Shugaban kwamitin Koli na addinin Musulunci Ishaq Oloyode ya sanar da ganin watan Ramadana a Najeriya.
Hakan ya nuna cewa dukkan musulmin Najeriya za su tashi da Azumi ranar Litini 6 ga watan Mayu da yayi daidai da 1 ga watan Ramadana.
Oloyode ya ce sarkin Musulmai, Sultan Abubakar Saad zai sanar wa musulman kasar nan ganin watan.
Discussion about this post