• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa

    Jami’an Kwastam sun kama haramtattun kaya na miliyoyin naira a Katsina

    Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kaya na naira biliyan 6.6 a jihar Ogun

    American University of Nigeria Student -Crt- Google

    Malaman jami’o’i na roƙon a biya su albashin wata da watannin da aka riƙe masu

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    Kotu ta yanke wa mahaifin da ya yi shekara 9 yana lalata da ƴa’ƴan sa mata biyu

    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Ƴan sanda sun kama magidancin da ya yi wa matar makwabcinsa fyade

    ABUJA: Kotu ta daure wasu ‘yan mata biyu saboda yawon gulmace-gulmace a unguwa

    Kotu ta tsare matar da aka kama tana madigo da ‘yar shekara 8 a Kaduna

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    ‘Yan sanda sun kama tsohon da ya yi wa ‘yar shekara hudu fyade a Katsina

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa

    Jami’an Kwastam sun kama haramtattun kaya na miliyoyin naira a Katsina

    Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kaya na naira biliyan 6.6 a jihar Ogun

    American University of Nigeria Student -Crt- Google

    Malaman jami’o’i na roƙon a biya su albashin wata da watannin da aka riƙe masu

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    Kotu ta yanke wa mahaifin da ya yi shekara 9 yana lalata da ƴa’ƴan sa mata biyu

    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Ƴan sanda sun kama magidancin da ya yi wa matar makwabcinsa fyade

    ABUJA: Kotu ta daure wasu ‘yan mata biyu saboda yawon gulmace-gulmace a unguwa

    Kotu ta tsare matar da aka kama tana madigo da ‘yar shekara 8 a Kaduna

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    ‘Yan sanda sun kama tsohon da ya yi wa ‘yar shekara hudu fyade a Katsina

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Gangamin Kalubalantar Ganduje! Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
May 16, 2019
in Ra'ayi
0
Imam Murtada Gusau

Imam Murtada Gusau

Gangamin Kalubalantar Ganduje Gandun Sharri! Daga Imam Murtadha Gusau

Laraba, Ramadan 10, 1440 AH (Mayu 15, 2019)

Da sunan Allah, Mai Rahama, Mai jinkai

Assalamu Alaikum

Ya ku ‘yan uwana masu girma! A gaskiya yanzu na dan fara samun sa’ida, yanzu na dan fara nunfasawa, yanzu na dan fara jin dadi, yanzu hankalina ya dan fara kwanciya, yanzu ne na kara yarda da amincewa da sakankancewa cewa lallai duk da abubuwan da suke faruwa a arewa, na rashin tsaro, har yanzu arewa tana da karfi, kuma tana da manyan bayin Allah, kuma masu yi don Allah, da na samu labarin cewa manya, bayin Allah, mutanen kirki, masu son ci gaban arewa da Musulunci, masu kaunar hadin kan al’ummah, sun fara yunkurin daukar mataki a kan gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, da yake kokarin ya mayar da mu baya, yake kokarin ya kara jefa yankin arewa cikin wani sabon shafi na rarraba kan jama’ah da tarwatsa al’ummah, domin cimma wata manufa tasa ta siyasa, ba domin ci gaban talakawan Kano ba.

Allah ya saka wa manyan dattawan Kano da alkhairi, Allah ya saka wa Sarkin Musulmi Mai Alfarma Muhammadu Sa’ad Abubakar da alkhairi, Allah ya biya su da gidan Aljannah, amin.

‘Yan uwa, wallahi wannan yunkuri na su abin a yaba ne kwarai da gaske, haka ake son manya suyi, wato suyi kokarin taka wa duk wani shedani burki, mai kokarin mayar muna da hannun agogo baya, mai kokarin rusa al’ummah! Ta yaya wani dan siyasa, marar kishin al’ummar sa, marar girmama addininsa da al’adunsa, marar ganin girman manya, zai buwaye su? Kawai don Allah ya dan ba shi aron mulki na ‘yan wasu shekaru, amma yazo yana kokarin rusa muna abinda iyayen mu da kakannin mu da malaman mu da mujahidan mu suka gina muna shekaru aru-aru da muke tinkaho da shi kuma muke alfahari da shi?

Wai kuma don rashin kunya, mai wannan aikin har wasu suke kokarin kiran sa wai “KHADIMUL ISLAM”? Ta yaya za’ayi mai kokarin rusa addinin Musulunci da abinda Musulunci ya assasa kuma ya zama khadiminsa? Idan ba an mayar da mutane jahilai ba?

