• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

NAZARIN NA MUSAMMAN: Manyan Matsalolin Manchester United

Mohammed LerebyMohammed Lere
April 28, 2019
in Wasanni
0
Ole-Gunnar-Solskjaer-Man-Utd-TEAMtalk

Ole-Gunnar-Solskjaer-Man-Utd-TEAMtalk

Kungiyar Manchester United, wadda ya zuwa wannan mako, ta buga wasa 9 a jere, amma ta yi nasara a wasanni 2, an ci ta a wasanni 7 a cikin 9 din.

Ta na fama da gagarimar matsala, ko a ce matsaloli biyar wadanda kuma babu wata hanyar iya gagance su, kamar yadda masu sharhin wasan kwallo na Ingila da duniya ke nunawa.

Kafin Barcelona ta fitar da Manchester United a wasan Champions Legue, sai da Everton ta zura mata kwallaye 4:0.

Sannan kuma a ranar Talatar da ta gabata, Manchester City ta je har gida ta lallasa United da ci 2:0.

BABU SHIRIN GARAMBAWUL NA KUSA KO NA NESA

Babu wani takamaimen tsari ko shiri na tafiyar da kungiyar, ko kuma yin garambawul, tun bayan tafiyar dadadden mai horaswar kungiyar, Sir. Alex Ferguson.

A lokacin Ferguson, Manchester United ba ta bukatar dogon shiri idan ta sa gaba wajen neman nasara a gasanni kwallo.

Ferguson zai dora wakilcin gudanar da wasu ayyuka ga wadanda ya san za su iya, sannan kuma ya kan maida himma ya fuskanci kalubalen da ke gaban sa.

Ya san irin ’yan wasan da zai dauka masu jini a jika da za a ci moriyar su yau, gobe har zuwa shekaru sama goma a can gaba.

Matsala:

Matsaloli sun bijiro, sun lullube Manchester tun bayan tafiyar Ferguson, lokacin da Mataimakin Shugaban Kungiyar, Ed Woodward ya jagoranci tafiyar da sha’anin gudanarwar ta.

Sai ya rika tafiyar da Manchester kamar harka ta kwangila. Woodward bai san komai ba a harkar kwallo, amma sai ya kankame komai sai shi, sai kuma abin da ya ce kawai.

Nan da na sai aka fara yin kutubalbal da Manchester United, inda David Moyes ya karba ya ba Louis van Gaal. Shi kuma ya karba ya mika wa Jose Mourinho.

Dukkan su ukun babu wani wanda ya kamo hanyar da Ferguson ya bi ya dora kungiyar a hanyar kwallon kafa madaidaiciya.

Yanzu an kawo Ole Gunnar Solskjaer, wanda tsohon dan wasan kungiyar ne, ya san makama, kuma ya san madafa, amma kuma ba shi da masu dafa masa da zai iya taka tudun-mun-tsira har ya tserar da Manchester daga halin da ta ke a ciki.

RASHIN SAYEN KWARARRUN ‘YAN WASA

Dukkan kociyan da aka yi bayan Ferguson, ba su nuna kwarewa wajen sayen kwararrun ’yan wasa ba, sai su ka karkata wajen sayen wadanda suka sani kawai.

Sannan kuma sun rika samun sabani da wasu ’yan wasa, wadanda duk iyawar ka, idan ka na da matsala da kociya, to kai za ka kwan a ciki.

Duk kociyan da ya zubar da girman sa har ya ke fada da dan wasa, to ba kociyan kwarai ba ne.

Kowane kulob na Ingila da sauran kasashe na da tsarin daukar ’yann wasa da kuma tsarin salon wasan da suke takawa. Amma kuma kowane kulob na da wadanda ba su dace da irin salon wasan kulob din ba.

Amma wadanda ba su dace da Manchester ba, kuma su ke buga wasa a kulob din, sun fi na sauran kungiyoyi manya yawa.

Idan Manchester ba ta tashi tsaye ta gina tsarin da zai rike kungiyar tsawon shekaru 10 zuwa 20 nan gaba ba, to za su ci gaba da harbat-ta-Mati ne kawai. Sai dai su rika ganin wasu kungiyoyi na buga Champions Legue kawai, su kuma sun shiga rububi.

Ku dubi yadda tuni Gordiola na Manchester City ya daidaita da Gabriel Jesus, Raheem Sterling da Bernando Silva sun sabunta yarjejeiyar ci gaba da zama kulob din.

