• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Ba ni da ra’ayin takarar shugaban kasa, lokacin da aka zabe ni gwamnan Kaduna gashin kai na baki wul yanzu duk furfura – El-Rufai

    KALAMAN ƁATANCI GA ANNABI: Duk wanda ya yi zanga-zangar addini a Kaduna zai ɗanɗana kuɗar sa – Gargaɗin El-Rufa’i

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    Malami ya janye daga takarar gwamnan Kebbi duk da kurin da ya rika yi wai jama’a suka tilasta shi ya fito

    Chris Ngige

    Ngige ya janye takarar shugaban ƙasa, ya zaɓi ci gaba da zama ministan Buhari

    ZAƁEN 2023: APC za ta iya faɗuwa zaɓe idan ba ta tashi tsaye ba -Buhari

    ALAMOMIN WATSEWAR ƊAURIN TSINTSIYA A KANO: Mataimakin Kakakin Majalisa ya fice daga APC, ya koma PDP

    Ƴan Tiwita sun ce ba za su zaɓi Atiku ba saboda ya goge sakon yin tir da kisan Deborah da ta yi Ɓatanci ga Annabi

    Ƴan Tiwita sun ce ba za su zaɓi Atiku ba saboda ya goge sakon yin tir da kisan Deborah da ta yi Ɓatanci ga Annabi

    ƁATANCI GA MANZON ALLAH: Gwamnatin Sokoto ta rufe kwalejin Ilmi na Shehu Shagari

    ƁATANCI GA MANZON ALLAH: Gwamnatin Sokoto ta rufe kwalejin Ilmi na Shehu Shagari

    ‘Kowa Ya koma Gona’, amsar Buhari da aka ce masa bai taɓuka komai a bunƙasa tattalin arziki ba

    Buhari ya umurci Gwamnan CBN, Emefiele da jami’an gwamnati da ke takarar kujerun siyasa su ajiye aiki

    gunmen

    ‘Yan bindiga sun saki faston cocin Katolika da suka sace bayan an biya miliyoyin naira kuɗin fansa

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Ba ni da ra’ayin takarar shugaban kasa, lokacin da aka zabe ni gwamnan Kaduna gashin kai na baki wul yanzu duk furfura – El-Rufai

    KALAMAN ƁATANCI GA ANNABI: Duk wanda ya yi zanga-zangar addini a Kaduna zai ɗanɗana kuɗar sa – Gargaɗin El-Rufa’i

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    Malami ya janye daga takarar gwamnan Kebbi duk da kurin da ya rika yi wai jama’a suka tilasta shi ya fito

    Chris Ngige

    Ngige ya janye takarar shugaban ƙasa, ya zaɓi ci gaba da zama ministan Buhari

    ZAƁEN 2023: APC za ta iya faɗuwa zaɓe idan ba ta tashi tsaye ba -Buhari

    ALAMOMIN WATSEWAR ƊAURIN TSINTSIYA A KANO: Mataimakin Kakakin Majalisa ya fice daga APC, ya koma PDP

    Ƴan Tiwita sun ce ba za su zaɓi Atiku ba saboda ya goge sakon yin tir da kisan Deborah da ta yi Ɓatanci ga Annabi

    Ƴan Tiwita sun ce ba za su zaɓi Atiku ba saboda ya goge sakon yin tir da kisan Deborah da ta yi Ɓatanci ga Annabi

    ƁATANCI GA MANZON ALLAH: Gwamnatin Sokoto ta rufe kwalejin Ilmi na Shehu Shagari

    ƁATANCI GA MANZON ALLAH: Gwamnatin Sokoto ta rufe kwalejin Ilmi na Shehu Shagari

    ‘Kowa Ya koma Gona’, amsar Buhari da aka ce masa bai taɓuka komai a bunƙasa tattalin arziki ba

    Buhari ya umurci Gwamnan CBN, Emefiele da jami’an gwamnati da ke takarar kujerun siyasa su ajiye aiki

    gunmen

    ‘Yan bindiga sun saki faston cocin Katolika da suka sace bayan an biya miliyoyin naira kuɗin fansa

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

NAZARIN NA MUSAMMAN: Manyan Matsalolin Manchester United

Mohammed LerebyMohammed Lere
April 28, 2019
in Wasanni
0
Ole-Gunnar-Solskjaer-Man-Utd-TEAMtalk

Ole-Gunnar-Solskjaer-Man-Utd-TEAMtalk

Kungiyar Manchester United, wadda ya zuwa wannan mako, ta buga wasa 9 a jere, amma ta yi nasara a wasanni 2, an ci ta a wasanni 7 a cikin 9 din.

