• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

JANAR BABANGIDA: Allah ya kara wa Rayuwa Albarka, Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
August 18, 2019
in Ra'ayi
0
JANAR BABANGIDA: Allah ya kara wa Rayuwa Albarka, Daga Imam Murtadha Gusau

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jin Kai

Assalamu Alaikum

‘Yan uwa na masu girma! Daga cikin manyan mu masu albarka, kuma tsoffin shugabannin kasar nan ta mu mai albarka, wato Najeriya, Shugaba Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), shine shugaban da aka taba samu ya aikata ayyukan alkhairi, masu amfani ga al’ummah har sama da guda dubu daya a zamanin mulkin sa da yayi na shekaru takwas. A inda ni dai a iya sani na, bayan Shugaba Babangida din, babu wani Shugaba guda daya tak duk tarihin nahiyar Afirka, da tarihin Shugabanni da su ka ta ba yin hakan. Kai ko da Shugabannin da suke kan kujerar shugabancin kasashen su a halin yanzu, ban ji wani wanda ya kwatanta hakan ba, idan dai ba Gamji Dan kwarai, Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato ba. Wanda ya gina kuma ya samar da ayyukan alkhairin da ba su kirguwa a fadin yankin Arewa; Jami’ar Ahmadu Bello Zariya (ABU), daya kenan daga cikin ayyukan Sardauna da muke amfana da su har yau. Sai kuma wasu ayyukan da yawancin su Gwamnonin mu na Arewa goma sha tara sun yi watsi da su, inda hakan yasa suka balbalce, yayin da suka sayar da wasu; irin su Babban Bankin Arewa, wato Bank of the North!

Imam Murtada Gusau
Imam Murtada Gusau

Kadan daga wasu ayyukan alkhairin IBB

Shugaba Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), shine ya gina fadar mulki ta Shugaban kasa da ke babban Birnin Tarayyar Najeriya, wato Aso Rock Villa Abuja, kuma shine ya fara tare wa a cikin ta. Shine ya samar da gine-gine masu amfani a babban Birnin Tarayya, wato Abuja, kamar: Eagle Square, Federal Secretariat, FCDA Secretariat, National Mosque, National Church, National Assembly, Supreme Court, Court of Appeal, Barikin sojoji har guda goma a Abuja, Kasuwar Wuse, NNPC Tower.

Sannan kuma Shugaba Babangida shine ya samar da ma’aikatu masu matukar muhimmanci da har yau ake cin ribar su da amfanin su, irin su: NAFDAC, DIFRRI, MAMSER (NOA), CCT, CCB, CCN, Gifted Children’s School Suleja, NHIS, NEXIM, NDIC, NDLEA, FRSC, ECOMOG, Ministry of Women Affairs, NWC, National Mathematical Center, NDE, Ministry of Agriculture and Rural Development, NAFSESS, NSFCP, FUMTP, NPB, FEPA, NALDA, CDS, RMRC, CMEWS, NEPC, FMIDS, Petro-Chemical Plant Kaduna, Petro-Chemical Plant Eleme, Osaka Dam Ajaokuta, Shiroro Hydro Power Station Niger, Dukkanin Sakatariyoyin Gwamnatocin Jihohin Najeriya, da kuma dukkan sakatariyoyin da yanzu haka ake amfani da su a kowace karamar hukuma, sai Delta IX Gas Turbine Plant da tagwayen hanyoyin Abuja zuwa Kano, da hanyoyi masu tarin yawa da ba zai yiwu a fade su ba a dan wannan rubutu takaitacce.

Sannan Shugaba Babangida bai taba sayo tataccen man fetur daga wata kasar waje ba. Duk man fetur din da aka sha a zamanin mulkin sa, a matatun man da Nijeriya ke da su aka tace shi. Kuma a lokacin sa duk matatun man Nijeriya suna aiki dari-bisa-dari, haka ya sauka daga kan mulki ya bar su!

Sannan Shugaba Ibrahim Badamasi Babangida ne ya kirkiro sabbin Jihohi guda goma sha uku, a duk fadin Nijeriya don talaka ya amfana kuma ya san cewa ana mulki. A inda kafin hakan da kuma bayan hakan, babu wani shugaban Nijeriya da ya girmama talaka, ta hanyar kirkiro sabbin Jihohi da yawa haka domin talaka ya amfana, gwamnati ta zo kusa da shi.

Ga jerin Jihohin da IBB ya Kirkiro kamar haka:

1. Jihar Adamawa

2. Jihar Katsina

3. Jihar Jigawa

4. Jihar Yobe

5. Jihar Kebbi

6. Jihar Delta

7. Jihar Edo

8. Jihar Taraba

9. Jihar Kogi

10. Jihar Abia

11. Jihar Osun

12. Jihar Enugu

13. Jihar Akwa Ibom

Sannan Shugaba Ibrahim Badamasi Babangida shine ya yawaita kananan hukumomi a Nijeriya, har yawan su ya kai 774. Sannan babu mamaki, kai da ke karanta rubutun nan a halin yanzu, idan ba domin hakan da IBB yayi ba, da watakila har yanzu Jihar ku babu ita a cikin jerin Jihohin Najeriya da muke da su yanzu. Sannan kuma da yanzu kana cikin wata karamar hukuma ne a jone. Amma sai ga shi saboda halin karimci da kishin ci gaban rayuwar ka, IBB din da babu mamaki mai yiwuwa har da kai ake zama ana zagin sa, ana cin mutuncin sa, ana maganganun da basu dace ba na batanci a gare shi. To ya kai bawan Allah, ka sani, ko-ka-ki ko-ka-so, shine dai mai kaunar ka tsakanin sa da Allah, tun da gashi nan ya kirkiro maku Jiha da karamar hukuma da kake cin gajiyar su da amfanin su a yau, wanda hakan ce ma ta baka damar samun bakin magana da babatu!