Haba jama’ah! Wai don Allah waye Ganduje? Ai abun kunya ne ma wallahi a wurin manyan arewa ace wannan mutum ya buwaye su! Shi din wa? Haba, ai wallahi wargi wuri yake samu!

Ina rokon Allah ya taimaki manyan mu, ya basu sa’a da nasara a kan wannan yunkuri na alkhairi, amin.

A gaskiya kuma wajibin mu ne mu san cewa wannan yunkuri nasu shine daidai, kuma shine rufin asirin mu. Domin wallahi yancin mu da mutuncin mu da martabar addinin mu da al’adunmu suke kokarin kwato muna, don haka wajibi ne muyi masu addu’a da fatan Allah ya taimake su!

Haba ‘yan uwa, wai ace wannan mutum Ganduje rashin kunyar ta sa ta kai har ga ya raina muna Sarkin Musulmi? Wanda wallahi idan ka raina shi ka raina addinin mu? Wai ace wai wannan mutum yaki ya girmama Sultan, haba! To idan ka wulakanta muna wadannan mutane, waye kuma yayi saura? So muke yi irin wulakanci da cin mutuncin da arna, turawa, ‘yan mulkin mallaka, mashaya giya, wawaye, jahilai, suka yiwa sarakunan mu da addinin mu wani dan siyasa, karen farautar turawa yaci gaba da shi, kuma mu sa masa ido? Wallahi ba zai taba yiwuwa ba!

Ku sani, wallahi, wannan mutum, Ganduje gandun sharri, idan ba mataki kwakkwara aka dauka a kan sa da ire-iren sa ba, wallahi za su ci gaba da wulakanta muna sarakuna iyayen al’ummah.

Ya manta cewa, wadannan bayin Allah, wato sarakuna, jagororin addinin mu ne da al’adunmu? Ya manta cewa, jihadin Shehu Dan Fodio ne ya kawo su, kuma shine ya assasa wadannan kujerun? Bai san cewa idan an wulakanta sarakuna, addinin mu da al’adun mu ne ake nema a rusa ba? Wallahi, wannan yaki ne da ya kamata duk wani dan halak, mai kishin addinin mu da al’adun mu da arewar mu ya shiga ayi da shi. Domin mu sani, da an rusa muna sarakunan mu, an raina su, to shike nan, bamu da wani katabus kuma, kuma bamu da wani abu da kuma ya rage da zamu yi tinkaho da shi.

Wannan al’amarin, al’amari ne da ya kamata mu sani cewa, Ganduje fa ba wai kawai da Mai Martaba Sarkin Kano Malam Muhammadu Sanusi II yake fada ba, a’a da dukkanin mu ‘yan arewa, Musulmai yake fada. Don haka, ya zama wajibi a gare mu, mu hadu mu yake shi domin mu dawo da martabar mu da mutuncin mu. Yin haka shi zai sa duk wani wawan dan siyasa da giyar mulki ta ke dibar sa, ya ke kokarin tozarta muna iyayen mu, wato sarakuna, zai san da cewa, bai fa isa yaci mutuncin su ya zauna lafiya ba!

Wadannan mutane, masu kokarin raina muna shugabanni da sunan siyasa, ya kamata su sani, wallahi, dukkanin sarakunan mu, tun daga Sarkin Musulmi, har zuwa Shehun Borno, har zuwa Sarkin Gwandu, har zuwa Mai Martaba Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na II, har zuwa Sarkin Gombe da Sarkin Suleja…kai da duk ko wane sarki da kuka sani, shugabanni ne na addinin Musulunci, jagororin mu ne na addini. Don haka taba su taba addinin Musulunci ne.

Muna daukar wulakantasu, wulakanta addini ne. Cin mutuncin su, cin mutuncin addini ne. Don haka, wallahi, ya kamata wawayen ‘yan siyasa, jahilai, da magoya bayan su, da ‘yan koren su, basu yi masu banbadanci, su kiyaye wannan. Kuma su iya sani cewa, ba zamu taba zuba ido, muyi shiru, mu rungume hannuwa, muna kallo, ana cin mutuncin jagororin addinin mu da al’adunmu mu kyale su ba. Domin zubar da mutuncin wadannan bayin Allah, wallahi zubar da mutuncin addinin Musulunci ne! Domin idan ma har kana da wani sabani da su (personal grudges), to kujerarsu da asalin kujerar zaka kalla ba su ba!

Don haka ya zama wajibi mu kiyaye!

Ina rokon Allah yaja zamanin sarakunan mu baki daya, Allah ya kara kare mutuncin su da imanin su da kujerun su, Allah ya isar masu ga duk wani mutum mai neman cin zarafin su, amin.