Ta na fama da gagarimar matsala, ko a ce matsaloli biyar wadanda kuma babu wata hanyar iya gagance su, kamar yadda masu sharhin wasan kwallo na Ingila da duniya ke nunawa.

Kafin Barcelona ta fitar da Manchester United a wasan Champions Legue, sai da Everton ta zura mata kwallaye 4:0.

Sannan kuma a ranar Talatar da ta gabata, Manchester City ta je har gida ta lallasa United da ci 2:0.

BABU SHIRIN GARAMBAWUL NA KUSA KO NA NESA

Babu wani takamaimen tsari ko shiri na tafiyar da kungiyar, ko kuma yin garambawul, tun bayan tafiyar dadadden mai horaswar kungiyar, Sir. Alex Ferguson.

A lokacin Ferguson, Manchester United ba ta bukatar dogon shiri idan ta sa gaba wajen neman nasara a gasanni kwallo.

Ferguson zai dora wakilcin gudanar da wasu ayyuka ga wadanda ya san za su iya, sannan kuma ya kan maida himma ya fuskanci kalubalen da ke gaban sa.

Ya san irin ’yan wasan da zai dauka masu jini a jika da za a ci moriyar su yau, gobe har zuwa shekaru sama goma a can gaba.

Matsala:

Matsaloli sun bijiro, sun lullube Manchester tun bayan tafiyar Ferguson, lokacin da Mataimakin Shugaban Kungiyar, Ed Woodward ya jagoranci tafiyar da sha’anin gudanarwar ta.

Sai ya rika tafiyar da Manchester kamar harka ta kwangila. Woodward bai san komai ba a harkar kwallo, amma sai ya kankame komai sai shi, sai kuma abin da ya ce kawai.

Nan da na sai aka fara yin kutubalbal da Manchester United, inda David Moyes ya karba ya ba Louis van Gaal. Shi kuma ya karba ya mika wa Jose Mourinho.

Dukkan su ukun babu wani wanda ya kamo hanyar da Ferguson ya bi ya dora kungiyar a hanyar kwallon kafa madaidaiciya.

Yanzu an kawo Ole Gunnar Solskjaer, wanda tsohon dan wasan kungiyar ne, ya san makama, kuma ya san madafa, amma kuma ba shi da masu dafa masa da zai iya taka tudun-mun-tsira har ya tserar da Manchester daga halin da ta ke a ciki.

RASHIN SAYEN KWARARRUN ‘YAN WASA

Dukkan kociyan da aka yi bayan Ferguson, ba su nuna kwarewa wajen sayen kwararrun ’yan wasa ba, sai su ka karkata wajen sayen wadanda suka sani kawai.

Sannan kuma sun rika samun sabani da wasu ’yan wasa, wadanda duk iyawar ka, idan ka na da matsala da kociya, to kai za ka kwan a ciki.

Duk kociyan da ya zubar da girman sa har ya ke fada da dan wasa, to ba kociyan kwarai ba ne.

Kowane kulob na Ingila da sauran kasashe na da tsarin daukar ’yann wasa da kuma tsarin salon wasan da suke takawa. Amma kuma kowane kulob na da wadanda ba su dace da irin salon wasan kulob din ba.

Amma wadanda ba su dace da Manchester ba, kuma su ke buga wasa a kulob din, sun fi na sauran kungiyoyi manya yawa.

Idan Manchester ba ta tashi tsaye ta gina tsarin da zai rike kungiyar tsawon shekaru 10 zuwa 20 nan gaba ba, to za su ci gaba da harbat-ta-Mati ne kawai. Sai dai su rika ganin wasu kungiyoyi na buga Champions Legue kawai, su kuma sun shiga rububi.

Ku dubi yadda tuni Gordiola na Manchester City ya daidaita da Gabriel Jesus, Raheem Sterling da Bernando Silva sun sabunta yarjejeiyar ci gaba da zama kulob din.

Amma Mancher United sai kwan-gaba-kwan-baya ta ke ta yi da Alixes Sanchez, wanda ke neman sai a biya shi albashin fam milyan 20.35 a duk shekara, duk da cewa ba ya tabuka komai a yanzu.

