• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba  sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad

    An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad

    An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed

    An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba  sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad

    An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad

    An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed

    An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Masarautu Da Masarautar Kano: Ta Allah Ba Taku Ba! Daga, Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
July 1, 2019
in Ra'ayi
0
Jibanta cutar Sankarau cewa hukuncin Allah ne da Yari yayi bai yi daidai da karantawar Musulunci ba – Inji Sarkin Kano

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jin Kai

Assalamu Alaikum

Ya ku jama’ah! Yana da kyau da matukar muhimmaci mu fahimci asalin Sarauta, masarautun mu da Sarakunan mu na Musulunci na kasar Hausa. Domin fahimtar su da sanin su za ya sa mu san matsayin su a cikin al’ummah, wannan sai yasa mu girmama su, kuma mu san darajar su.

Su dai wadannan masarautu namu da dukkanin tsare-tsaren su, ya kamata mu san cewa ba turawa bane ko mulkin mallaka ko mulkin soja ko tsarin dimokradiyyah ya samar da su a Nijeriya.

Imam Murtada Gusau
Imam Murtada Gusau

Masarautun sun girme wa dukkan wadancan tsare-tsaren da na ambata. Kuma wadannan masarautu tsari ne na Musulunci ya samar da su, sanadiyyar gwagwarmayar Musulunci domin tabbatar da Shari’a da ya faro tun daga shekarar 1804, wadda ita ce ta samar da Cibiyar Daular Usumaniyyah, mai dauke da Masarautu 33 kamar yadda masana tarihi suka shaida muna. Shehu Usman Dan Fodio, a matsayin sa na babban malami, mujahidi, shine ya jagoranci sauran malamai da dalibai a wannan gwagwarmaya, aka yi jihadi, da Allah ya basu nasara sai aka tabbatar da wadannan masarautu, wanda shi Shehu shine Amirul Mu’minina ko Sarkin Musulmi. Shine ya bai wa wadannan Sarakuna tuta suka zama Amirai, wato shugabannin Musulunci a masarautun su, shi kuwa shugaba wato Shehu, yana Birnin Sakkwato. Haka fa wadannan masarautu da sarakuna bayin Allah suka ci gaba da gudanar da sha’anin Musulunci da warware matsalolin al’ummah har zuwa yau da nike wannan rubutu. Bisa la’akari da ilimin tarihi, za mu ga cewa wadannan masarautu an samar da su ne tun shekaru dari kafin turawa suyi wa Nijeriya mulkin Mallaka.

Wadannan masarautu namu na Musulunci, masu daraja, tun lokacin da aka kirkiri kasar Nijeriya suke ta shan wahala, suke ganin wulakanci da musgunawa a wurin makiya Musulunci da Musulmai, wato turawan mulkin mallaka, da ‘yan koren su daga cikin wasu sojoji da ‘yan siyasa. Saboda haka, maganar rarraba masarautar Kano da tsatstsaga ta da Gwamnatin Ganduje ta yi a yau, wanda kuma In Shaa Allahu, mun san cewa sai an rusa su, kawai ci gaba ne da wancan aiki na makiya Musulunci da Musulmai, da kuma rarraba kan jama’ah da kokarin haifar da husuma, adawa da gaba tsakanin al’ummah; kuma wannan yunkuri ne na rusa tsarin dukkanin masarautu a Kano da kuma ko’ina a arewacin Nijeriya.

Ya ku jama’ar Musulmi! Wannan kadan kenan game da bayani akan asalin wadannan masarautu namu. Kuma rashin sanin wannan ko jahiltar wannan ko kuma son zuciyar mu shine yake sa kaga Musulmi Dan arewa, abun mamaki, wai yana kokarin cin mutuncin masarautun mu, ko kuma ka ga mutum Musulmi Dan arewa, wai yana goyon bayan wani Dan siyasa domin tozartawa tare da cin mutuncin wani Sarki daga cikin sarakunan mu na Musulunci.

Kamar yadda na ga wasu shedanun ‘yan siyasa da magoya bayan su, suke kokarin yin batanci ga Mai Martaba Sarkin Kano, Malam Muhammadu Sanusi II, akan yayi kokarin ya bayar da shawarwari masu amfani ga gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari, a wurin taron da ofishin Babban Akawun Tarayyar Nijeriya ya shirya a Birnin Kano. A wurin wannan taro, shawarwari Mai Martaba Sarki ya bayar, a matsayin sa na masanin tattalin arziki, ya yabawa gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari a inda ta kyautata, ya bata shawara a inda ya kamata tayi gyara.

Amma sai miyagun mutane, shedanu, masu kokarin haddasa husuma da fitina tsakanin shugabanni, domin cimma wani buri na su, suka yi kokarin juya wadannan jawabai na Mai Martaba, a matsayin wai yana attacking gwamnati ne.

