• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Ba ni da ra’ayin takarar shugaban kasa, lokacin da aka zabe ni gwamnan Kaduna gashin kai na baki wul yanzu duk furfura – El-Rufai

    KALAMAN ƁATANCI GA ANNABI: Duk wanda ya yi zanga-zangar addini a Kaduna zai ɗanɗana kuɗar sa – Gargaɗin El-Rufa’i

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    Malami ya janye daga takarar gwamnan Kebbi duk da kurin da ya rika yi wai jama’a suka tilasta shi ya fito

    Chris Ngige

    Ngige ya janye takarar shugaban ƙasa, ya zaɓi ci gaba da zama ministan Buhari

    ZAƁEN 2023: APC za ta iya faɗuwa zaɓe idan ba ta tashi tsaye ba -Buhari

    ALAMOMIN WATSEWAR ƊAURIN TSINTSIYA A KANO: Mataimakin Kakakin Majalisa ya fice daga APC, ya koma PDP

    Ƴan Tiwita sun ce ba za su zaɓi Atiku ba saboda ya goge sakon yin tir da kisan Deborah da ta yi Ɓatanci ga Annabi

    Ƴan Tiwita sun ce ba za su zaɓi Atiku ba saboda ya goge sakon yin tir da kisan Deborah da ta yi Ɓatanci ga Annabi

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Ba ni da ra’ayin takarar shugaban kasa, lokacin da aka zabe ni gwamnan Kaduna gashin kai na baki wul yanzu duk furfura – El-Rufai

    KALAMAN ƁATANCI GA ANNABI: Duk wanda ya yi zanga-zangar addini a Kaduna zai ɗanɗana kuɗar sa – Gargaɗin El-Rufa’i

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    Malami ya janye daga takarar gwamnan Kebbi duk da kurin da ya rika yi wai jama’a suka tilasta shi ya fito

    Chris Ngige

    Ngige ya janye takarar shugaban ƙasa, ya zaɓi ci gaba da zama ministan Buhari

    ZAƁEN 2023: APC za ta iya faɗuwa zaɓe idan ba ta tashi tsaye ba -Buhari

    ALAMOMIN WATSEWAR ƊAURIN TSINTSIYA A KANO: Mataimakin Kakakin Majalisa ya fice daga APC, ya koma PDP

    Ƴan Tiwita sun ce ba za su zaɓi Atiku ba saboda ya goge sakon yin tir da kisan Deborah da ta yi Ɓatanci ga Annabi

    Ƴan Tiwita sun ce ba za su zaɓi Atiku ba saboda ya goge sakon yin tir da kisan Deborah da ta yi Ɓatanci ga Annabi

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

WASIKAR OBASANJO: Muhimman Abubuwa 11 Da ya Gargaɗi Buhari a kan su

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
July 15, 2019
in Babban Labari, Rahotanni
0
WASIKAR OBASANJO: Muhimman Abubuwa 11 Da ya Gargaɗi Buhari a kan su

Tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo, ya sake rubuta wa Shugaba Muhammadu Buhari wasiƙa, inda a wannan karon ya gargaɗe shi cewa Najeriya ta kama hanyar shiga bala’in ‘katilan-makatulan’, kuma Buhari ɗin ne kaɗai zai iya hana ƙasar faɗawa cikin wannan mummunan bala’i.

Obasanjo ya ce kashe-kashe da rikice-rikice na ci gaba da zame wa Najeriya bala’i, ga kuma babbar matsalar yadda ƙabilanci ya ruruta wuta tun bayan hawan Buhari mulki, shekaru huɗu da suka gabata.

Obasanjo ya ce an shafe shekaru masu yawan gaske rabon da Najeriya ta samu kan ta cikin irin wannan masifa da ake fama da ita.

Idan ba a manta ba, cikin wasiƙar da ya rubuta masa, ya shaida wa duniya cewa Najeriya fa ta kamo hanyar afkawa cikin kashe-kashen da idan ba a yi da gaske ba, to zai yi wuya a iya kashe gobarar.

Muhimman Saƙonni 10 da Wasiƙar Obasanjo Ta Ƙunsa

1 – Rugujewar Haɗin kan Kasar nan

Zan yi magana ne dangane da halin ko-a-mutu-ko-a-yi-rai da mu ke ciki, wanda ya shafi kasar mu baki ɗaya. Wannan matsala an bar ta ta na ta kara ruruwa, har ta ci karfin ginshikan da suke rike da wannan kasa tun lokacin da aka kafa ta. Tuni tubulan da suka gina hadin kan kasar nan an fara ruguza su.

