• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Gogarman masu garkuwa Hamisu Wadume ya shiga hannu

Mohammed LerebyMohammed Lere
August 20, 2019
in Labarai
0
Hamisu Wadume

Hamisu Wadume

Gogarman masu garkuwa da mutane Hamisu Wadume da sojoji suka saki bayan sun kashe wasu zaratan ‘Yan sanda ya shiga hannu.

Rahotanni da ya iske mu ya nuna cewa yanzu haka an damke Wadume, sai dai ba a bayyana ko a ina ne aka kama shi ba.

DALLA-DALLA: Yadda gogarman masu garkuwa da mutane, Wadume ya tsere a kwale-kwale

Wannan wani sabon binciken kwakwaf ne da PREMIUM TIMES ta gudanar, inda ta bankado harkalla, kulle-kulle da kisan-fin-karfin da sojoji suka yi wa zaratan ‘yan sanda uku, sannan suka kubutar da gogarman mai garkuwa da mutane daga hannun ‘yan sanda. Dama Hausawa na cewa “makashin ka na gindin ka.” Ku karanta ku ji yadda wannan jarida ta baje muku komai a kan faifai.

An yi wa wadannan zaratan ‘yan sanda masu zakulo masu garkuwa da mutane su uku kisan-gilla ne a daidai kauyen Gidinwaya, wanda ke tsakanin garin Ibi da Wukari a Kudancin Jihar Taraba.

Akwai shingen sojoji a kan kwalta, daidai Gidinwaya, kuma sojojin da ke tsaro da binciken motoci masu wucewa a Gidinwaya din ne suka bude musu wuta. Sojojin daga Bataliya ta 93 da ke Takum ne aka tura su domin aiki a shingen na kan kwalta.

Wannan kisan-gilla ya haifar da babbar barazana ga lamarin tsaron kasar nan tare kuma da haifar da rashin jituwa mai tsami tsakanin Sojojin Najeriya da ‘yan sandan Najeriya.

Jami’an ‘yan sandan da aka bude wa wuta sun a tafiya ne a cikin wata fatar mota bas, sun fito ne daga Ibi, inda suka kamo wani rikakken mai garkuwa da mutane mai suna Hamisu Bala, wanda aka fi sani da Wadume.

Rahoton Wakilin PREMIUM TIMES daga wurin da aka yi kisan

Wakilin PREMIUM TIMES ya ziyarci har wurin da sojoji suka kashe ‘yan sandan a Gidinwaya da ke kan titin Ibi zuwa Wukari.

Binciken da ya yi a can da za ku karanta a yanzu, har da ikirarin da mutanen kauyen suka yi, wadanda ya tattauna da su dangane da yadda abin ya faru.

Binciken PREMIUM TIMES a kauyen ya sha bamban da abin da sojohi suka bayyana cewa ya faru a kauyen na Gidinwaya.

A halin da ake ciki a yanzu, kauyen Gidinwaya kewaye ya ke da sojoji, wasu a kwak-kwance cikin shirin damarar yaki a cikin daji, tsallaken inda aka bindige ‘yan sandan. Sun sa-ido sosai su na lura da yadda mazauna kauyen ke gudanar da harkokin su.

Mutanen kauyen su kuma su na cikin tsaro da fargabar abin da zai iya samun su idan suka fai gaskiyar abin da ya faru dangane da kisan Sufeto Mark Ediale, Sajen Usman Danzumi da Sajen Dahiru Musa. Sai kuma wani farar hula mai suna Jibrin da shi ma a lokacin sojojin suka harbe su tare.

SOJOJI KO ‘YAN SANDA: Wa ya fara buɗe wuta

A sanarwar da Kakakin Yada Labarai na Sojojin Najeriya, Sagir Musa ya fitar ranar Larabar makon jiya, ya bayyana cewa sojoji sun yi tsammanin masu garkuwa da mutane ne. Kuma an tsayar da su, amma suka ki tsayawa. Sannan kuma Sagir ya ce ‘yan sandan ne suka fara bude wa sojojin wuta.

