• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

SABBIN MINISTOCI: Shin Buhari ya zabi wadanda ya sani ne ko kuma wadanda aka sani ne?

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
July 24, 2019
in Rahotanni
0
Buhari Ministers

Buhari Ministers

Tun daga lokacin da Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmed Lawan ya karanta jerin sunayen sabbin ministocin da Shugaba Muhammadu Buhari ya tura majalisa domin amincewa, al’ummar kasar nan suka maida hankulan su a kan jerin sunayen na mutane 43.

PREMIUM TIMES HAUSA ta kalato ‘kabli-da-ba’adin’ da suka cukurkude sunayen wadanda majalisa za ta fara tantancewa a yau Laraba.

1 – RASHIN CIKA WA MATASA ALKAWARIN NADA SU MINISTOCI

Ranar 21 Ga Janairu, Daraktan Kamfen na Matasan APC mai suna Tony Nwoye, ya shaida a wani taro cewa sun gana da Shugaba Muhammadu Buhari, kuma yay i musu alkawarin cewa a wannan zango zai nada matasa ministoci a cikin ministocin sa. Sai dai kuma yayin da sunayen suka fito, babu ko daya daga cikin matasan da suka yi wa APC fafutikar kamfen din zaben 2019 ko daya.

Isa Pantami ne mafi karancin shekaru 47 a cikin ministocin. Shi kuma ba ya cikin gurguzun matasan da suka taya Buhari jekal-jekalar kamfen tsawon shekaru da shekaru.

Mai bi masa a karancin shekaru 49, shi ne Festus Keyamo, wanda lauyan EFCC ne, daga baya kuma ya rikide ya koma tantarin dan siyasar kare akidar Buhariya. Kuma shi ne daraktan yada labarai na kamfen din Buhari a zaben 2019.

‘Yan wasan fina-fainan Hausa sun yi ta watsa bayanan cewa sun a sa ran za a ba fitaccen dan fim din nan Ali Nuhu mukamin ministan wasanni da matasa.

Ko a ranar da aka bayyana sunayen ministocin, sai da ka ga wasu ‘yan wasan sun je majalisa, sun a nuna goyon bayan su cewa a nada Ali Nuhu Minista.

2 – RASHIN SUNAN KABILUN YANKIN ABUJA NA NEMAN TAYAR DA KURA

Al’ummar asalin yankin Abuja da kewaye sun yi fatali da jerin sunayen ministocin da Shugaba Buhari ya fitar, a bisa dalilin cewa babu dan kabilar su ko daya a cikin sunayen. Wata sanarwar da Kakakin Yada Labarai na Hadaddiyar Kungiyar Kabilun Abuja, Sumner Shagari-Sambo ya sa wa hannu a jiya Talata bayan fitar da jerin sunayen ministoci, ta ce sun gaji da zalunci da kuma danniyar da ake wa kalibun yankin Abuja.

Sun yi korafin yadda ake kwace musu kasasr su ta gado, ana bai wa wasu suna kantama-kantaman gine-gine ana kara mamaye su. Sannan kuma sun ce ba a taba nada dan asalin kabilar Abuja ministan Abuja ba.

Sun ce a yau za su dora wa Sanata Philips Aduda da ke wakiltar su, ya tashi a gaban majalisa ya nuna rashin amincewa da saka dan kabilar Abuja a cikin ministoci.

3 – ZARGIN NADA WADANDA APC TA YI WA ‘WANKAN TSARKI’

Jama’a da dama sun yi mamakin nada wasu da ake ganin cewa sun koma APC ne a lokacin da EFCC ke binciken su. Sannan kuma daga bisani kamar Timipre Sylva tsohon gwamnan Jihar Bayelsa, sai da ya koma APC aka kori karar sa, sannan kuma aka maida masa da gidajen da aka kama.

Godswill Akpabio ya koma APC a lokacin da EFCC ke neman sama da naira bilyan 100 a hannun sa. Ya tsaya takarar sanata amma ya fadi. Yanzu an nada shi minista, kuma babu wata kotu da ta wanke shi. Wanda hakan ya jefa jama’a tunanin cewa ko dai mulkin Buhari ya yi adabo da akidar yaki da cin hanci da rashawa.

4 – NEMAN BAMBANCIN MAGE DA KYANWA

Makonni biyu da suka gabata, Buhari ya ce akasarin wadanda ya nada ministoci duk bai san sub a, ‘yan alfarma ne kawai. Amma a yanzu sai ya darje a cikin wadanda ya sani gar-da-gar. Kuma sai wadanda ya tabbatar da nagartar su.

Wannan ya sa jama’a na al’ajabin cewa shin irin su Silva da Akpabio ne ya sani gar-da-gar, kuma mutane nagari da ya tabbatar da nagartar su din kenan?