Na shiga damuwa da tsoro sosai ganin cewa a yanzu tura ta kusa kaiwa bango, mun kusa kaiwa inda ba za mu iya jan linzami mu tsaida bala’in da ka iya tunkarar kasar nan ba.

Dole ne na nuna damuwa ta, domin a matsayi nan a dan Najeriya, a yanzu haka da tabon raunin Yakin Basasa Zan mutu a jiki na. Haka shi ma da na da tabon raunin yakin Boko Haram zai mutu a jikin sa.

2 – Yanke Ƙaunar Samun Tsaro Daga Gwamnati

Idan fa jama’a ta yanke kauna daga tunanin samun tsaro daga gwamnati, to sai su bi duk wata hanyar da su ke ganin cewa ita ce mafitar nemar wa kan su tsaro. Ko dai mutum ya nemi tsare kan sa ko ta halin kaka, ko kuma gungun jama’a su nemi hanyar tsare kan su ko ta wace hanya. Kowa sai ya nemi ta sa da za ta iya fisshe shi kenan.

3 – Ƙaryar An Kakkaɓe Boko Haram

Sama da shekaru goma kenan ana fama da Boko Haram. A cikin shekarun nan goma kuwa, hudu a cikin gwamnatin ka aka shafe su. A kullum Boko Haram sai ta’asa su ke yi, duk kuwa da ƙaryar da gwamnatin ka ke ta kantarawa cewa an gama da Boko Haram.

Kalaman da Babban Hafsan Hafsoshin Najeriya ya yi kwanan nan, inda yayi korafin cewa sojoji ba su da kuzari ko kishin yaki da Boko Haram, wata magana ce da amsa kan ta da kan ta dangane da halin da ake ciki a kan Boko Haram.

Duk ma abin da ka ga dama ka je ka ci gaba da fada wa mutane, amma dai kowa ya sani cewa Boko Haram na nan daram, kuma a kullum su na kashe mutane, su na sace mutane da yin garkuwa da su, su yi fyaɗe, kuma su na kama mutane a matsayin bayi su na sayarwa. Wasu kuma su na tilasta su shiga harkar Boko Haram, ta hanyar ɗana musu bam domin su shiga cikin jama’a su na tarwatsa su.

Sannan ina tabbatar maka da sanda da duka kadai ba za a iya korar Boko Haram ba. Saboda ta yaya za ka iya kakkaɓe Boko Haram a Arewa alhali kashi 50 bisa 100 na yankin Arewa maso Gabas ba su da ilmi? Ta yaya za ka kakkaɓe Boko Haram alhali kashi 70 bisa 100 na yankin ba su da aikin yi?

4 – Hargitsewar Rikicewar Makiyaya da Manoma

Rikicin makiyaya da manoma da aka ƙi dauka da muhimmancin magance shi, a yanzu ya yi muni kwarai. Ya tashi daga rikici ya koma hare-hare, samame, garkuwa da mutane da kuma sace su, fashi da makami, kashe-kashe duk faɗin kasar nan.

Babban abin takaicin shi ne yadda wannan ɓarna da ake tafkawa ake mata kallon cewa Fulani ne ke yin ta tare da daurin gindin Fulani manyan kasar nan a yankuna daban-daban.

Karin abin bakin ciki kuma shi ne yadda ‘yan Najeriya da dama da ma wadanda ba ‘yan Najeriya ba ke kallon cewa kai ne aka dora wa dukkan laifin abin da ake aikatawa, a matsayin ka na Bafulatani. Wani lokaci dai hasashe kan zama gaskiya.

5 – Fulani Su Fito Su Faɗi Ƙorafinsu A Zauna a Duba

Akwai bukatar Fulani su fito su fadi dukkan korafe-korafen da suke da shi. Idan su na da hujja, sai a zauna a shawo kan matsalar. Idan akwai wasu kabilu masu wani korafi, su ma su fito su bayyana na su. Sai a zauna a baje komai a kan tebur a nemi maslaha.

6 – Lokaci na Neman Ƙurewa

Bai kamata a riƙa yi wa komai riƙon-sakainar-kashi ba. saboda lokaci na ƙurewa, ko’ina a faɗin kasar nan ba ka jin komai sai koke-kore da korafe-korafen rashin gamsuwa da halin da kasar ke ciki.

Fadar Gwamnatin Amurka da Majalisar kasar sun yi mana hannun ka-mai-sanda cewa ya kamata su kimtsa gidan su kafin ya ruguje. Haka ita ma Majalisar Ingila ta shaida mana.

