Kungiyar ‘Victims Support Fund (VSF)’ ya tallafa wa mata 17,000 wadanda suka yi fama da hare-haren Boko Haram a Arewa Maso Gabashin kasar nan da jarin Naira 20,000 domin inganta rayuwar su.
Shugaban kungiyar Sunday Ochoche ya fadi haka da yake zantawa da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya a Abuja.
Ochoche ya bayyana cewa VSF ta tsara shirin tallafa wa mata a fannin sana’o’i da farfado da aiyukkan gona domin inganta rayukan mutanen da hare-haren Boko Haram ya shafa a yankin Arewa Maso Gabashin kasar nan.
” Mun fara da tallafa wa mata masu sana’o’in hannu 100 da Naira 20,000. A yanzu dai wannan shiri ya tallafa wa mata 17,000 da jarin Naira 20,000 da aka zabo daga sansanoni 10 dake yankin.
Ochoche ya ce a fannin aiyukkan gona kuma VSF za ta tallafa wa mata da maza dake noman rani da damuna da kuma wadanda ke kiwo.
Ya ce a fannin gona VSF za ta samar da taki, iri, magungunan feshi da sauran su wadanda manoman za su bukata sannan a fannin kiwata dabbobi VSF za ta horas da masu kiwata dabbobi musamman masu kiwon awaki kan yadda za su iya siyar da nonon awakin su domin siyarwa.
Discussion about this post