5 – NADA MAI HARKALLAR DABINON SAUDIYYA MINISTA

An cika da mamakin anin sunan Sadiya Faruk daga Jihar Zamfara ya sa jama’a da dama sun tuna da harkallar cinye tulin dabinon da kasar Saudiyya ta bai wa Najeriya tallafi a lokacin azumin bara, da niyyar raba wa jama’a, musamman a mazauna sansanin masu gudun hijira a lokacin shan ruwa.

6 – HADA KEYAMO DA SLYVA A WURI DAYA

Bayyana sunan babban lauya Festus Keyamo a cikin jerin ministoci, ya sa wasu da dama na gwasale gwamnatin Buhari. Idan ba a manta ba, Keyamo ne lauyan da EFCC ta dauka, ya gurfanar da Timipre Silva a kotu, akan zargin wawurar bilyoyin kudade. Ya yi ta kokarin nuna wa kotu irin gagarimar satar da y ace Sylva ya yi tare da gidajen da ya mallaka.

Bayan Sylva ya koma APC daga PDP, sai Keyamo ya fito ya ce ya tsame hannun sa daga gurfanar da Sylva, saboda wasu mishkilolin da ya ke fuskanta da wasu uzurorin da suka hana shi ci gaba da aikin.

Ba a dade ba kuma sai aka wanke Sylva ta hanyar maida masa da gidajen sa da EFCC ta kwace.

A yau Silva da Keyamo duk ministoci ne, za su rika zama a kan teburi daya ana gudanar da ayyuka, a matsayin sun a ministoci nagari da Buhari y ace zai darje kafin ya nada.

7 – RASHIN DAWO DA WASU MINISTOCIN KAN MUKAMAN SU

Jama’a da dama sun yi farin ciki jin cewa Buhari bai sake nada wasu ministoci da dam aba. Cikin wadanda aka yi murnar rashin sake komawar sa akwai Mansur Dan-Ali tsohon ministan tsaro.

A zamanin sa rashin tsaro yay i muni a jihar sa, wato Zamfara. Cikin kananan hukumomin da kashe-kashe suka yi kamari, har da Birnin Magaji, inda nan ne aka haife shi.

Sai kuma tsohon ministan ayyukan gona Audu Ogbeh, wanda sau da yawa an fi kuka da shi wajen yawan shekaru da kuma tsufa. Majiya mai tushe ta tabbatar da cewa wasu lokuta idan zai hau bene sai an rike shi, don kada yay i tangal-tangal ya fadi, ko ya rikito kasa.

Shi ma Abdur-Rahman Dambazau an sha yin kuka da shi cewa a matsayin san a ministan harkokin cikin gida, muggan makamai sun shigo cikin kasar nan, wanda mallakar su ta kara haifar da hare-hare da kashe-kashe sosai musamman Arewa.

Tsohon Ministan Harkokin Lafiya, Isaac Adewale ma ba a ji haushin kin nada shi da Buhari ya yi ba.

Duk da kusancin da ake ganin Solomon Dalung na da shi ga Shugaba Muhammadu Buhari, hakan bai sa an maida shi a matsayin minista ba.

Ana ganin daga cikin dalilan har da wata dala dubu 13, 000 da ya kasa maida wa Hukumar Kwallon Kafa ta Kasa.

8 – TULIN TSOFFIN ’YAN ALEWA A CIKIN MINISTOCIN BUHARI

A cikin ministocin da Buhari ya bada sunayen su, akwai tsoffin gwamnoni har guda 9 da kuma tsoffin sanatoci su bakwai. Sannan kuma akwai wadanda suka taba yin wakilci a Majalisar Tarayya na zango daya ko sama da haka.

9 – KORAFIN RASHIN YIN RABA DAIDAI

Dokar Najeriya ta ce shugaban kasa zai zabi ministocin sa daya daga kowace jiha a cikin jihohin kasar nan. A baya ministocin sa 36 ne. A yanzu kuma 43.

Maimakon a ce an kara minista daya daga kowace shiyya, sai a ka kara ministoci biyu a Shiyyar Arewa maso Yamma. Wato aka zabo minista biyu a Jihar Kano da kuma Jihar Kaduna, wadanda a shiyya daya suke.

Hakan ya sa wasu na ta korafin cewa an yi wa yankunan su rashin adalci.

Tags: AbujaAkumeBayelsaBuhariEFCCFarukFestus KeyamoGeorgeGodswill AkpabioHausaLabaraiMinistociNewsPREMIUM TIMESSylver
Previous Post

Yadda tayoyin jirgin ‘Air Peace’ suka farfashe yayin sauka filin jirgin Legas

Next Post

Gara da zago suka cinye min satifiket din makaranta – Cif Joji Tanko

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Justice Tanko

Gara da zago suka cinye min satifiket din makaranta - Cif Joji Tanko

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki
  • TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna
  • Gwamnatin Kano ta hana lika fastoci a ginegine a fadin jihar
  • Sojoji sun kashe ‘yan ta’adda 58, sun kama wasu 161 a cikin makonni biyu a yankin Arewacin Najeriya
  • Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.