Babban kotun shari’a da ke Abuja ta ba gwamnatin Najeriya dama ta haramta kungiyar Shiite a kasarnan.
Mai shari’a Nkeonye Maha na babban Kotun Abuja ya bayyana a takarda cewa daga yanzu kada wani ya bayyana kansa a matsayin dan Shi’a a kasarnan.
Sannan kuma ya bayyana cewa Antoni Janar din Kasa zai saka wannan takarda a jaridun kasar nan har guda biyu kafin a kaddamar sannan gwamnati ta tabbatar da haka a dokar kasa wanda shugaban kasa zai rattaba hannu a kai.
Idan ba a manta ba PREMIUM TIMES ta ruwaito labarin shirin gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari na bayyana ƙungiyar IMN, wato Shi’a a matsayin haramtacciyar ƙungiya a ƙasarnan.
Hakan ya biyo bayan bayanan kud-da-kud ne da PREMIUM TIMES ta jiyo daga majiya masu ƙarfi.
Rahoton ya bayyana cewa babban dalilin da ya sa Buhari zai tabbatar da haka kuwa shine ganin irin yadda ƴan shi’a suka canja salon zanga-zangar, ya koma hare-hare da arangama da suke yi da ƴan sanda da har sai anyi jina-jina a duk lokacin da suka fito.
Buhari ya tausaya wa ƴan sanda ganin cewa abin na neman yafi ƙarfinsu kuma ba za a iya tura sojoji ba domin abin bai kai a shigo da su ba.
Tun bayan arangamar da ƴan sandan suka yi da ƴan shi’a masu zanga-zanga shugaba Buhari ya shiga ganawar gaggawa da jami’an tsaro domin sanin abinda za a yi a kai cikin gaggawa.
Arangamar ƴan sandan da masu zanga-zanga, ƴan Shi’a yayi sanadiyyar rayukan mataimakin kwamishinan ƴan sanda Usman Umar da kuma wani matashi mai aikin bautan ƙasa dake tare da gidan talabijin din Channels.
Sannan su kan su ƴan shi’an sun bayyana cewa sun rasa mabiya shida a wannan artabu da akayi da ƴan sanda.
Gidan talabijin ɗinne ta sanar da haka inda tace duk da an garzaya da matashin asibiti cikin gaggawa, ashe lokaci yayi, ya cika.
Tuni ma har an binne shi a Kaduna a cikin wannan mako.
Idan Buhari ya saka hannu a wannan doka, wannan ƙungiya ya zama haramtacce kenan a kasar nan.
Dama can Buhari ya bayyana ƙungiyar IPOB a matsayin haramtaccen ƙungiya sai kuma gashi yanzu idan har an tabbatar da hakan, ƙungiyar IMN zai zama na biyu kenan.
Discussion about this post