Amma Mancher United sai kwan-gaba-kwan-baya ta ke ta yi da Alixes Sanchez, wanda ke neman sai a biya shi albashin fam milyan 20.35 a duk shekara, duk da cewa ba ya tabuka komai a yanzu.

Idan Manchester ba su saki Sanchez ya tafi ba, to ba za su fita cikin matsalar ’yan wasa ba. Bai yiwuwa su rike shi suna biyan sa abin da ya fi sauran ’yan wasan da suka fi shi kokari, nesa ba kusa ba.

To amma wane kulob ne zai sayi Sanchez a yanzu? Wa zai sayi biri a sama, ko kuma jibadau-kayan-nauyi?

Sannan da wahala David de Gea da Marcus Rashford su sake zama kulob din idan wa’adin su ya cika.

MATSALAR MAI HORASWA

Ole Gunner da aka dauko, bai taba horas da wani babban kulob ba. An dai dauko shi ne domin a gaggauta cike gurbin da aka cire Mourinho, sannan kuma babu wani babban kociya da za a dauka a lokacin.

Ya na zuwa sai ya taki sa’a, kulob din ya koma cin kwallaye da samun nasara, ba kamar irin rikon-sakainar-kashin da Mourinho ya yi masa ba.

’Yan wasan da suka rika rigima da Mourinho, irin Rashford, Pogba, Anthonu Martial duk sun samu ’yancin su kenan. Sai dai kuma tun kunnen doki 2:2 da Manchester ta buga da kungiyar Burnley a cikin Janairu, shikenan sai hannun agogo ya rika komawa baya-da-baya.

RASHIN IYA TAKUN WASA

Manchester da ke hannun Solkjaer a yanzu ba ta da bambanci da wadda ya gada, babu abin da ya canja.

Karfin da ta ke takama da shi, shi ne karfin kwararren mai tsaron gida, De Gea da kuma karfin ‘yan gaba guda biyu kawai. Daga ba su ba kuwa, duk sauran magen-Lami ce, ba cizo ba yakushi.

Daga inda ka ce Manchester ta samu matsala daga masu tsaron bayan ta, to shi kuma mai tsaron gida sai duka ya yi masa yawa, har ya rasa wanda zai kare, a yi ta sharara masa ruwan kwallaye.

GAGGAWAR AMINCEWA DA SOLKJAER

Manchester ta yi gaggawar damka wa Solkjaer kwangilar tsawon shekaru uku. Ganin ya shigo da sa’a daga farko, an ci gaba da dora laifin matsala a kan Mourinho da aka kora.

Yanzu kuma da reshe-ya-juye-da-mujiya, sai ake dora laifin a kan ’yan wasa. Amma kuma ’yan wasan da Mourinho din ya bari, su dai ne har yanzu, ba a canja ko an kara ko daya ba.

MATSALAR GLAZER, MASU KUNGIYAR MANCHESTER

Idan aka koma duba matsalar da su kan su shugabannin Manchester ke haifar wa kulub din, to batun yawan kuskuren da De Gea ke yi idan an takura shi, ko surutan kwallo ba ta yi wa Pogba kyau a wani wasa ba, wannan duk karamar magana ce.

Manchester dai ta na karkashin wasu ’ya’yan hamshakin attajirin nan Malcolm Glazer, su shida ke da kulob din. Tun da suka sayi kulob din cikin 2005 su ke ta kwasar ribar da ake samu a duk shekara, su da sauran masu kananan hannayen jari a kulob din.

Daga 2005 zuwa bana, an cire fam bilyan 1, sama da naira bilyan 430 kenan daga asusun Manchester, ana biyan masu kulob matsayin ribar da ake samu a duk shekara.

Kamata ya yi wadannan makudan kudade a bar su a cikin asusun kungiyar ana kara mata karfi, kamar yadda irin su Real Madrid da Barcelona ke yi da kuma PSG da Manchester City su ke yi a yanzu .

Amma duk ribar da Manchester ta ci a karshen shekara, sai a kwashe kudin a tura birnin Florida na Amurka, inda shugabannin kungiyar ke zaune su na gudanar da harkokin kasuwancin su.

TULIN BASHI MAI WAHALAR BIYA

Ya zuwa karshen shekarar da ta gabata, ana bin Manchester bashin fam milyan 495.8. wanda dalilin wannan bashi ne shugabannin kungiyar a kashen kakar wasan da ta gabata suka rattaba ka’idojin cewa:

“Za mu rage yawan kashe kudade domin mu samu mu rika biyan bashin da ke kan mu. Cikin abubuwan da za mu kage kashe kudi a kai, har da yawan dauko haya ko sayen ‘yan wasa, rage yawan masu taimaka wa kociya….duk da dai mun san wannan zai shafi karfin iya gogayyar mu da sauran manyan kulob wajen samun ’yan wasa da masu horas da su.”

