Duk da rashin tsaro da kashe-kashen rayuka da ake fama da shi a jihar Zamfara, jam’iyyu 43 na nan na shirin fafatawa a zaben kananan hukumomin da za ayi a jihar.
Hukumar zabe ta jihar ta tsayar da ranar 27 ga watan Afrilu a matsayin ranar da za a yi zaben kananan hukumomi a jihar.
Jami’in hukumar na jihar Bello Wadata ya sanar da haka da yake zantawa da Kamfanin Daillancin Labaran Najeriya ranan Litini.
Wadata ya ce hukumar ta zauna da masu ruwa da tsaki a jihar domin tattaunan yadda za a tunkari zaben.
Wadata ya ce suna sa ran cewa shiri da matakai da hukumar ta dauka game da zabe zai taimaka wajen ganin zaben ya gudana cikin kwanciyar hankali.
Discussion about this post