Wasu shaidu guda biyu sun tabbatar wa PREMIUM TIMES cewa ‘yan sandan ba su bude wa sojoji wuta ba, kamar yadda su mahukuntan sojojin suka yi ikirari.

Amma kuma shaidun sun tabbatar wa wakilin PREMIUM TIMES cewa ‘yan sandan ba su tsaya a shingen sojojin ba.

An bindige ‘yan sandan kamar mita 100 daga inda shingen sojojin ya ke.

Yadda yaran Wadume Suka riƙa bin Ƴan sanda a baya tun daga Ibi

“Wato su yaran Wadume sun rika bin motar da ‘yan sanda suke ciki dauke da ogan su tun daga Ibi, bayan da suka kamo shi daure da ankwa.” Haka wata kwakkwarar majiya ta shaida wa PREMIUM TIMES, kuma majiyar ta ce a kan idon ta al’amarin da ya faru a Gidinwaya ya faru.

“Su yaran Wadume ne suka shaida wa sojojin da ke shingen bincike a nan Gidinwaya cewa farar mota bas da ke a gaban su, masu garkuwa da mutane ne suka sato Alhaji Hamisu Wadume. Dama kuma shi Hamisu Wadume din sojoji duk sun san shi farin sani, za su iya yin komai domin su kare lafiya ko ran sa.”

Majiyar ta ce daga nan ne sai sojojin suka shaida wa abokan aikin su da ke shingen kan hanya da ke daidai Gidinwaya cewa wato shinge na biyu, wadanda su din ne suka bi su, suka bindige su.

Majiyar PREMIUM TIMES ta shaida wa wakilinmu cewa farar hular da aka kashe mai suna Jibrin, wani magini ne, kuma ya ma san shi sosai. Ya ci gaba da yi wa wakilin mu karin bayanin cewa Jibrin ya na kwarmata wa ‘yan sanda masu kamo ‘yan garkuwa duk wani sirrin yadda za a kamo su.

Sannan kuma wannan majiya ta ci gaba da cewa shi Jibrin din ma yaran Hamisu Wadume sun taba kashe wani dan uwan sa.

DA DAN GARI A KAN CI GARI DA YAKI

Majiyar PREMIUM TIMES ta kara yin wani karin hasken cewa:

“To ni dai ban san dalilin da ya sa ‘yan sanda ba su tsaya a shingen sojoji ba domin a bincike su. Amma mai yiwuwa sun ki tsayawa ne saboda sun san dangantakar da ke tsakanin Hamisu wanda suka kama din da su sojojin, wanda hakan zai iya sa su kubutar da shi, su hana a tafi da shi. Saboda ya saba yi wa sojojin kyautar kudade sosai.”

Majiyar mu ta ce ta ma san daya daga cikin sojoji biyar din da suka kashe ‘yan sandan tare da Jibrin. Sai dai kuma majiyar ta ce ta yi amanna a zaton sojojin su ‘yan sandan masu garkuwa da mutane ne.

Akwai wasu mutane uku da PREMIUM TIMES ta kara zantawa da su, wadanda su ma suka hakkake cewa sojojin sun yi zaton masu garkuwa da mutane ne suka sato Hamisu Wadume za su gudu da shi. Saboda Hamisu dai mutum ne da sojojin suka sani sosai.

Kowane daga cikin su PREMIUM TIMES ta yi hira da shi ba tare da dayan ya san an tattauna da wancan ba.

Daya daga cikin majiyar PREMIUM TIMES ya tabbatar da cewa sojojin da ke shinge na biyu ne suka bi motar da ‘yan sandan ke ciki, suka rika harbin ta, har ta yi hatsari ta fadi.