Alhali duk mutum mai ilimi, mai basira, idan ya kalli jawabin Sarki ko ya karanta shi, za ya ga cewa wallahi babu inda Sarki yayi attacking shugaba Muhammadu Buhari ko gwamnatin sa.

Jaridu irin su The Nation da sauran kafafen yada labarai na yanar gizo, da sauran kafafen yada labarai na zamani duk sun ruwaito cewa wai, Mai Martaba Sarki yana cewa, “KASAR NIJERIYA NA DAB DA DURKUSHEWA” wato NIGERIA ON THE VERGE OF BANKRUPTCY”, wanda wannan kawai sharri ne da kage da karya ga wannan bawan Allah, wato Mai Martaba Sarkin Kano, Malam Muhammadu Sanusi II.

Bayan wannan sharri da makarkashiya na kokarin canza kalaman Sarki ya wuce, wanda munafukai da makirai da magauta basu ci nasara ba, sai kuma kwatsam muka ga miyagu, ciki har da jam’iyyar APC ta Jahar Kano, da masu yi masu kamfen a kafafen yada labarai na zamani, irin Facebook, WhatsApp da sauransu, suna ta yada hoton Mai Martaba Sarki tare da ‘yar sa Husnah Sanusi, wadda Sarki ya halarci bikin yayen ta a makarantar su da ke Birnin Ikko, wato Legas, tare da rakiyar Damburan, Alhaji Munir Sanusi (Shugaban ma’aikatan fadar Kano).

Da yake mu a nan Nijeriya muna da saura a wayewa da ilimi, wai yau an wayi gari mutum ya nuna wa ‘yar sa da ya haifa soyayya da kauna ta hanyar kara mata karfin gwiwa a karatun ta, ya zama wani abun tsegumi, abun surutu, abun cece-kuce da hayaniya! Wai jahilcin mu har yasa wasu suna ganin bai kamata Mai Martaba Sarki yayi haka da ‘yar sa da ya haifa ba!

To ku sani, babu wani laifi da Sarki yayi a nan. Mai Martaba yayi daidai, domin zamani ne yazo da haka, kuma Musulunci baya fada da abun da zamani ya kawo, matukar abun nan bai sabawa Musulunci ba. Idan Sarki yabi zamani bai yi laifi ba!

Idan ku baku jawo ‘ya ‘yan ku a jika, idan ku baku nunawa ‘ya ‘yan ku kauna da soyayya shike nan sai kuyi ta zama a haka, amma kar ku zama kidahumai, wawaye, ku sa wa wani ido idan kun ga yayi hakan!

Sannan daga karshe, abun da nike so mu fahimta a wannan makala tawa shine, rashin sanin muhimmacin masarautun mu shi yasa da wani Sarki daga cikin Sarakunan mu yayi wani abu sai kaji ana ta kokarin cin mutuncin sa da nuna masa raini. Sannan abun mamaki, Sarakunan nan fa ya kamata mu fahimci cewa, su ba ma’asumai bane, wato ba Annabawa bane, kuma su ba Mala’iku bane. Mutane ne kamar kowa, amma sai dai banbancin mu da su, su shugabannin ne da Addinin Musulunci ya wajabta muna yin biyayya gare su. Dole ne muyi masu da’a, sai fa idan sun umurce mu da aikata abun da yake ya sabawa Allah da Manzon sa!

Saboda haka kar mu dauka cewa su ma’asumai ne basu yin laifi, sai wannan yasa mu sa masu ido a cikin al’amurran su. Da sun yi abu kadan muyi ta yayata shi muna kokarin raina su!

Allah ya taimake mu, yasa mu dace, amin.

Dan uwanku,

Imam Murtadha Muhammad Gusau, daga Okene, Jahar Kogi, Nijeriya. Za’a iya samun sa a adireshi kamar haka: gusaumurtada@gmail.com ko kuma +2348038289761.

Tags: AbujaHausaKanoLabaraiNajeriyaPREMIUM TIMESSarki SanusiSarkin
Previous Post

Za a iya tuhumar maigidan da yi wa matarsa fyade – Masu Karatu

Next Post

Yadda Fastoci, Malamai, Alfa-Alfa ke cin zarafin mabiyan su da sunan addini

Next Post
Yadda Fastoci, Malamai, Alfa-Alfa ke cin zarafin mabiyan su da sunan addini

Yadda Fastoci, Malamai, Alfa-Alfa ke cin zarafin mabiyan su da sunan addini

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • TURA TA KAI BANGO: Dalilin da ya sa dole na hakura da takarar sanatan Kebbi – Aliero
  • ZARGIN HARƘALLAR NAIRA BILIYAN 98: Bincike ba kaina farau ba, kuma kotun koli wanke ni ta yi – Amaechi
  • An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • El-Rufai ya lashe Zaben fidda gwani na kujerar majalisar tarayya, zai gwabza da Samaila Suleiman
  • An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.