A yanzu haka jagoran mabiya Shi’a na Najeriya, Sheikh Ibrahim El-Zakzaky, ya bar hannun jami’an tsaro a Kaduna, ya na filin jirgin Abuja, a kan hanyar tafiyar sa neman magani zuwa Indiya.
Makusantan babban malamin sun shaida wa PRMIUM TIMES cewa ya isa filin jirgin Abuja a yau Litinin da rana.
Za a dauki malamin ne wani jirgin sama da aka yi shata daga Najeriya zuwa Indiya.
“Ina tabbatar muku cewa ya na a kan hanyar sa ta zuwa Indiya a yau Litinin din nan a wani jirgin da aka yi shata.’’ Haka wani makusancin malamin ya shaida wa PREMIUM TIMES.
Wannan tafiya ta taso ne mako daya bayan da Babbar Kotun Jihar Kaduna ta ba shi iznin tafiya neman magani a kasar Indiya domin neman magani.
Sai dai kuma PREMIUM TIMES HAUSA ba ta tabbatar da ko kotun Kaduna ta amince da shawarwarin da Gwamnatin Jihar Kaduna ta bayar ko ta nemi kotu ta kakaba wa E-Zakzaky wasu tsauraran ka’idoji ba ko a’a.
Kaduna ta nemi kotun ta kakaba wa malamin wasu sharudda kafin ta bar shi ya fice zuwa Indiya. Sharuddan sun hada da:
Sai Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya ta ga hujja daga Asibitin Medanta na Indiya, cewa lallai can din ne za a duba lafiyar su El-Zakzaky, kuma sai an tsara sharuddan amincewar su cewa da sharuddan tafiya neman magani a bisa tasarin diflomasiyya.
Masu tafiya neman maganin a tabbatar sun sa hannun amincewa cewa idan sun warke za su dawo Najeriya su ci gaba da fuskantar shari’ar da suke yi. Sannan kuma su da kan su ne za su dauki nauyin kudin tafiyar su da na dawowar su, kudin yi musu magani da kudin hidindimun zaman su a Indiya a tsawon lokacin da za su yi a can.
Dole su kawo masu belin da za su tsaya musu, mutum biyu wadanda za su iya gabatar da su a duk lokacin da aka neme su. Daya daga cikin masu belin ya kasance basarake ne mai daraja ta daya dan jihar Kaduna. Daya kuma ya kasance sananne ne a jihar Kaduna. Dukkan su biyu din su kasance su na da gida a cikin Jihar Kaduna.
Gwamnatin Najeriya ta samu tabbataci a rubuce daga Gwamnatin Indiya cewa idan su El-zakzaky sun nemi a ba su mafaka, to ba za ta bas u ba. Sannan kuma ta haramta musu gudanar da duk wasu aikace-aikacen da abin da ya kais u kasar ne su yi ba. Musamman abin da zai zama barazana ga Najeriya.
Su rubuta takardar amincewa ta hannun lauyoyin su cewa idan sun je Indiya ba za su yi wasu abubuwan da za su zama barazana ko cutarwa ga ci gaba da shari’ar su da ake yi ba, ko barazana ga tsaron kasar nan da kasar Indiya.
Jami’an tsaro daga Najeriya su raka su zuwa Indiya neman magani, kuma su kasance tare da su a iya tsawon lokacin da za su kasance a Indiya, har dawowar su Najeriya.
Sai Ofishin Jakadancin Najeriya da ke Indiya ya amince kuma ya tantance duk wani wanda zai kai musu ziyara a asibiti tukunna kafin a bari ya gana da su.
Yanzu dai hukuma ta amince zai tafi kenan.
Discussion about this post