Idan Manchester ba su saki Sanchez ya tafi ba, to ba za su fita cikin matsalar ’yan wasa ba. Bai yiwuwa su rike shi suna biyan sa abin da ya fi sauran ’yan wasan da suka fi shi kokari, nesa ba kusa ba.

To amma wane kulob ne zai sayi Sanchez a yanzu? Wa zai sayi biri a sama, ko kuma jibadau-kayan-nauyi?

Sannan da wahala David de Gea da Marcus Rashford su sake zama kulob din idan wa’adin su ya cika.

MATSALAR MAI HORASWA

Ole Gunner da aka dauko, bai taba horas da wani babban kulob ba. An dai dauko shi ne domin a gaggauta cike gurbin da aka cire Mourinho, sannan kuma babu wani babban kociya da za a dauka a lokacin.

Ya na zuwa sai ya taki sa’a, kulob din ya koma cin kwallaye da samun nasara, ba kamar irin rikon-sakainar-kashin da Mourinho ya yi masa ba.

’Yan wasan da suka rika rigima da Mourinho, irin Rashford, Pogba, Anthonu Martial duk sun samu ’yancin su kenan. Sai dai kuma tun kunnen doki 2:2 da Manchester ta buga da kungiyar Burnley a cikin Janairu, shikenan sai hannun agogo ya rika komawa baya-da-baya.

RASHIN IYA TAKUN WASA

Manchester da ke hannun Solkjaer a yanzu ba ta da bambanci da wadda ya gada, babu abin da ya canja.

Karfin da ta ke takama da shi, shi ne karfin kwararren mai tsaron gida, De Gea da kuma karfin ‘yan gaba guda biyu kawai. Daga ba su ba kuwa, duk sauran magen-Lami ce, ba cizo ba yakushi.

Daga inda ka ce Manchester ta samu matsala daga masu tsaron bayan ta, to shi kuma mai tsaron gida sai duka ya yi masa yawa, har ya rasa wanda zai kare, a yi ta sharara masa ruwan kwallaye.

GAGGAWAR AMINCEWA DA SOLKJAER

Manchester ta yi gaggawar damka wa Solkjaer kwangilar tsawon shekaru uku. Ganin ya shigo da sa’a daga farko, an ci gaba da dora laifin matsala a kan Mourinho da aka kora.

Yanzu kuma da reshe-ya-juye-da-mujiya, sai ake dora laifin a kan ’yan wasa. Amma kuma ’yan wasan da Mourinho din ya bari, su dai ne har yanzu, ba a canja ko an kara ko daya ba.

MATSALAR GLAZER, MASU KUNGIYAR MANCHESTER

Idan aka koma duba matsalar da su kan su shugabannin Manchester ke haifar wa kulub din, to batun yawan kuskuren da De Gea ke yi idan an takura shi, ko surutan kwallo ba ta yi wa Pogba kyau a wani wasa ba, wannan duk karamar magana ce.

Manchester dai ta na karkashin wasu ’ya’yan hamshakin attajirin nan Malcolm Glazer, su shida ke da kulob din. Tun da suka sayi kulob din cikin 2005 su ke ta kwasar ribar da ake samu a duk shekara, su da sauran masu kananan hannayen jari a kulob din.

Daga 2005 zuwa bana, an cire fam bilyan 1, sama da naira bilyan 430 kenan daga asusun Manchester, ana biyan masu kulob matsayin ribar da ake samu a duk shekara.

Kamata ya yi wadannan makudan kudade a bar su a cikin asusun kungiyar ana kara mata karfi, kamar yadda irin su Real Madrid da Barcelona ke yi da kuma PSG da Manchester City su ke yi a yanzu .

Amma duk ribar da Manchester ta ci a karshen shekara, sai a kwashe kudin a tura birnin Florida na Amurka, inda shugabannin kungiyar ke zaune su na gudanar da harkokin kasuwancin su.

TULIN BASHI MAI WAHALAR BIYA

Ya zuwa karshen shekarar da ta gabata, ana bin Manchester bashin fam milyan 495.8. wanda dalilin wannan bashi ne shugabannin kungiyar a kashen kakar wasan da ta gabata suka rattaba ka’idojin cewa:

“Za mu rage yawan kashe kudade domin mu samu mu rika biyan bashin da ke kan mu. Cikin abubuwan da za mu kage kashe kudi a kai, har da yawan dauko haya ko sayen ‘yan wasa, rage yawan masu taimaka wa kociya….duk da dai mun san wannan zai shafi karfin iya gogayyar mu da sauran manyan kulob wajen samun ’yan wasa da masu horas da su.”