“Yan sandan sun nemi fitowa su tsare, amma sai sojojin suka bude musu wuta, nan take biyu suka mutu. Shi ma Jibrin a nan ya mutu. Dan sanda na uku ya yi kokarin nuna musu katin shaidar aikin dan sanda, amma sai suka karasa kashe shi, duk kuwa da cewa sun gan shi sanye da falmara ta ‘yan sanda. Sauran ‘yan sandan kuma sun tsere, amma da harbin bindiga a jikin su, sun samu raunuka.”

JANGWANGWAMA: YADDA SOJOJI SUKA SAKI WADUME

Duk wannan kwatagwangwamar da ake yi, tuni gungun yaran Hamisu Wadume sun karaso wurin da aka harbe ‘yan sandan sun yi tsaye cikin ‘yan kallo.

“Gaba daya abin nan duk ya faru ne a cikin minti 20 kacal. Kuma duk wannan kwatagwangwama da ake tabkawa shi Hamisu Wadume ya na a kan titi zaune ya harde kafafun sa, amma daure da ankwa.

“Daga nan sai sojojin suka sa hannu suka rika ciro ‘ID card’ daga aljifan ‘yan sandan su na dubawa bayan sun kashe su kenan. amma duk da a haka sai suka rika cewa katin shaidar aikin wai na jabu ne.

NAKA SHI NE NAKA

“Daga nan sai sojojin suka rika cewa “mu tafi kawai, mu bar wurin. Sannan kuma suka rika surfa zagi su na cewa ai babu abin da ma gwamnati ke musu na kulawa, su na cewa su Wadume suka sani, domin shi ke kula da su, shi su ke cin moriyar sa.” Duk inji majiyar PREMIUM TIMES, wanda ya hakkake cewa a gaban sa aka yi komai.

“Daga nan sai sojojin suka kwance wa Wadume ankwa, suka ce ya kama gaban sa kawai, ya bar wurin. Da ido na na ga sojojin su biyar. Bayan sun cire masa ankwa, sai ya shiga wata bakar mota wadda yaran sa suka zo da ita, suka zaburi mota, suka juya suka koma hanyar Ibi.”

“Sojojin ba su ma boye abin da suka yi ba. A kan kwalta Ibi zuwa Wukari komai ya gudana. Har ma jinjina wa kan su da bajintar da suka yi suka rika yi. Ogan su ne ma mai suna Kaftin Usman ya zo ya shiga cikin su, ya karbi bindigogin ‘yan sandan yay i gaba da su.”

Wakilin PREMIUM TIMES ya gano cewa wannan jami’in soja mai suna Kaftin Usman, ya yi kaurin suna sosai a Ibi, Gidinwaya da Wukari. Duk inda ake maganar Hamisu Wadume, sai ka ji an jefo sunan sa a batun. An ce ya na alaka ta kut-da-kut tare da Hamisu Wadume.

HAMISU WADUME DA KAFTIN USMAN: ABOKIN DAMO GUZA

Wata majiyar PREMIUM TIMES ta kwatanta gogarman dan garkuwa da mutane Hamisu Wadume da Kaftin Usman cewa su biyun ‘abokan cin mushe, ba su boye wa juna wuka’.

“Komai tare su ke yi. Shi kan sa Sarkin Ibi, Aku Ibi ya na mu’amala da su. Sarkin Ibi na son sa, kowa na son sa. Wadume ya na ragargazar kudi tamkar gwamnati. Ya na biya wa mutane bukata, da warware musu matsalolin su. Na san mutane 11 da ya raba wa babura a kauyen Gidinwaya kadai.”

Majiyar mu ta yi ikirarin cewa basaraken Ibi da Kaftin Usman sun a bai wa Wadume goyon baya. Amma PREMIUM TIMES ba ta tantance wannan zargi ba.

Wasu rahotanni na nuna cewa Kaftin Usman ne ya bada umarnin a bindige sojojin. Amma dai majiyar mu da ta ce ta yi magana da abokin ta wanda soja ne a cikin wadanda sojoji biyar din da suka yi kisan, ya ce bai gamsu da wannan zargin ba.