Sannan duk wanda ya san tarihin kasar nan, yasan da cewa Shugaba Ibrahim Badamasi Babangida ya bar Dalar Amurka kan farashin Naira goma sha takwas (N18). Sannan ba’a taba ganin dogon layin man fetur a gidajen mai ba, kai ko da kuwa sau daya ne, duk tsawon shekarun da yayi yana mulkin Najeriya.

Sannan shine Shugaban da ya fara samar da fanfunan tuka-tuka, wato Boreholes, a kauyukan da bututun ruwan fanfo wato Pipes din famfo ba su karasa ba.

Kuma har ila yau, a zamanin mulkin sa ne ‘yan Najeriya suka amfana da ruwan famfo a ko’ina, ba tare da wata wahala ba. Sai mutum ya bude, ya kunna yayi amfani da shi, idan ya gama sai yayi tafiyar sa, ya bar kan famfon a kunne yana ta zubar da ruwa a banza, saboda wadata da kuma irin yadda IBB din ya jajirce, ya tabbatar da ganin cewa ruwan famfon sun wadaci kowa da kowa, kuma sun shiga kowane lungu da sako na Najeriya.

Amma duk da wannan kokari da jajircewa da wannan bawan Allah yayi, wai a yau zaka samu wasu mutane suna zagin sa, suna suka tare da cin mutuncin sa. Ba domin komai ba sai don saboda son zuciya irin ta Dan Adam, ko domin saboda ya jahilci wannan bawan Allah, ko don an wanke kwakwalwar mutum, an yi masa karya da farfaganda cewa IBB mutumin banza ne. Wallahi ka sani ya kai bawan Allah, kana rage masa zunubai ne da wannan zagin naka mara dalili.

Eh, mun san da cewa IBB ajizi ne, mutum ne, Dan Adam ne kamar kowa, yana iya yin daidai kuma yana iya yin kuskure. Domin shi ba Annabi ba ne kuma ba Mala’ika ba ne ko wani katangagge ko ma’asumi daga aikata laifi ko kuskure. Amma dai ni nayi imani da Allah, ayyukan alkhairin sa sun fi na sharrin sa yawa!

Saboda haka, ina kira da muji tsoron Allah, mu girmama manyan mu. Kar mu yarda mu biye wa ‘yan kudu da wasu shedanun mutane da suke zagin wannan bawan Allah mai daraja da nagarta, saboda wata manufa ta su da suke bukatar cimmawa ta sharri. Alhali idan muka duba, zamu ga cewa ai su suna girmama nasu manyan. To don me kuwa za su rinka zuga mu mu muna cin mutuncin namu manyan?

Ina rokon Allah ya shirye mu, yasa mu gane, amin.

Shi kuwa tsohon Shugaban kasar Najeriya, wato Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), wanda ya cika shekaru saba’in da takwas da haihuwa, ina rokon Allah ya kara masa lafiya, imani da nisan kwana; kuma ya kara masa shekaru masu albarka da amfani ga Al’ummah, yasa ya gama lafiya, amin.

Ina rokon Allah ya zaunar da kasar mu Najeriya lafiya, ya taimaki Shugabanin mu, amin.

Dan uwan ku,

Imam Murtadha Muhammad Gusau, ya rubuta daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa a adireshi kamar haka: gusaumurtada@gmail.com ko kuma 08038289761.

Tags: AbujaAikiGusauIBBLabaraiNajeriyaPREMIUM TIMES
Previous Post

WASANNI: Farautar Neymar da Barcelona ke yi, burga ce don a kwantar wa Messi hankali -Le Parisien

Next Post

Shugabannin Igbo basu ga komai ba tukunna, saura gwamnoni – Inji Kanu

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
Nnamdi-Kanu

Shugabannin Igbo basu ga komai ba tukunna, saura gwamnoni - Inji Kanu

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Abubuwa 12 Da Suka Hana A Ga Ƙoƙarin Mulkin Buhari
  • YUNƘURIN BALLEWA DAGA NAJERIYA: Yadda tsagerun Yarabawa suka kama Gidan Radiyon Gwamnatin Tarayya, kwana ɗaya kafin rantsar da Tinubu
  • RA’AYIN PREMIUM TIMES: Shekarun Mulkin Buhari: An sake ɓata goma, biyar ba ta gyaru ba
  • Zan yi tafiya da kowa da kowa a gwamnati na – Uba Sani
  • TINUBU: Abinci zai wadata cikin farashi mai sauƙi

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.