A lokacin da su Glazer suka sayi Manchester, sun taras da bashin fam milyan 275 a kan kungiyar.

Matsala ita ce, idan ba a biya bashin ba, to duk shekara akwai kudin ruwa har fam milyan 60 da zai rika karuwa, ko kuma a rika biya, har zuwa shekarar da aka biya kudin bashin gaba daya.

Irin yadda Manchester United ta rika samun makudan kudaden shiga, har yadda ta ke ci gaba da samu a yanzu, babu dalilin da zai sa a ce ba ita ba ce ta fi kowace kungiya karfi a duk duniya?

Shin wai me ya ake neman bari Manchester United ta koma ’yan-harbat-ta-Mati ne?

Sun samu kwararren kociya, Alex Fersguson, wanda ya sayar da Cristiano Ronaldo, ya sayi Micheal Owen arha takyaf, kuma a ci kofin Premier a shekarar. Idan ba Ferguson ba, duk duniya wane kociya ne zai iya yin haka?

HALIN DA OLD TRAFFORD YA KE CIKI

Yanzu idan ka ziyarci filin wasa na Old Trafford, haushi da takaici zai kama ka, idan ka ga yadda aka bar wasu sassa na sa ba a kula da su.

Ko a ranar Laraba ta makon jiya, sai da ruwan sama ya rika zubowa a kan ’yan kallo daga wani wuri da rufin filin ya lalace ba a gyara ba.

Sannan kuma sama da shekaru uku kenan narka-narkan beraye ke ta karakaina kuma su na ci gaba da yawa a cikin ginin filin kwallon.

Akwai wawakeken fili a cikin harabar filin kwallo nan a Old Trafford, wanda har yanzu an ki amfani da wurin a yi wasu gine-gine. Sai fa wani otal da ’yan wasan Mancherter wadanda suka ci kofi a 1992 suka hada kudi suka gina a filin.

Zamani ya zo duk wani babban kulob ya na tafiya da zamani, kuma ya na ci gaba. Madrid na kan hanyar gida filin wasa da babu kamar sa a duniya. Barcelona na kan gagarimin shiri da sabon sauyi. Atletico Madrid ta gina sabon filin wasa, wanda a cikin sa za a buga wasan karshe a Champions League a Madrid.

Juventus fa? Ita ma sabon filin wasa. PSG da Liverpool na gagarimin sauyi. Manchester City na sabon filin wasa. Arsenal da Tottenham sun yi sabon filin wasa.

Mancchester United fa? Babu sabon filin wasa, babu sabbin ’yan wasa, babu kwararrun ’yan wasa, kuma an ki gyara tsohon filin su na kaka da kakanni, wato Old Traffpord.

Ana ganin idan har dan Sarkin Saudiyya, Yarima Salman, wanda ke shugabancin kasar a yanzu ya amince ya sayi kungiyar daga hannun ’ya’yan Glazer, to za ta iya dawowa cikin hayyacin ta nan da shekaru kadan.

Amma dai hakikanin gaskiya shekaru 14 da Man U ta yi a hannun Glazers, Turawan kasar Amurka, ci gaba ta rika samu, amma na mai ginar rijiya.

Tags: Alex FersgusonLabarinManchesterOle Gunnar SolskjaerPogbaPREMIUM TIMESUnited
Previous Post

NYSC ta yi sabon shugaba

Next Post

Hukumar Hizba ta warware aure 312 cikin shekara 4 a jihar Jigawa

Next Post
Hukumar Hizba ta warware aure 312 cikin shekara 4 a jihar Jigawa

Hukumar Hizba ta warware aure 312 cikin shekara 4 a jihar Jigawa

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • FARMAKIN JIRGIN ƘASA: ‘Yan ta’adda sun saki ɗaya mai cikin saboda tausayin laulayin da ta ke yi
  • APC TA YI RASHI: Dalilin ficewa ta daga APC na koma jam’iyyar mai alamar kayan marmari -Abdulmumin Jibrin
  • RUBUBIN TAKARAR SHUGABAN ƘASA A 2023: Yadda Buhari ke gwara kawunan ‘yan takarar APC
  • KALAMAN ƁATANCI GA ANNABI:Ƴan siyasan mu sun yi shiru tsit, kowa na tsoron ya fito ya fadi gaskiya – Tilde
  • Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.