najeriya ba ta gina ko shimfida bututun a karkashin kasa zuwa inda P&ID ya ce a kai mata su ba.

4 – Sai P&ID ya ce ya kashe dala milyan 40 wajen aikin gina masana’antar gas, wadda kuma rashin shimfida bututun gas da Najeriya ba ta yi ba, babban laifin karya yarjejeniyar kwangila ta duniya ce.

5 – An kasa warware wannan matsala a lokacin Jonathan, domin bayan kulla yarjejeniyar Umaru bai dade a kan mulki ba, ya rasu.

6 – Cikin watan Agusta, 2012, sai P&ID ya fusata, ya maka Najeriya kara a Kotun Bin Diggidin Karya Jarjejeniyar Kwngila a Cinikayya a London.

7 – P&ID ya nemi kotu ya tilasta wa Najeriya biyan ta diyyar asarar da ta tabka, ciki kuwa har da kirdadon irin ribar da za ta samu a tsawon shekaru 20 na tsawon yarjejeniyar duk kamfanin ya nemi Najeriya ta biya shi.

Yadda Jonathan da Buhari suka gaji Alakakai

1 – A lokacin Jonathan an yi kokarin sasantawa, inda P&ID ya nemi a biya shi diyyar dala bilyan 1.5, amma a karshe ya amince da zai karbi dala milyan 850.

Wannan sasantawa ta samu tsaiko, saboda Jonathan bai yi nasarar zabe a 2015 ba. Tilas ya bar wa gwamnatin Buhari mai jiran hawa mulki a lokacin cin gadon yadda za ta warware wannan kwatagwangwama. Dama shi ma Jonathan ya tsaya jan-kafa ya na neman a rage kudin daga dala milyan 850 zuwa kasa da haka, har ya sauka ba a cimma matsaya ba.

Buhari ya yi sakacin rashin nada ministoci kan lokaci, wanda hakan ya sa Najeriya ta rasa ministan shari’a da zai bai wa Buhari shawara cikin gaggawa dangane da yadda za a shawo kan lamarin, kafin kotu ta yanke hukunci.

Da yawan masu sharhi sun tafi a kan cewa wadanda su ke kewaye da Buhari a lokacin, watau fadawan sa ‘yan-ba-ni-na-iya, sun nuna masa cewa matsalar gwamnatin PDP ce. Saboda a lokacin bai nada ministoci da wuri ba.

Katsam, cikin watan Yuli, 2015, watanni biyu bayan hawan Buhari, sai kotu ya yanka wa Najeriya biyan P&ID diyyar dala bilyan 6.6, sai kuma karin wata dala bilyan 2.3 da kotu ta amince cewa su ne kiyasi ko kirdadon ribar da P&ID zai iya samu a tsawon shekaru 20 ya na huldar da Najeriya, idan da yarjejeniyar ta tafi salum-alum, yadda aka gindaya.

BUHARI – Gaba Kura Baya Siyaki

A gaskiyar magana, Buhari bai dade da hawa mulki ba sai farashin danyen mai ya karye a kasuwannin duniya. Sannan kuma naira ta rika yin faduwar ‘yan bori da duk lokacin da ta yi arba da dalar Amurka.

Sai dai kuma da daman a ganin cewa shi ma ya yi sakaci, domin idan ya na ganin ba zai iya biyan P&ID ba dala milyan 850 ba, zai iya neman sassauci, don kada a bari ta sake garzayawa kotu a lokacin.

Ga shi kuma a lokacin ana halin walle-walle, har jihohin kasar nan ba su iya biyan albashin ma’aikatan su.

Ina Mafita?

Babu wata mafita sai dai Najeriya ta sake neman zama teburin sasantawa da P&ID, domin matsawar hukuncin da kotun Landan ta zartas ya tabbata, kuma Kotun Amurka ta rattaba irin wannan hukunci a kan Najeriya, to za a tatsi wadannan makudan kudade daga asusun gwamnatin tarayya na Ingila da Amurka ta dankara wa P&ID.

Amma kuma yanzu Gwamnan Babban BANKIN Najriya, Godwin Emefile da Babban Sakatare na Ma’aikatar Shari’a, sun sha alwashin cewa wannan hukunci ba zai hau kan Najeriya.

Ko ya abin zai karke? Dabara ta rage ga mai shiga rijiya!

Me hakan Zai haifar?

Ko tantama babu wannan hukunci idan ya tabbata zai jefa Najeriya cikin matsin tattalin arziki matuka. Domin ba a taba yi wa wata kasa irin wannan hukuncin biyan diyyar karya yarjejeniyar kwangila ta makudan kudade haka kamar Najeriya ba.

Tags: BirtaniyaButcherfeturGoodluckHausaJonathanMarigayiNajeriyaPREMIUM TIMESRilwanu LukmanYar'adua
Previous Post

ZABEN MAJALISAR DATTAWA: Kotu ta wancakalar da karar da Shehu Sani ya shigar

Next Post

Boko Haram sun kwace Ikon kananan hukumomi biyu a Barno

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Borno Attack

Boko Haram sun kwace Ikon kananan hukumomi biyu a Barno

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • JAWABIN BANKWANA: Na gama da ku lafiya, inda na gaza kuma a yayyafe – Buhari
  • TASHIN HANKALI A FILATO: Miyetti Allah sun yi kururuwar Jasawa na shirin kakkaɓe su ƙarƙaf, an kwashe masu shanu 25,000 cikin mako biyu
  • SUN CI TALIYAR ƘARSHE: Sanata Lawan ya damu ganin kashi 70 bisa 100 na ‘Yan Majalisa sun faɗi zaɓe
  • RIGIMAR SHUGABANCIN MAJALISA: ‘Ina goyon bayan Abbas, shi zan yi wa kamfen wurjanjan’ – Wike
  • RASHIN SANI: Yadda jami’an Kwastam suka bindige ɗan uwansu Jami’i a shingen bincike

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.