• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    GARGAƊI GA BUHARI: ‘Ƙaƙudubar ƙarancin kuɗi na yi wa zaɓen 2023 da dimokraɗiyya babbar barazana’ – Akeredolu

    Gwamnatin Jihar Ondo ta faɗi dalilin da ya sa ba za ta buɗe masallacin cikin watan Ramadan ba

    Kotu ta yi wa gwamnatin Gombe da ‘yan sanda katanga da dan jarida, Dahiru Kera

    Kotu ta yi wa gwamnatin Gombe da ‘yan sanda katanga da dan jarida, Dahiru Kera

    Samuel Ortom

    Gwamna Ortom ya janye ƙarar da ya maka hadimin sa, wanda ya kayar da shi a zaɓen Sanatan Benuwai, kuma ya roƙi yafiya

    An kara wa ma’aikatan jinya na jihar Yobe albashi

    Akalla mutum 7,806 suka kamu da cutar tarin fuka a tsakanin shekarar 2021 – 2022 a jihar Bauchi

    Iyorchia Ayu ba alheri ba ne, baƙin jinin sa ne ya janyo faɗuwar PDP zaɓen 2023 – Chimaroke Nnamani

    Iyorchia Ayu ba alheri ba ne, baƙin jinin sa ne ya janyo faɗuwar PDP zaɓen 2023 – Chimaroke Nnamani

    Janar Diya, tsohon Mataimakin Janar Abacha ya rasu

    Janar Diya, tsohon Mataimakin Janar Abacha ya rasu

    Kashim Shettima of Borno

    SHARI’AR ZARGIN SHETTIMA YA FITO TAKARA WURI BIYU: Kotu ta kori ƙarar da PDP ta nemi a soke takarar Tinubu da Shettima

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    GARGAƊI GA BUHARI: ‘Ƙaƙudubar ƙarancin kuɗi na yi wa zaɓen 2023 da dimokraɗiyya babbar barazana’ – Akeredolu

    Gwamnatin Jihar Ondo ta faɗi dalilin da ya sa ba za ta buɗe masallacin cikin watan Ramadan ba

    Kotu ta yi wa gwamnatin Gombe da ‘yan sanda katanga da dan jarida, Dahiru Kera

    Kotu ta yi wa gwamnatin Gombe da ‘yan sanda katanga da dan jarida, Dahiru Kera

    Samuel Ortom

    Gwamna Ortom ya janye ƙarar da ya maka hadimin sa, wanda ya kayar da shi a zaɓen Sanatan Benuwai, kuma ya roƙi yafiya

    An kara wa ma’aikatan jinya na jihar Yobe albashi

    Akalla mutum 7,806 suka kamu da cutar tarin fuka a tsakanin shekarar 2021 – 2022 a jihar Bauchi

    Iyorchia Ayu ba alheri ba ne, baƙin jinin sa ne ya janyo faɗuwar PDP zaɓen 2023 – Chimaroke Nnamani

    Iyorchia Ayu ba alheri ba ne, baƙin jinin sa ne ya janyo faɗuwar PDP zaɓen 2023 – Chimaroke Nnamani

    Janar Diya, tsohon Mataimakin Janar Abacha ya rasu

    Janar Diya, tsohon Mataimakin Janar Abacha ya rasu

    Kashim Shettima of Borno

    SHARI’AR ZARGIN SHETTIMA YA FITO TAKARA WURI BIYU: Kotu ta kori ƙarar da PDP ta nemi a soke takarar Tinubu da Shettima

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

KWANKWASO: Shin Yaki Ya Ci Kwamanda, Ko Da Sauran Fama?

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
March 25, 2019
in Rahotanni
0
Rabiu Musa Kwankwaso

Rabiu Musa Kwankwaso

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya zama Gwamnan Jihar Kano cikin 1999, a karkashin jam’iyyar PDP, bayan kasancewar sa kafin sannan ya taba rike mukamin Mataimakin Shugaban Majalisar Tarayya, a zangon siyasar da aka yi karkashin mulkin sojoji.

RIGIMAR KWANKWASO DA RIMI

Farkon hawan Kwankwaso kujerar mulki, ya fara da samun matsala da iyayen gidan siyasar PDP, su marigayi Abubakar Rimi, sakamakon wani tsaurin idon da Rimi ke ganin cewa Kwankwaso ya yi masa a matsayin sa na gwamna.

Abin da kuwa ya faru shi ne, kafin zaben 1999, PDP kan yi tarukan siyasar ta a Gidan Akida, wanda gida ne na taron siyasar Rimi, amma daga baya ya rikide na PDPin jihar Kano bai-daya a lokacin.

An ci gaba da taruka a Gidan Akida har bayan hawan Kwankwaso gwamnati. Ba a dade ba sai Kwankwaso a matsayin sa na gwamna, ya ce tunda Gidan Akida gidan siyasa ne na bangaren mutum daya, wato Rimi, to bai kamata a rika taro a can ba. Musamman tunda PDP ta kasu bangare-bangare a Kano.