Ina rokon Allah ya taimake su, yayi masu jagora da kariya, ya kare mutuncin su da kujerun su daga wawanci da shirmen wawaye, mahassada, makirai, magauta da jahilai, amin.

Ya kamata Ganduje da duk wani dan siyasa da ke son farraka al’ummah, ya kawo masu rarrabuwa da rikici da gaba, a lokacin da aka kafa garin Kano babu wani shugaba guda daya da ya hada kan jama’a a karkashin mulkinsa. Jama’ar da suke zaune a kauyuka kamar Dala da Goron Dutse da Fanisau da Magwan da Jigirya duk suna karkashin shugabanci ne na mutanen da suke tare da su. Daga baya ne da garuruwan suka fara bunkasa, sannan dangantaka tsakaninsu ke kara inganta, a lokacin ne aka samu shugaba guda daya da ya hada kan mutane, shine Sarkin Kano.

Sannan ya kamata Ganduje da duk wani dan siyasa da ba ya son al’ummah su zauna lafiya, cikin hadin kai da kaunar juna, su sani, ita wannan masarauta ta Kano tana cikin manyan masarautu a kasar Hausa a yammacin Afirka. Kuma tarihi ya nuna cewa tsohuwar masarauta ce da aka kafa shekaru aru-aru tun zamanin jahiliyya kafin ma zuwan addinin Musulunci. Kuma wannan masarauta ta taimaka sosai wurin bunkasa garin Kano da Arewa da ma Najeriya baki daya. Garin Kano ya kasance cibiyar kasuwanci a yankin arewacin Najeriya da jamhuriyyar Nijar da ke makwabtaka da garin, don haka cin mutuncin wannan masarauta, cin mutuncin jama’ar Kano ne baki-daya.

Kuma ya kamata mu sani, shi sarkin Kano Malam Muhammadu Sanusi II, ikon Allah ne, Allah ne ya kawo shi, Allah ne ya dora shi akan wannan kujera, ba shine ya dora kan sa ba. Don haka wallahi, duk wanda yace zai ja dashi, to zai ja da ikon Allah ne! Sarki Muhammadu Sanusi II shine na 57 a jerin sarakunan Kano, kuma na 14 a jerin sarakunan Fulani.

An nada shi sarkin Kano bayan mutuwar Sarki marigayi Alhaji Ado Bayero.

Malam Muhammadu Sanusi II jikan Sarkin Kano Sanusi I ne. Maihaifinsa Aminu Sanusi yayi Chiroman Kano. Allah ya gafarta masu, amin.

Kuma binciken masana ya nuna cewa shine sarkin Kano da ya fi magabatansa ilimin zamani, sannan kuma yana da ilimin addinin Musulunci.

Kwararren masanin tattalin arziki ne, kuma kwararren ma’aikacin banki, inda ya taba rike mukamin gwamnan Babban Bankin Najeriya, wato CBN.

An sauke shi daga mukamin gwamnan CBN saboda yadda yake sukar gwamnatin Goodluck Jonathan da mulkinsa a lokacin, domin shi mutum ne da baya iya yin shiru idan ya ga cewa ana kokarin zaluntar al’ummah.

An haifi Malam Muhammadu Sanusi II a ranar 31 ga watan Yulin 1961. Kuma an nada shi Sarkin Kano ranar Lahadi 8 ga watan Yuni 2014.

Ina rokon Allah ya taimake shi, ya dora shi a saman makiyansa da magautan sa, da dukkan masu yi masa makirci, ya taya shi riko, ya kara masa imani da son talakawan sa, amin.

Wassalamu Alaikum

Dan uwan ku, Imam Murtadha Muhammad Gusau, ya rubuta daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa ta adireshi kamar haka: gusaumurtada@gmail.com ko kuma +2348038289761.

Tags: AbujaGoodluck JonathanHausaLabaraiNajeriyaPremioum times
Previous Post

Ko ka san cewa kwankwadan ruwan kwakwa na hana tsufa da wuri? Ga amfanin sa 12

Next Post

Hukumar Zabe ta dage zaben Kogi da Bayelsa

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
Voters Inec Nigeria

Hukumar Zabe ta dage zaben Kogi da Bayelsa

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa
  • Kotu ta bada belin mutumin da ke zargin wani da sace masa ‘gaba’
  • Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kaya na naira biliyan 6.6 a jihar Ogun
  • DOKAR HANA ZIRGA-ZIRGA: Garƙame mu da aka yi a Kano ya jawo mana hasara a Kasuwa, an jefa mutane ciki takura
  • Buhari ya yi da-na-sanin wasu abubuwa da ya aiwatar yana shugaban kasa – Adesina

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.