Wasu ’yan bindiga sun bude wuta yayin da ake tsakiyar gangamin yakin neman zaben jam’iyyar APC a kan titin Edet Akpan, Uyo, babban birnin jihar Akwa Ibom.
An tabbatar da ji wa da dama rauni a wurin.
Wani mai babur din A Daidaita Sahu ya ce da idon sa ya ga lokacin da wata mota kirar Toyota Hilux ta tsaya a tsallaken titi, inda wasu mutane suka fito daga cikin motar, suka tsallaka suka tsaya a bakin kofar shiga filin taron.
Ya ce su ne suka bude wuta cikin taron, kuma suka yi sauri, suka tsallaka titi a guje, suka shiga motar su suka arce.
Filin kamfen din dai babba ne, ya nunka filin kwallo fadi, kuma a wurin ne ake yawan taruruka na siyasa. A kullum wurin ba ya rabo da jama’a tun da kakar yakin neman zabe ta shigo.
Ko a ranar Litinin sai da Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo ya halarci taron APC a wurin, inda ya wakilci shugaba Muhammadu Buhari.
APC dai ta zargi PDP da laifin kai harin. Ita kuma PDP ta nesanta kanta daga harin da aka kai wa APC a filin kamfen din.
Kakakin ‘yan sandan jihar Akwa Ibom da PREMIUM TIMES ta kira bai dauka ba, har yanzu bai kira ko ya rubuto sakon tes ta waya ba.
Discussion about this post