Kwankwaso ya ce a rika yin taro a ofishin jam’iyya maimakon a Gidan Akida. Wannan dauke taro da ya yi zuwa ofishin jam’iyya ya bata wa Rimi rai matuka.

Sabani ya shiga tsakanin Kwankwaso da Rimi, har ta kai ‘yan siyasa sun rika zuzuta rikicin, yadda ya kara tsami sosai.

Cikin fushi, kuma a cikin 1999, Rimi ya rubuta wa Kwankwaso wata wasika mai dauke da bayanan cewa: “Rudanin da ka ke haifarwa a cikin jam’iyyar PDP a Kano, da kuma masaniyar da na ke da ita cewa takardar shaidar digirin ka na Dakta ta bogi ce, to za su iya janyowa a tsige ka.”

KARSHEN ZANGON SA NA FARKO, 2003

Kwankwaso ya kammala zangon san a daya a cikin yanayin da guguwar Buhariyya ta fara bugawa a Kano. Hakan ya kawo karshen mulkin sa, inda APP ta tsaida Ibrahim Shekarau, tsohon ma’aikacin Kwankwaso, kuma ya yi nasara a kan sa.

An nuna wa Kwankwaso kiyayya a lokacin zaben a Kano. Ranar da aka sanar da sakamakon kayar da shi a zaben 2003, an yi ta kade-kade da karakainar murna a Kano har kusan wayewar gari.

Allah ya rufa masa asiri, inda shugaban kasa na lokacin, Olusegun Obasanjo ya nada shi wani mukami, daga baya kuma aka ba shi Ministan Tsaro. Duk a wadannan lokutan ya ci gaba da tafiya tare da Abdullahi Ganduje, wanda shi ne mataimakin sa a lokacin da ya ke gwamna.

KWANKWASO DAWO DAWO

Bayan Shekarau ya kammala zangon sa na biyu, cikin 2011, Kwankwaso ya koma neman sake hawa kujerar gwamnan Kano, kuma Kanawa suka yi masa kyakkyawar tarba. Ya sake karbar mulki a hannun Shekarau, wanda ya mika wa mulki a cikin 2011.

KWANKWASIYYA AMANA

Sake hawan Kwankwaso ke da wuya sai ya karfafa gidan akidar siyasar sa ta Kwankwasiyya. Da ya ke PDP ta kasu gida-gida ko a Kano, to shi Kwankwaso in dai ka na tare da shi, to ka bi Kwankwasiyya kawai. Haka ya gidan bangaren sa har cikin 2014, lokacin da wasu gwamnoni suka yi wa PDP tawaye, suka shiga APC domin mara wa Buhari baya. Cikin su kuwa har da Kwankwaso.

KAFA GANDUJE A KANO

Bayan kammala zangon Kwankwaso na biyu, ya tsaida mataimakin sa Abdullahi Ganduje takara a karkashin APC, kuma ya yi nasara. Shi kuma Kwankwaso ya ci kujerar Sanatan Kano ta Tsakiya.

Bayan Ganduje ya zama gwamna, yay i wa Kwankwaso godiya a gaban jama’a, inda ya ce ubangidan sa Kwankwaso ya rufa masa asari, a yau wai shi Ganduje, bagidaje, bakauye, Bafulatanin daji mai kiwo, mai yawo da karnuka, amma a yau shi ne gwamna a Kano.

Sai dai kuma tun tafiya ba ta yi nisa ba, aka samu mummunan sabani tsakanin Kwankwaso da Ganduje. Sabanin ya zama gabar da ta kai Kwankwaso ya shafe shekaru uku bai shiga Kano ba, gudun fitina tsakanin mabiyan sa da mabiyan Ganduje.

Sake kada gangar siyasar 2019, wadda Kwankwaso ya sake neman takarar shugaban kasa a karkashin PDP, bayan ficewar sa daga APC ya koma PDP, bai yi nasara ba, saboda Atiku Abubakar ya kayar da shi da sauran ’yan takara duka.

Kwankwaso bai nemi sake tsayawa takarar sanata ba, sai ya nemi sake kafa kan sa a Kano, ta hanyar farfado da akidar Kwankwasiyya. Ya yi kokarin ganin cewa sai aminin sa ya zama dan takarar PDP a jihar Kano. Kuma hakan ta kasance.

Dukkan jiga-jigan PDP da sauran wadanda suka nemi takara ba su samu ba, sun koma bayan Gwamna Abdullahi Ganduje, kuma karkashin tutar Buhariyya.

Wannan ya sa an yi wa PDP mummunan kaye a Jihar Kano, a zaben shugaban kasa da na Majalisar Dattawa da na Majalisar Tarayya.

