Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo yayi kira ga ‘yan Najeriya dake zama a kasashen waje da suyi watsi da yawa-yawan cewa da ake yi wai garkuwa da mutane ya addabi mutanen Najeriya.
Osinbajo da yake tattaunawa da ‘yan Najeriya a birnin New York na kasar Amurka ya ce babu gaskiya a wannan magangani da ake yi, ” Abin duk siyasa ce kawai ba kamar yadda kuke ji a kafafen yada labarai ba”.
” Eh kwarai ana samun burbudin garkuwa da mutane jifa-jifa amma ba wannan ne farau ba. Bari ma kuji duk rahotanni da labaran da kuke ji a kafafen yada labarai wai an sace wancan, anyi garkuwa da wancan duk ba gaskiya bane, siyasa ce kawai kuji in gaya muku.
” Akwai wanda za aka ji wai anyi garkuwa da su, amma dai wasu labaran da zaka ji, kai ma kasan zuki ta malle ne, ba haka bane. Sannan a duk lokacin da aka kawo labarin wai an yi garkuwa da wani sai munyi bincike sosai, amma daga karshe sai mugano ashe hira ce ta mutane ba gaskiya bane.
Ya ce gwamnati na iya kokarinta wajen ganin an shawo ko kuma an kawo karshen matsalolin tsaro a Najeriya.
Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ne ya wallafa kalaman Osinbajo a shafin sa.
Discussion about this post