Ya zama dole su dubi maganganun da suke faɗa mana kuma mu yi tunanin abin da ka iya tasowa ta yadda za mu maida hankali da irin wadannan shawarwari.

7 – Kalaman Ƙiyayya Tamkar Gobarar Daji ce

Idan aka yi turnuku fa ba ka da mai iya tsaida kalaman ƙiyayya da barkewar mummunan rikici. Kalaman ƙiyayya na ƙabilanci wutar ƙaiƙayi ce. Za ta riƙa ruruwa daga ƙasa, a ƙarshe sai ta wo sama ta na ci, ta yadda babu mai iya kashe ta, har sai ta kai ga yin mummunar barna. Idan kunne ya ji, to jiki ya tsira.

Tun bayan kashe Ƴar Shugaban Ƙungiyar Afenifere, kusan sauran yankunan ƙasar nan sun harzuka, su na cewa abin ya ishe su haka nan fa!

Duk lokacin da aka ci gaba da rashin maida hankali ga masu koke-koke, to ƙasar nan ce za ta ji a jikin ta. Ni dai ina sanar da kai Shugaban Kasa kuma Babban Kwamandan Askarawan Najeriya cewa na damu kwarai da wadannan munanan bala’o’i wadanda za a iya kauce musu:

8 – Sakin ragama da akalar Najeriya a hannun ‘yan bindiga wadanda jama’a ke zargin cewa Fulani ne, sai kuma Boko Haram.

9 – Tsoron kada bala’in kashe-kashen ramuwar gayya ya ɓarke a kan Fulani, ta yadda za mu fada irin balbalin bala’in da kasar Rwanda ta taba samun kan ta a ciki. Babu wanda ya taba amanna cewa hakan za ta iya faruwa a Riwanda, amma ga shi kuma hakan ta faru.

10 – Tsoron kada irin wannan kashe-kashen ya koma a kan sauran wasu ƙabilun kasar nan tsakanin su da wasu ƙabilu. Hakan na iya faruwa ta hanyar watsa ji-ta-ji-ta, fargaba, tsoro, barazana da kuma kisan daukar fansa da ka iya ɓarkewa zuwa kisan kiyashi

11 – Fargabar ɓarkewar yamutsi daga wani sashe na ƙasar nan da ka iya watsuwa zuwa sauran sassan ƙasar nan cikin ƙanƙanin lokaci, wanda a ƙarshe zai iya kai ga raba ƙasar nan.

Saboda haka ya faru a Yugoslavia ba da dadewa sosai ba. Idan ba mu tashi tsaye ba, to ɗaya ko duka daga cikin waɗannan bala’o’in ka iya faruwa. Dole mu tashi da addu’a tare da daukar matakin da ya dace a lokaci guda.

Wannan yunƙuri kuwa Shugaban Ƙasa ne zai iya fara yin sa. Amma kuma ba zai iya cin nasara shi kaɗai ba, sai ya samu mataimaka. Masu iya magana na cewa idan ka na cikin washin addar ka, sai mahaukaci ya biyo ta bayan ka, ya fizge wukar daga hannun ka, to ka na bukatar taimakon jama’a da za su hadu domin a karɓe addar a hannun mahaukaci, ba tare da an ji wa wani rauni ba.

Tags: BuhariHausaLabariNajeriyaNewsObasanjo
Previous Post

HAJJI 2019: An kwashi Alhazan farko 1,529 daga jihohin Kaduna,Kano da Legas zuwa Saudiyya – NAHCON

Next Post

HAJJIN BANA: Aƙalla Alhazai 6,856 suka sauka garin Madina daga Najeriya

Next Post
Nigerian Pilgrims Hajj

HAJJIN BANA: Aƙalla Alhazai 6,856 suka sauka garin Madina daga Najeriya

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar
  • UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara
  • RAHOTON MUSAMMAN: Atiku Bagudu Da Mohammed Abacha: Manyan ‘Yan Kamashon Da Su Ka Taya Abacha Lodi Da Jigilar Dala Miliyan 23 Ɗin Da Gwamnatin Birtaniya Ta Ƙwato Kwanan nan
  • Akalla mutum 32 ne ‘yan bindiga suka kashe daga ranar 8 zuwa 14 ga Mayu a Najeriya
  • ‘ƳAN BINDIGA SUN DIRA KANO: Mahara sun yi garkuwa da dakgcen Karfi sun kashe wasu mutum 7

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.