A lokacin da su Glazer suka sayi Manchester, sun taras da bashin fam milyan 275 a kan kungiyar.

Matsala ita ce, idan ba a biya bashin ba, to duk shekara akwai kudin ruwa har fam milyan 60 da zai rika karuwa, ko kuma a rika biya, har zuwa shekarar da aka biya kudin bashin gaba daya.

Irin yadda Manchester United ta rika samun makudan kudaden shiga, har yadda ta ke ci gaba da samu a yanzu, babu dalilin da zai sa a ce ba ita ba ce ta fi kowace kungiya karfi a duk duniya?

Shin wai me ya ake neman bari Manchester United ta koma ’yan-harbat-ta-Mati ne?

Sun samu kwararren kociya, Alex Fersguson, wanda ya sayar da Cristiano Ronaldo, ya sayi Micheal Owen arha takyaf, kuma a ci kofin Premier a shekarar. Idan ba Ferguson ba, duk duniya wane kociya ne zai iya yin haka?

HALIN DA OLD TRAFFORD YA KE CIKI

Yanzu idan ka ziyarci filin wasa na Old Trafford, haushi da takaici zai kama ka, idan ka ga yadda aka bar wasu sassa na sa ba a kula da su.

Ko a ranar Laraba ta makon jiya, sai da ruwan sama ya rika zubowa a kan ’yan kallo daga wani wuri da rufin filin ya lalace ba a gyara ba.

Sannan kuma sama da shekaru uku kenan narka-narkan beraye ke ta karakaina kuma su na ci gaba da yawa a cikin ginin filin kwallon.

Akwai wawakeken fili a cikin harabar filin kwallo nan a Old Trafford, wanda har yanzu an ki amfani da wurin a yi wasu gine-gine. Sai fa wani otal da ’yan wasan Mancherter wadanda suka ci kofi a 1992 suka hada kudi suka gina a filin.

Zamani ya zo duk wani babban kulob ya na tafiya da zamani, kuma ya na ci gaba. Madrid na kan hanyar gida filin wasa da babu kamar sa a duniya. Barcelona na kan gagarimin shiri da sabon sauyi. Atletico Madrid ta gina sabon filin wasa, wanda a cikin sa za a buga wasan karshe a Champions League a Madrid.

Juventus fa? Ita ma sabon filin wasa. PSG da Liverpool na gagarimin sauyi. Manchester City na sabon filin wasa. Arsenal da Tottenham sun yi sabon filin wasa.

Mancchester United fa? Babu sabon filin wasa, babu sabbin ’yan wasa, babu kwararrun ’yan wasa, kuma an ki gyara tsohon filin su na kaka da kakanni, wato Old Traffpord.

Ana ganin idan har dan Sarkin Saudiyya, Yarima Salman, wanda ke shugabancin kasar a yanzu ya amince ya sayi kungiyar daga hannun ’ya’yan Glazer, to za ta iya dawowa cikin hayyacin ta nan da shekaru kadan.

Amma dai hakikanin gaskiya shekaru 14 da Man U ta yi a hannun Glazers, Turawan kasar Amurka, ci gaba ta rika samu, amma na mai ginar rijiya.

Tags: Alex FersgusonLabarinManchesterOle Gunnar SolskjaerPogbaPREMIUM TIMESUnited
Previous Post

NYSC ta yi sabon shugaba

Next Post

Hukumar Hizba ta warware aure 312 cikin shekara 4 a jihar Jigawa

Mohammed Lere

Mohammed Lere

Next Post
Hukumar Hizba ta warware aure 312 cikin shekara 4 a jihar Jigawa

Hukumar Hizba ta warware aure 312 cikin shekara 4 a jihar Jigawa

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN KASA: Atiku ya kai wa kotu tulin hujjoji daga na’urar BVAS a zaɓen 2023
  • Dikko Radda zai saka tsarin TSA a duka harkokin shige da ficen kudaden jihar Katsina
  • Dalilin da ya sa na canja sunan titin Raba zuwa titin ‘Nasir El-Rufai – Gwamna Uba Sani
  • KOKAWAR ƘWACE KUJERAR TINUBU: Kotu ta karɓi kwafen takardun zargin Asiwaju ya yi harƙallar muggan ƙwayoyi
  • SIYASAR KANO: Gwamna Abba ya soke naɗe-naɗe, ya ƙwace filaye da kadarorin da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.