A gaskiya kowa ya dauka siyasar Kwankwaso ya kare kenan a Kano, ko kuma ma a ce ta mutu. Duk da irin goyon bayan da Kwankwaso ke da shi, ganin yadda ya sha kaye a zaben shugaban kasa, an dauka a zaben gwamna ma haka za a yi wa Kwankwasiya dukan tsiya wanda zai hana ta sake mikewa tsaye.

FARIN JININ ABBA DA BAKIN JININ GANDUJE

Jam’iyyar PDP a Kano ta yi farin jinin samun dan takarar gwamna, wato Abba Kabiru Yusuf, da ake wa lakabi da Abba Gida-gida, daga wani salon wakar sa kamfen din sa da aka yi masa.

A gefe daya kuma Ganduje ya yi bakin jini saboda zargin sa da cika aljifan sa da milyoyin daloli da bidiyonya nuna ya na yi. wannan ya sa PDP ta samu kur’u fiye da APC kuma fiye da wadanda ta samu a zaben shugaban kasa.

KAI KADAI GAYYA

Kwankwaso ya koma Kano cikin watanni kadan da suka gabata domin sake shirin yakin siyasa. A cikin wannan dan takaitaccen lokaci kuma ya tabbatar da cewa shi kwamanda ne cikakke wanda sai da shi ake iya cin yaki. Kakaf a Najeriya yanzu hankalin kowa ya koma a kan makomar zaben Jihar Kano. Wanda kuma kowa ya san Kwankwaso ne ya kai zaben kasancewa yadda ya kasance a yanzu.

Kamar yadda Yasir Ramadan Gwale, wani dan gaban-goshin takarar gwamna Salihu Takai ya fada a Kano, ya ce: “Yanzu dai Kwankwaso ya mayar da kowa makaranta domin koyar darasin siyasa a jihar Kano. Tun daga Mundubawa har zuwa State Road, tun daga Darul Tauheed har zuwa gidan Akida kowa zai koma ya dauki darasi.”

“Kwankwaso shi kadai ya kara da gwamnoni uku, wato Abdullahi Ganduje, Ibrahim Shekarau da kuma Kabiru Gaya. Sannan ya kara da mataimakan gwamnoni uku, wato Nasiru Gawuna, Hafizu Abubakar da Abdllahi T. Gwarzo. Sannan ya kara da sanatoci shida da suka hada da Barau Jibrin, Lado, Zarewe, Hayatu, el-Doguwa da kuma Bello.

“Wannan fa banda tarin kwamishinoni na da da na yanzu, da ‘yan majalisar tarayya na da, da na yanzu, da tarin ‘yan siyasa da suka kunshi ciyamomi na mulki da na jam’iyya da kansiloli zababbu da nadaddu. Da gungun ‘yan siyasar da suka tattaru a gindin Gwamna Ganduje baya-bayan nan, duk Kwankwaso shi kadai ya tattara su ya murkushe.” Inji Sharada.

Jiya Lahadi da dare INEC ta bayyana Ganduje a matsayin wanda ya yi nasara. Idan aka dubi yadda zaben da aka maimaita ya zo da kwamachala da kuma irin yadda aka rika kiraye-kirayen a soke zaben. Za a iya cewa akwai sauran rigima a kotu.

Su kan su kungiyoyin kare dimokradiyya sun yi Allah-wadai da yadda aka rika amfani da muggan makamai wajen tarwatsa jama’a a wurin zabe. Dama kuma jam’iyyar PDP ta tsine wa sakamakon zaben da aka bayyana. Kenan, akwai sauran kallo a kotu.

Ko ba komai dai, bayyana Ganduje wanda ya yi nasara, zai sa shi samun damar yin barci mai nauyi, akalla kafin a sake sabon lalen kokawa a Kotun Sauraren Kararrakin Zabe.

Tags: AbujaGandujeHausaKanoKwankwasoLabaraiNajeriyaPREMIUM TIMES
Previous Post

Ina godewa Kanawa da suka sake bani damar shugabantar su – Ganduje

Next Post

Kotun daukaka kara ta soke ‘yan takaran APC na jihar Zamfara tun daga kan gwamna

Next Post
ABDULAZIZ-YARI Zamfara

Kotun daukaka kara ta soke 'yan takaran APC na jihar Zamfara tun daga kan gwamna

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Jihar Ondo ta faɗi dalilin da ya sa ba za ta buɗe masallacin cikin watan Ramadan ba
  • PDP ta janye dakatarwar da ta yi wa Anyim, Shema, Fayose, ta fasa gurfanar da Gwamna Ortom gaban Kwamitin Ladabtarwa
  • Ƙungiyar Lauyoyin Najeriya ta ce a riƙa watsa zaman sauraren ƙarar da Atiku da Obi su ka maka Tinubu a talbijin kai-tsaye
  • ZAFIN FADUWA: Dalilin da ya sa aka turo sojoji don a murde zaben gwamnan Zamfara, PDP ta yi nasara – Matawalle
  • Bashin da ake bin Najeriya ya mirgina cikin ramin naira tiriliyan 46.25 kafin shiga 2023 – DMO

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.