“Duk da na san Kaftin Usman ba mutumin kwarai ba ne, na san dai abokin Wadume ne tabbas. Amma ba shi ne ya bada umarnin a kashe ‘yan sandan ba.

“Sojojin da ke shinge na farko ne suka shaida wa sojojin da ke shinge na biyu cewa ga wasu nan sun sato Wadume, don haka su tsaida su. Su kuma sojojin da ke shingen farko, yaran Wadume suka buga musu waya, su ka ce ga wasu nan sun sato Wadume.”

YADDA WADUME YA TSERE DAGA IBI

Majiya ta ce sai bayan da Bataliyar Sojoji ta 93 da ke Takum ta fahimci shirme da kasassabar da sojoji suka yi ne sannan ta tashi haikan neman yadda za su kama Wadume. Daga nan sai suka tare duk wata hanyar da ta shiga ko ta fita Ibi, har ta zuwa Wukari.

Amma majiya ta ce Hamisu Wadume ya fice daga Ibi tuni tun kafin ma sojoji su fara tare hanya. Ana jin ya fice ta cikin wuran Kogin Donga da Kogin Taraba daga Kogin Ibi. Daga nan ya shige ta Kuka cikin Jihar Filato.” Haka wata majiya ta shaida wa PREMIUM TIMES.

Sai dai kuma PREMIUM TIMES ta labarta wa Kakakin Sojoji, Sagir Musa wasu bayanai da ta gano a Wukari, Ibi da kuma Gidinwaya. Amma bai ce komai ba.

Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Taraba, Alkasim Sanusi da kakakin su David Misal na Rundunar Taraba, sun sanar da wakilinmu cewa akwai tsatstsauran gargadin cewa kada su kuskura su yi magana da ‘yan jarida tukunna.

WAIWAYE ADON TAFIYA

Idan ba a manta ba, cikin shekarar da ta gabata ne tsohon Babban Hafsan Sojojin Najeriya, T.Y Danjuma ya nuna damuwa dangane da kashe-kashen da ake yi a Jihar Taraba, har ya shawarci kowa ya tashi ya kare kan sa.

Baya cewa furucin da ya yi cewa jami’an tsaro ba su iya kare ai’ummar jihar, ya kuma yi zargin cewa wasu manyan laifukan da ake aikatawa a jihar da daurin gindin sojoji a ciki.

Wannan kakkausan zargi da ya yi dai ya janyo masa bakin jini a kasar nan, musamnan a Arewa, inda ake ganin kamar suka ce ya yi wa gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari.

Tags: AbujaHausaLabaraiPREMIUM TIMESTarabaWadume
Previous Post

EFCC ta kai farmaki gidan Ambode, tsohon gwamnan Legas

Next Post

BAKON DAURO: Yara sama da miliyan 26 na cikin hadarin kamuwa da cutar a Najeriya -NPHCDA

Mohammed Lere

Mohammed Lere

Next Post
Immunizations

BAKON DAURO: Yara sama da miliyan 26 na cikin hadarin kamuwa da cutar a Najeriya -NPHCDA

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • ‘Ruhun Mai Tsarki ne ya umarce ni na kashe ta’ – Inji matar da ta kashe ‘yar shekara biyar
  • RIGA MALAM MASALLACI: Matasan Kano sun yi wa ginin ƴan canji diran mikiya, sun yi warwason kayan ‘ganima’
  • HIMMA DAI MATA MANOMA: Rashin jari mai kauri ya sa noma na ya ƙi gaba, ya ƙi baya – Wata mace mai himma
  • CIRE TALLAFIN MAI: Kungiyoyin ma’aikatan lantarki, Ƴan jarida da na Kwadago za su tsunduma yajin aiki daga ranar Laraba
  • Yadda bashin Dala Miliyan 19.3 na Bankin Musulunci ya bunƙasa noma a ƙananan hukumomin Kano 44 – Hamisu, Kodinetan KSADP

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.